Showing 6001 words to 9000 words out of 120733 words

Chapter 3 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

38889

sai ka mayar dashi wasa."

Har Kawu Rabi'u ya kawo madara da kwan zabin da ya tafi karbo wa Baba bata daina sababi ba, magaanar ta kadai kake ji a dakin sai dai Baba yayi murmushi lokaci zuwa lokaci ya amsa mata, shi kam Tariq ji yake kamar ya fice amma yasan idan yayi haka zai gamu da fishin Baba, shiyasa ya hakura ya zauna kawai yana sauraron surutun ta wanda baki daya babu magaanar da za'a kama.
   Fita Baba yayi yace zai je waje ya zauna da yan uwan sa kafin Yayan ta gama shiryawa, yana fita Tariq da ya tabbatar ya kule yaja tsaki yana dafe kansa.

"Uwarka kake wa tsaki bani ba."

Tace tana hararar sa, kallon ta yayi idanun sa na yin kasa sosai yace

"Ni ba dake nake ba."

"Ko ma da wa kake, mutum sai kuncin tsiya ba yar fara'a haba.".

"Yaya Ya Tariq fa shine angon ki, ki dinga lallabashi."

Fauwaz yace yana kokarin sake rura wutar fadan, buga cinyar ta, tayi tana daga murya

"Allah ya kiyashe ni da aikin dana sani, na auri mutum irin wannan ai na kade har ganye na, matar sa ta shiga uku wallahi."

"Idan kun gama ni ina waje."

Yace yana mikewa, ta rakashi da Allah raka taki gona ya fice kawai ya bar Fauwaz yana kyalkyala dariya, da gaske dariya suke bashi musamman Tariq da ya kasa gane wasan Yayan irin wanda ake yi na tsakanin jika da kaka, da gaske yake daukar komai duk da ba kasafai ya fiya nuna fushin sa ba amma zaka ga sam baya sakewa da ire-iren wasannin.
   Shi ya taimaka mata ta karasa hada kayan ta sannan ya daukar mata jakar, suka fito ta dinga shiga waje-waje tana musu sallama tun yana bin ta har ya gaji yace yana mota. A kwance ya samu Tariq din ya kwantr da kujerar side din me zaman banza fuskarsa rufe da hular da ya saka, booth ya bude ya saka kayan Yayan sannan ya dawo ta side dinsa yayi masa magana, mikewa yayi ya fita ya bashi wajen ya koma mazaunin driver.

"Har yanzu ka kasa gane wace Yaya."

"Haka aka ce maka?"

"Ai naga kamar abun yana damunka, banda yawan maganar ta she's very nice and fun to be with, zatayi ta saka dariya ne."

"Ni kuma sai aka ce maka dariya nake so nayi ko? Bani da aikin yi sai dariya ko?"

"Ba haka nake nufi ba, yawwa gata nan ma ta fito, case closed."

Yace ya ja bakin sa yayi shiru.

"Ni zan bude kofar da kai ne kenan?"

"Afwan Hajiya Yaya, wane mutum ya bar sarauniya da bude kofa?"

Ya bude mata da sauri ya taimaka mata ta shiga, sannan ya rufe mata kofar.

"Ranki ya dade." Yace yana dariya

"Kafi oo sau dubu, Allah dai ya baka mata ta gari me hankali da sanin ya kamata kamar kai."

"Amin."

Yace yana cigaba da dariya, Baba ne yazo ya shiga motar kusa da Yaya, sannan suka sake sallama dasu Kawu Rabi'u, Tariq yaja motar suka fita daga kauyen.

Gudu ya soma yi sosai bayan sun hau babban titi, salati Yaya ta fara yi tana salallami.

"Tariq, rage speed din nan." Baba yace yana kokarin kwantar mata da hankali

"Anya kalou yaran nan yake? Ba zaa kaishi ayi masa rukiya ba kuwa?"

Tace bayan ya rage tafiyar sosai, ta cikin rear mirror ya kalle ta, ya maida kansa gaba ya cigaba da tukin sa yana jin Baba da Fauwaz suna dariya

"Ba abin dariya bane wallahi, dole ma a nemo Malam Na Allah yayi masa rukiya gaskia."

