Showing 72001 words to 75000 words out of 120733 words

Chapter 25 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

38894

yi, duk da komai da za'a ci a bikin order akayi amma kuma akwai aikin da ake mata a kitchen shi zata je ta duba. Murmushi Fauwaz yayi bayan ya baro wajen Maman, dan yasan bata san Tariq ya aikata tsiyar ba, kuma yasan idan ta sani akwai matsala sosai, su dai yan kallo ne, gefe zasu koma suka yadda zata kaya. Kallon gate din da aka bude yayi, Tariq din ne, ya shigo ya samu gefe yayi parking Fauwaz din ya karasa wajen motar  ya bud'e masa kofar, ya zuro kafarsa bayan ya fito rike da kayan sa, ya mikawa Fauwaz din.

"Ajiye min a ciki ina zuwa, zan ga Baba."

"Ai tun asubah be shigo ba fa, sai dai Mama ita ce take neman ka dama."

Hannu yasa ya karbi kayan yace

"Bari na fara shiryawa toh, samo min plain tea nayi warming ciki na."

"Ok."

***A gurguje ya shirya cikin shigar farar shadda wadda da akayi wa aiki da bakin zare, tea din ya dauka yana sha da hannu daya, dayan hannun kuma yana daidaita hular kansa, kiran sa akayi a waya ya daga da sauri dan yasan Baba ne, sukayi magana ya ajiye cup din ko rabi be sha ba, ya rige babbar rigar a hannun sa bayan ya saka bakin takalmin sau ciki, ya fito da sauri ya nufi bangaren Maman, part din nata a cike yake sai yaji duk ya takura, Amira da tazo zata fita yace tayi wa Maman magana.

"Ta shiga wanka." Tace tana kallon yadda kayan jikin sa sukayi masa kyau

"Ok, kice mata mun wuce."

"Ok sai kun dawo."

Har yayi gaba itama ta wuce sai ya tuna

"Amira."

"Na'am?"

"Anjima driver ya kaiki wajen Jidda."

"Tana ina?"

"Ban sani ba."

"Wallahi Ya bansan ina ba shiyasa na tambaya."

"Gidana toh."

Saurin toshe bakin ta, tayi alamun laaa, sai tayi dariya, hararar ta yayi yana kallon ta, tayi saurin daina dariyar yace

"Saura kuma ki bud'e bakin nan naki ki fada wa mama, zan yi magana da ita idan na dawo."

"Ba zan ma fada ba wallahi, ni yanzu ma zan tafi sai na dawo anjima kafin lokacin event din yayi."

"Event din me za'a yi?"

"Anan gidan ne zaa yi, itama Jiddan ta sani ai kayan da zata sa ma yana waje na."

"Ba zata zo ba, kije dai ke sai ki dawo anjima din."

"Toh shikenan bari na chanja kayana, zan ce ma Mama na je a sake gyara min gashi sai na tafi chan."

"Gyaran gashi? Aina akayi?"

"Glamorous Saloon ne, duk fa yau zamu je da Jiddan dama."

"Ok kuje tare din, a gyara mata sai ku koma gida."

"Ok tam."

"Kice mata nace ta saka Hijab idan zaku fita."

"Toh Yah." Tace tana gimtse dariyar da take neman taho mata, juyawa yayi da sauri ya bar wajen, ta kwashe da dariya ta buga tsalle.

Kaamar yadda tace masa zata fadawa Maman haka tace mata, ta dauko ATM din ta, ta bata ta fito wajen takwas bayan su Ya Tariq din sun tafi, ta samu Sam tace ya kaita gidan  Tariq. Jidda na kwance a falon bayan ta gama kukan bakin ciki ta hakura gashi bata ga wayar ta ba, bare ta kira ko Aunty ce tasa ta roke shi taji ana knocking, tashi zaune tayi ta tabbatar da knocking din ake ko kunnenta ne sai taji an sake kwankwasawa, wajen kofar taje tace waye? Da sauri ta bud'e jin muryar wadda bata yi zato ba, suka rungume juna suna ihu kamar wadanda suka shekara basu ga juna ba. Zama sukayi a kujerar Amira ta kalli falon

"Haduwa, ashe kina nan."

"Dama zaki zo?"

"Gashi kuwa, Ya Tariq ne yace nazo na kular masa da matar sa."

"Ba wani nan, ni kyale ni kinsan ya ce wai bazan je gida ba, dan Allah haka ya dace?"

"Kinsan fa shi daban yake, wallahi dan zaki sha fama."

"Allah sarki ni."

"Wai yaushe kika taho? Kuma kin taho gaba daya kenan?"

"Oho nima ban sani ba, bansan me suka kulla shi da Aunty da Yaya ba, yazo ya tiso keyata a gaba har kuka sai da nayi wallahi."

"Ai Ya Tariq, sai a barshi wallahi, haka ya hanaki dinner kina ji kina gani."

"Ki daina tuna min dan Allah."

"Toh sorry, tashi zakiyi ki mana wani abu mu dan ci ko breakfast ban yi ba, yace muje a gyara miki gashin kanki."

"Gashi kuma? Ni ai bana retouching."

"Eh ai ba retouching ba, sake dai gyara mishi kayanshi zaa yi."

"Kayan shi?"

"Eh mana, baki sani ba?"

"Ke kika sani, ta yaya gashi na zai zama kayan shi tsakani da Allah kema dai banda neman magana."

"Ah toh na waye dah? Lallai ma ke din nan wallahi."

"Oho ke kika sani, babu komai a gidan nan sai dai kisha tea da cake."

"Anjima ai za'a kawo garar, wai hadda Ya Tariq a garar da Baba yayi."

Ta kwashe da dariya,

"Ko da yake yace shi yarsa yayi wa ba Ya Tariq ba."

"Allah sarki babanmu, Allah dai ya saka masa da gidan aljanna."

"Amin Amin. Muje ki shirya dan da wuri zan koma kar abubuwan su hade min, amma zan dawo da daddare idan kina so."

"Eh dan Allah ki dawo, wallahi inaso ko kwana ne ma kiyi."

"Wa? Ni? Tabdijam, Ya Tariq din ne zai barni na kwana?"

"Me zai hana?"

"Ba za'a ji mutuwar sarki a baki na ba, jeki shirya dai bari na sha tea din."

"Kyaji da gulmar ki."

Tace tana yin gaba ta shiga kofar da zata kaita dayan falon kafin dakunan nasu. Wanka tayi a gurguje ta ciro riga da skirt ta saka ta dauko veil dinta da handbag ta fito ta samu Amiran ta kunna TV tana kallo tana shan tea din

"Kira min wayata inaga a gida na barta."

"Ok."

Kitchen ta wuce ta hado tea din tazo ta zauna lokacin da amira ta kira wayar tata,

"An d'aga gashi ." Ta mika mata, karba tayi ta kara wayar a kunne

"Hello aunty?"

"Uncle ne ba Aunty ba." Da sauri ta ciro wayar daga kunnen ta, ta kalli number din, taga dai number ta ce,

"Waye?" Amira tayi mata alama da hannu

"Dama wayata nake nema shine nace Amira ta kira min ita."

"Oh okh, tazo kenan, kin daina kukan?"

"Umm.."

"Good, akwai wani abu ne?"

"Um um."

"Okh sai mun dawo." A ciki ta amsa ya kashe

"Wai wa ya daga?"

"Ya T..." Tace tana mika mata wayar ta

"Wai kina nufin da wayar taki ya tafi."

"Gashi nan, ni ban masan yaushe ya dauka ba."

"Lallai Ya Tariq, ai kamar akwai landline a hanyar kitchen din chan, na ganta a saman wani table."

"Ni wayata nake so,."

"Kika sani ko new one za'a kawo miki."

"Ai bance inaso ba."

"Malama ki daina pretending dan Allah, Amira ce fa, your best friend mene wai ban sani ba,ko yanzu kin daina son Ya Tariq din ne ake bashi I don't care attitude."

"Ni da nace miki ina son sa ne?"

"Fadawa wanda be sani ba."