Yana jin su yayi musu shiru tukin sa kawai yake yana fatan su isa lafiya ya tattara ya bar garin gobe dan yasan tunda ta dawo ba zata kyale shi ba sam.
   Har suka isa gida magana daya take, aikuwa yana gama parking yayi saurin fita ya dauki kayanta a booth yayi cikin gidan da sauri. Anty ce a bangaren Yayan tana karasa gyara mata sashen, ya dire jakar yana jan siririn tsaki.

"Ya akayi?" Tace masa cike da kulawa

"Kai na ke ciwo."

"Kaje akwai panadol a kan fridge ka dauka ka sha, sannu."

"Ok." Yace yayi saurin barin wajen dan baya so suzo su tadda shi, part din Antyn ya shiga, babu kowa a falon ya dauki paracetamol din ya nufi kitchen zai dau ruwa marar sanyi dan shi a rayuwar sa baya shan ruwan sanyi sai idan ana tsananin zafi.
    Tana tsaye a jikin drawer din kitchen din tana gyaran kayan miya, kafarta ya kalla a ganta kamar kara, ya dauki ganin sa zuwa wuyanta da yayi masa kama da murkin lema, mamaki ya sake kamashi ganin tana aikin cike da kuzari, a yadda take da ramar nan be yi tunanin ko numfashi tana yin sa daidai ba, gani yake kamar ko kwakkwaran motsi tayi zata iya karyewa. Gyaran murya yayi ta juyo a tsorace, ya dauke ganin sa daga kanta ya dauki ruwan ya fice.

***Da gudun su suka fito jin sallamar Yayan, tana tsaye a tsakar gida suna gaisawa da Anty da su Abu, Amira ce ta rungumeta, tayi kamar zata yar da ita, ta tureta tana dariya

"Ke baki san kin girma bane ba? Ko dan har yanzu baki fara kirgar dangi ba?"

Kunyace duk ta kamasu, Anty tayi kamar zatayi dariya sai kawai tayi gaba tana cewa

"Yaya muje ki huta karki biye musu."

"Ai fa dan na kwaso gajiya, shima Alhaji ya rasa da wanda zai zo daukata sai da wanchan mahaukacin dan naki, ya dinga gudu dani duk yasa dan abincin da naci ya zazzage."

"Wai Tariq?"

"Kina da wani mahaukacin dan bayan shine?"

"Yanayin sa ne haka Yaya."

"Shi kansa wanda ya gado din haka muka sha fama dashi ya buga ya barni, idan zamu kwana be ce min ufffan ba, bana tanka masa haka akayi zaman nan."

"Allah sarki, Allah yasa ya huta."

Anty tace tana ajiye mata flask din ta da aka zuba mata kunu wanda ya zama kullum sai ta shashi, saboda sabo.

"Kunu ne? Kai Allah yayi miki albarka kinji? Allah ya baki kema masu yi miki."

"Amin." Tace tana murmushi, sai kuma ta fita ta bar Amira da Umaima da Yayan

"Welcome back granny, we missed you.!"

"Uwar granny din, na fada miki bana son sunan ko? Sai karyar turanci, toh turancin ma..."

"Ba kyau zagi fa Yaya."

"Anyi, idan ban yi ba ai ban cika bakatsiniyar ba, kuma ko gobe kika sake min turanci sai na zagi turancin, a banza a wofi wayon a zagi mutum ne."

"Bari kiga, amira sai kin taho, ni nayi gaba, Allah ya dawo da mu ai."

Ta mike,

"Idan kin je karki dawo, yar nema kawai."

"Almasifatu."

Tace ta ruga da gudu, tashi Yayan tayi ta jefa mata pillow din kujera

"Yar nema, zaki dawo har in da nake ne."

***Be shigo gidan ba sai wajen takwas na dare, lokacin Mama ta dawo, ya sameta a dakin ta, tana waya da kawarta, zama yayi akan bedside drawer ganin sa yasa ta katse wayar.

"Tariq!

Ta kira sunan sa, amsawa yayi yana kallon ta

"Ya akayi?"

Tace tana zama daga gefen gadon kusa dashi. Tun bayan da ya fara wayo halin sa ya fito sosai, babu wanda yake zama ya fadawa matsalar sa, ya sha yin ciwo a daki shi kadai babu wanda ya sani, baya taba cewa ayi masa abu sai dai ka fuskanta da kanka kayi masa amma ba wai dan ya tambaya ba, da farko halin sa ya fara tsorata ta, amma kuma kasancewar kakansa mahaifin Baban haka yake sak halin sa ya saka kawai ta hakura dan tasan biyu ce ta hadu ita kanta miskila ce. Ganin sa yanzu ya saka tasan akwai muhimmiyar magaanar da zai mata shiyasa ma ta katse wayar dan zai iya chanja shawara cikin kankanin lokaci.

"Ina jinka."

Ta sake maimaita masa tana kallon fuskar sa

"Dama na gama hada kayan tafiyar ne, sakon da kika ce zaki taho dashi daga cikin gida."

"Oh ai ban manta ba Tariq, gashi chan miko ledar chan, karfe nawa ne jirgin naka?"

"9am, amma da asubah zamu fita."

"Ok, Allah ya kaimu, ya bada sa'ar abinda aka je nema."

"Amin." Yace yana rike da ledar, be koma ya zauna ba, hakan yasa ta gane dama abinda ya kawo shi kenan.

"Nagode."

Yace ya juya ya bar dakin, tayi murmushi kawai tana bin bayan sa da kallo.

***Da asubah bayan sun idar da sallah ya shigo cikin gidan, ya wuce shashen Anty ya kwankwasa, suna zaune bayan sun idar da sallah ita da Jidda suna karatun al'qur'ani, ta dauka Baba ne dan shine yake shigowa da asubah ya duba duk wadda ba ita ce da girki ba, tashi tayi ta bude kofar ganin Tariq yasa ta tuna da magaanar tafiyar sa

"Ba dai har kun fito ba?" Tace tana matsa masa ya shigo ciki

Kamshin turaren sa na Versace ne ya gauraye falon, ya zauna a kujerar dake gefen kofar sannan yace

"Barka da Safiya Anty!"

"Barka dai, ka tashi lafiya?"

"Alhamdulillah, yanzu muke shirin fita, jirgin karfe tara ne."

"Ayya, Allah ya kaiku lafiya ya tsare, ya bada sa'ar abinda aka je nema."

"Amin ya Allah."

Yace yana mikewa,

"Ina kwana?"

Ta gaishe shi cikin muryar ta da take kara sashi mamakin yanayin ta, hatta muryar ta kama take da yanayin jikin ta, yar firit muryarta kamar ana busa usur. Be amsa ba sarai kuma yaji sai da Anty tace ana gaishe ka sannan yace.

"Lafiya."

A gajarce, maimakon ya tafin sa kawai ya tsaya yana nazari, wajen minti daya ya dauka yana tsaye yana juya magaanar da take masa yawo akai, kafin yace

"Anty ki kai yarinyar nan asibiti a duba ta, inaga bata da ishashiyar lafiya."

"Jidda?"

Gyada kansa yayi

"Yes, baki ganta ba? Tayi rama da yawa kar ayi iska me karfi ta tafi da ita."

Dariya sosai ya bawa Anty, ta dinga girgiza kanta cike da mamakin sa

"Toh shikenan Tariq, zan kaita."

Ajiyar zuciya ya sauke kamar wanda yayi wani aiki babba yace

"Yawwa. Sai anjima."

"Allah kaddara saduwar mu."

Tace ya fice da sauri yana tuna lokacin da ya rage masa.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: *_Sanadin_*

               *_Labari nah_*

     Free Page ( 5)


©®Hafsat Rano

****Duk da karancin shekarun ta amma maganar sa tayi mata zafi, kuma tsakanin sa da Allah yake maganar, kamar ya kushe halittar ta ne ko wani abu, amma kuma da ta sake kallon kanta sai taga kuma akwai kamshin gaskiya a maganar sa, tabbas tana da rama ta ban mamaki, dan ita kanta wani lokacin sai ta dinga jin kamar zata karye.

"Haka Tariq yake, yanzu akan wannan maganar asibitin ko yaje sai ya sake kira ya jaddada min, da gaske yake daukar ire-iren wadannan abubuwan musamman da ba wani saka baki ya cika yi a abu ba, amma duk abinda kuma ya damu dashi toh fa baya hakura sai ya cim masa."

Shiru tayi bata ce komai ba har Antyn ta gama bayanin da ta lura so take ta wanke shi, tashi tayi kawai ta soma gyara falon ita kuma Anty ta nufi kitchen dan sama musu dan abinda zasu ci kafin hajiyar gidan ta kirasu zuwa karin kumallo dan duk ranar girkin ta sai an sha yunwa a gidan musamman yanzu da Baba zai fita da asubah ba dashi za'a karya ba dan yace daga airport din ma wani wajen zai yi suna da meeting na majlisun su a masallaci.