"Tashi mu tafi, kar ya dawo yace ya fasa."

"Kad'an daga aikin babban Yaya."

Ta mike zata yafa mayafi Amira ta tuno da abinda yace mata

"Wallahi na tuna,yace karki yafa mayafi wallahi"

"Na shiga uku, mayafin ma?"

"Wallahi haka yace mun, kuma yana sane sai ya tambaya."

"Gaskiya ni wallahi."

"Haka zaki hakura, dole abi miji dan a zauna lafiya."

"Ke kika sani." Ta


suka fito, Sam yana zaune tare da gate man yana jiran su, suka shiga motar yaja suka bar gidan. Ita aka fara yiwa sannan akayi Amiran, sai sheki gashin yake da kyalli musamman ita da take da gashi sosai, ita kanta me salon din sai da ta yaba da tsantsi da yalwar gashin ta, duk da bashi da cika sosai tsayin da tsantsin ne gashi baki sosai.

A gate aka ajiyeta Amira tace ba zata shigo ba su Salma suna ta kiran ta, kamar zatayi kuka haka ta shiga gidan tana cike da jin haushin Tariq din.



*_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_*

_(Where every flavour tells a story .....)_

*_By HAFSAT RANO_*
_(Mother/wife/writer)_

_08030811300_
_IG:Rano_scrumptious_meal_

_INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_

_MU NA YIN:_

*_FUNKASO_*
*_ALKUBUS_*
*_SINASIR_*
*_WAINA_*

*_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_*
*_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_*
*_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_*

*_LOCAL DRINKS:_*

_HIBISCUS (ZOBO)_
_GINGER_
_AMAANI FRUITY SHAKE_


_MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._

_KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._

_FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_

_ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_

_PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (38)


***Bayan la'asar suka dawo, yana shiga gida ya dauki motar sa ko ciki be shiga ba dan yasan Maman ma tana cikin mutane ya wuce nasa gidan, baki daya wunin ranar tunanin ta yayi tayi, shiyasa suna sauka yayi gidan ya huta gaba daya a chan duk da anjima dole ya dawo gidan nasu kafin a tafi kai yaran.
Horn yayi aka bud'e masa ya shiga da motar ya samu gefe yayi parking sannan ya fito, hannun sa rataye da babbar rigar da bata fi awa daya a jikin sa ba ya cire ta dan duk a takure yake. Key din ya mikawa faisal ya haura, ya murd'a kofar yaji ta a rufe sai yayi knocking. Idar da sallar ta kenan dan bacci tayi tun da tayi azahar ta kwanta sai lokacin ta tashi, tayi sallar tana zaune jigum tana tunanin yanzu su Amira suna chan ana shan shagali ban da ita, da tuni tana part din Yaya ana ta harka. Knocking din ya sake yi ta tashi daga wajen da take ta nufi kofar ta bud'e ta, yana tsaye hannun sa rike da wayar ta da tashi sai babbar rigar dake sakale da dayan hannun, matsawa tayi ta bashi hanyar ya shiga ciki ta rufe kofar ta juyo ciki. Har ya zauna a kujera ya ajiye wayoyin a gefen sa, ya cire hular kansa yana dan kishingid'a saboda yadda yake jin gajiya. Bata ce masa komai ba, ta wuce kitchen ta dauko ruwa da cup ta kawo masa sannan ta mike ta shige ciki, ruwan ya dauka yasha ya dauki remote ya kunne TV ya mike kafarsa sosai sannan ya karo AC falon.
Dakin taje ta zauna kurum tayi shiru tana tunanin me ya kamata tayi,shima kuma kamar wanda aka kullewa baki be ce mata komai ba, sai duk taji babu dadi dan ta dauka zai yi mata magana tunda dai shi ya ajiye ta. Ta dan dade a zaune sai kawai ta tashi tace bari ta watsa ruwa duk da tayi da suka fita da Amira, amma kuma baccin da tayi taji tana bukatar ta watsa ruwan dan duk zuciyar ta a jagule haka ta tashi.
Tana shiga wankan ya shigo dakin, ya zauna a gefen gadon rike da wayar ta da ya kawo mata, motsin ruwa yaji a toilet ya gane tana ciki, maimakon ya fita sai yayi zaman sa idanun sa na kan kofar toilet din yana danna wayar sa. Sam bata ji shigowar sa ba, shiyasa ta fito kai tsaye daga toilet din daure da towel din da yayi amfani dashi dazu, kanta a rufe da karamin towel saboda kar ruwa ya taba.
Sai da tazo kusan rabin dakin sannan ta ankare dashi, tayi diri-diri duk ta diririce kamar zata koma sai kuma taga shima komawar da kunya, tsayawa tayi chak kawai a wajen da take ta sunkuyar da kanta k'asa

"Ga wayarki."

Yace yana daga mata ita sama idon shi na kan ta

"Zan dauka." Tace tana jan towel din a kokarin ganin ta sake rufe jikin ta sosai

"Zo ki karba, ko na koma da ita."

"Ni ba amfani zan da ita ba."

"Ba wani, Aunty ta kira ki, sannan Amira tayi miki text wai zasu zo, na kirata nace bana neman su."

"Toh ka fita idan na saka kayan zan fito sai na karba."

"Ba in da zani."

Yace yana gyara zaman sa, motsawa tayi daga in da take tsaye a hankali har ta isa wajen wardrobe dinta, ta zaro Hijab zata saka ya mike ya iso ya rike Hijab din yana mata kallon cikin ido

"What are you try to hide?"

Shiru tayi dan yadda ya matso so close da ita, ya hana ta motsawa yana kuma yi mata kallon k'asa-k'asa.

"I'm asking you, me kike boye wa, show me."

"Dan... Allah... Kayi hakuri.".

Ta fada a rarrabe ganin ya rike jikin towel din, murmushi yayi yana cije saman lips dinsa, ganin yadda duk ta firgice ta shiga tashin hankali.

"Kema wai kin girma ko?"

"Dan Allah ni dai kayi hakuri."

"I can't, haram ne?"

"Eh." Tace da sauri ba tare da tasan ma ta fada ba. Kallon ta yayi da sauri still yana rike da gefen towel.din itama ta rike kakam

"Ta ya akayi ya zama haram?"

Ya kai hannun sa saman kanta ya cire towel din da ta daura ta rufe gashin

"Wow." Yace yana ya saka hannu ya shafa gashin

"Ta ya akayi ya zama haram? Fada min."

"Sanyi nake ji, ka tsaya nasa kaya na, dan Allah."

"Ok, ok.. Saka toh." Ya cika towel din ya jingina da jikin mirror yana folding hannayen sa

"Kaje waje."

"Ba in da zani, idan zaki sa kisa idan kuma sai na taimaka miki fine, I will be glad to help."

"Na shiga uku."

"Da saura ma yarinya." Ya kad'a kai yana murmushi. Doguwar riga ta dauko ta dora ta akan towel din sannan ta zare towel din ta kasa, ta saka Hijab din akai. Dariya ta bashi yadda take ta sauri ta gama ta kai towel din ciki ta sakashi a washing machine, sannan ta fito

"Kin manta baki saka abinda na gani a cikin wardrobe dinki ba, da twin dinsa."

"Bra and pant." Ta fada a zuciyar ta,

Da sauri ta fice daga dakin dan ta gano Ya Tariq so yake sai ya hanata sakat a gidan. Dariya ya saka, ya mike daga jinginar da yayi yabi bayan ta, ya sameta a kitchen kamar be neman abu. Hannun sa zube a cikin aljihun sa ya tsaya a kofar kitchen din yace

"Kije ki shirya sosai, ki sameni a mota."

"Gida zamu?"

"Oho, don't waste my time."