***Safiyya ce kawai ta fito da zai tafi ita da Mama suka rakashi har mota, dan su Amira ce musu yayi su zauna kar wadda ta fito baya son ire-iren wadannan abubuwan, last da zai tafi suka sha kukan su yana kallon su shi abun ma mamaki ya bashi, shiyasa wannan karon yace kar su fito, har ya shiga mota ya tuna da Yaya, shi shaf ya ma manta da ita, ya kuma san idan har ya tafi be mata sallama ba ya shiga uku, dan maganar ba zata taba karewa ba ta dinga mita kenan, fitowa yayi daga motar ya nufi bangaren ta yana fatan ya sameta ta koma bacci, yana tura kofar falon ya ganta tana shirin fitowa, da sauri yayi baya ta kalle shi

"Na zata ai tafiya zakayi baka zo ba."

"Ban tafi ba." Yace

"Na zata ai nace, wajen ka nake shirin zuwa yanzu haka ma, zauna muyi magana."

Tace tana zama, kamar kar ya zauna sai kuma ya zauna

"Kana ji, nayi magana da wani malamin mu na chan kauye, yace zaa kawo maka rubutu kasha idan abun be sauki ba sai ayi maka rukiyya, bansan yau zaka tafi ba, ba wanda ya fada min sai da babanku ya dawo yake fada min, yanzu sai ku fara biyawa ku karba sai ku wuce."

"Ina?"

"Ban sani ba."

"Allah ya baki hakuri, zamu biya mu karba."

Yace ya mike

"Karka fa tafi baka karba ba, ka kira su ayapot din kace su jira ka."

"Toh, zan kira."

"Yawwa, Allah ya baka lafiya kaji."

"Amin."

Ya amsa yayi saurin ficewa, ya san rigimar Yaya shiyasa shi duk abinda tace toh yake ce mata,in ba haka ba yaushe mutumin da zai yi tafiya, a jirgi ma ba a mota ba ace wai ya kira yace a jira shi, rigimar ta yawa ne da ita shi takamaimai ba me san rashin lafiyar me yake ba da har za'a ce ya sha magani. Yana zuwa ya fada mota, Baba ya fito suka tafi.

*** Bayan tayi wanka suna zaune da Muhammad da Usman suna bata labarin ball Anty tace ta taso suje ta gaida Yaya, tashi tayi rike da hannun yaran suka fita zuwa bangaren Yayan da yake daga gefen gidan, tana dan madaidacin tsakar gidan ta, a zaune Abu na shanya mata kaya suna hira suka shigo. Da ido Yayan ta kafe Jiddan har suka karaso ta durkusa kasa ta gaishe ta, ta amsa a sake kafin ta dora

"Ina kika samo yar fillo Halima?"

"Yar gidan Yaya ce fa, Hauwa'u."

"Allah sarki, itace ta girma haka."

"Itace."

"Lallai, amma dai ya bar miki ko? Dan banga amfanin zaman zankadediyar yarinya kamar wannan a hannun makirar matar nan ba Lami."

Dariya tayi

"Eh ya bar min."  Tace a kunyace

"Kai madallah madallah, zumunci kenan, ya kyauta ke kuma Allah ya baki ikon rike ta da amana, ya baki ikon tarbiyarta."

"Amin Yaya."

"Kinga shikenan nima na samu yar daki, dan da alama zatafi zabiyoyin chan hankali. (Su Maryam)."

Dariya kawai tayi, ita kuma Jidda tana rakube a gefen tabarmar tun shigowar su, su usman suka koma. Antyn ma cewa tayi tana zuwa ta fice ta barta a wajen Yayan dan bata so tace ta taso, tana fada Yaya zata hau sababi, shiyasa ma kawai tace mata kawai tana zuwa.

   Suna zaune Yaya na ta faman bata labari, labarin rayuwar ta da dah, wani tayi dariya wani kuma sai tayi shiru musamman idan Yayan ta baro wani zancen da bata gane ba. Cikin hirar ne ta sako maganar Tariq, ta rage murya sosai sannan tace

"Aljanu ne dashi fa, ina kyautata zaton aljanun kakansu ne suka dawo kansa, halin su daya da Maigidan nan, gashi naga alamun har so yake yafi Malam bakin hali (Mijinta)..." Sai ta dora tana sake rage murya

"Kinsan fa tsabar bakin halin Malam, duk sanda na haihu sai ya tattara ya koma dakin zaure, ko dan ba zai gani ba, har sai mun yi arba'in, idan bako ya shigo gidan ba zai taba sanin yana nan ba, ko tarin sa ba zaki ji ba, kum bakin sa ko wari baya masa."

"Allah sarki, yanayin sa ne a haka."


"Ba wani ke, bakin hali ne kawai."

Shiru tayi kawai dan bata san me kuma zata sake cewa Yayan ba,sauya labarin tayi zuwa wani daban sai ga Fauwaz ya shigo, ya kalli Yayan ya kalli Jidda sai kuma yayi murmushi

"Yaya bakuwa kikayi ne?"

"Toh baki abun magana an hallaro (wai Yaya ce take cewa wani baki abun magana)"

"Bakuwa kikayi ne Hajiya Yaya?"

"Ba bakuwa bace, kwanan ta nawa a gidan nan baku hadu ba?"

"A ah, kinsan mu idan ba abu ba, ba kasafai muke shiga cikin gidan ba."

"Toh gata nan, kanwar kace dan ta zama yar gidan nan itama, yar Yayan Halima ce."

"Toh Masha Allah, sannun ki."

"Ina wuni?" Tace tana mikewa

"Lafiya lou, kina lafiya?"

Shiru tayi tana wasa da hannun ta

"Zaka korar min ita daga zuwa, Jidda yi zamanki mu cigaba da hirar mu."

"Ah hira kuke? Jidda zauna ayi dani nima."

Sai ya zauna a wajen da ta tashi yana tankwashe kafarsa,

"Zan je na taya Anty aiki."

"Kin jiki, yar kumamar nan dake wane aiki zaki iya?" Yaya tace tana kallon ta

Murmushi ta yi, Fauwaz yace

"Ai ba anan take ba Yaya, sai tafi yaran chan aiki."

"Tunda dama su ba uwar da suke tsinanawa ba, ayi magana ace boko, bokon banza bokon wofi."

Dariya sukayi shi da Jiddan, Yayan ta cigaba da sababi akan bokon, sai ga su sun shigo part din, Amira ce ta ja hannun Jiddan ta zaunar da ita a gefen Ya Fauwaz, maryam ta tsaya daga tsaye tace

"Tun muna daki muke jiyo maganar ki Yaya."

"Ko kice daga bangon duniya ba."

"A'ah dakin dai, kina magana ko hadiyar yawu bakya yi Yaya, ki dinga hutawa."

"Tunda ki kike ci dani kike sha dani, ai sai ki gindaya min sharadi, mutum da bakin sa an isa a hana shi magana ne."

"Allah ya huci zuciyarki gimbiya Yaya, ba abin fada bane."

Tace tana zama a kusa da Amira, suka saka Yayan a tsakiya, wani iri Jiddah take ji, musamman da bata taba experiencing irin wannan rayuwar ba, sai take jin wata nutsuwa na saukar mata, a kalla zatayi rayuwa irin wadda mutane da yawa suke yi, a kalla zata san dadin zama cikin mutane tayi gogagya dasu cikin rayuwa.
   Sun dade a wajen Yayan har sai da Mama ta aiko su zo kitchen lokacin girkin rana yayi, bata bi su kitchen din ba, ta wuce ciki ta samu Anty tana bacci ita da Usman , sai ta shige daki ta kwanta kawai tayi lamo akan gadon rayuwar ta na dawo mata daki -daki, mataki-mataki. Bata san daga nan wanne mataki zata taka ba, Amma ko ma wanne iri ne zatayi kokari wajen kula da rayuwar ta da kanta, dan ba zata so ta sake maimaita rayuwar ta, ta baya ba.
    Washegari litinin suka tashi da shirin zuwa makaranta, tun asubah kowa na gidan ya mike aka hau shirin shiryawa, tana shara Anty tace ta ajiye taje tayi wanka dan tare da ita zaa tafi makarantar, fuskarta ce ta fadada da fara'ah, tayi saurin karasa sharar yayi wanka a gurguje dadi na kamata, kaya ta tarar akan gadon da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login