Da sauri ta koma dakin, ta dauki underwears din ta koma toilet ta saka sannan ta saka riga da skirt sakakku ta dora veil akanta me dan kauri dan bata so yace mata lallai sai ta saka Hijab. Flat shoe ne a kafarta duk da bata da tsawo chan amma shine raayinta, shi ta saka ma yanzu ta fito ta same shi a zaune a mota yana amsa waya ta cikin kunnen sa dake sakale da Bluetooth. Tana zama ya dora mata wayarta akan cinyar ta, ta dauka ta jujjuya ta, sannan ta kunna ta hau whatspp dan ganin me yake faruwa.
Wayar yake tayi idanun sa na kan titin ko sau daya be juyo ya kalle ta ba, har suka karasa gida, da murnar ta,ta kalle shi shima a daidai lokacin ya juyo bayan ya gama wayar wadda da dukka alamu akan aikin sa ne.

"Ki ajiye wayarki kusa dake, zan kiraki." Yace bayan ya samu waje yayi parking zata fita, gid'a masa kai tayi ta fita daga motar yana kallon ta, sai da taga ta fita sannan ta kalle shi

"Ba zan koma ba."

Sai tayi gaba da sauri ta shige part dinsu, dariya ta bashi ma, ya kada kansa yana hasaso yadda zai ciccibeta idan har tace zata masa gardama. Fita ya sake yi daga gidan dan zuwa ya samu Baba a chan guess house dinsa.

Babu kowa a part din nasu sai masu aiki duk suna chan bayan gidan in da ake taron bikin kafin azo kai amaren gidajen su, Amira ta kira a waya tace ta kawo mata kayanta, sai gata ita da Nu'ayma, ta saka suka fita Amira na tsokanar ta.
Aunty ce ta hango su da suka taho wajen, ta kalli chan in da Maman take taga tana wani abun bata lura da Jiddan ba, tashi tayi ta riga su isa ta kama hannun Jiddan tace musu tana zuwa. Chan wajen da ba mutane suka je Jiddan ta gaishe ta, ta amsa cike da murnar ganin ta

"Ashe da gaske yake da yace zai kawo ki."

"Kece kika ce ya kawo ni?"

"Eh nice, sannan Baban ku ma yana son hadaku gaba daya yayi muku magana har Maman Fauwaz, ki nutsu ki kwantar da hankalin ki, duk abinda zai je ya dawo ki rike mijinki kinji? Karki ji tsoron kowa."

"Aunty menene? Akwai matsala ne?"

"Babu ko daya, nasan ba lallai ta amince da tarayyarku ba, musamman yanzu da duk muka gane Tariq yana son ki, zatayi kokarin baki matsala dole sai kin jajirce sannan ki hada da addu'a,."

"Wallahi ni Aunty tsoro nake ji."

"Babu abinda zai faru kinji? Ki kwantar da hankalin ki."

"In sha Allah, nagode."

"Muje ciki, kije ki gaishe su ki dake kuma, mahaifiyar mijinki ce ta zama dolen ki."

"Toh." Tace a sanyaye, suka koma ciki Mama ta hango su, ta gimtse fuska sai taga Jiddan na tahowa in da suke a zaune da manyan kawayen ta harda matar gwamnan adamawa da matan manyan koshoshin kasar

"Jidda." Aunty Mimi ta tare ta tana kusa da in su Maman suke dan suna jin su ma

"Laaa, ina wuni?"

"Lafiya Lou, ban ganki ba gaba daya a kwana biyun nan, har Amira na tambaya tace kina nan."

Murmushi tayi bata ce komai ba,

"Karasa wajen su Maman ki gaishe su."

"Toh." Tace tana matsawa wajen su, ta russuna har k'asa ta gaida su, suka amsa a sake banda Mama da ta juyar da kanta gefe tana magana.

"Matar Tariq ce, shine babba a yaran Mama." Aunty Mimi tace musu tana murmushi

"Ah Hajiya Aisha har suruka ce dake amma bamu sani ba? Gata nan Masha Allah wallahi."

"Kun sani yanzu ai."

Tace tana dariyar yak'e, gefe kuma kamar ta jawo Aunty Mimi da Jiddan ta hada tayi musu shegen duka haka taji, tashi Jiddan tayi ta koma chan wajen su Amira, kafin daga bisani ta fice daga wajen ta tafi dubo Hajiya Yaya.

Da murnar ta,ta shiga kamar wadda ta dade bata ga Yayan ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login