Showing 93001 words to 96000 words out of 120733 words

Chapter 32 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

38855

a gaba sai Mama da Aunty N a tsakiya. Da sauri Fauwaz ya nufi wajen motar sa ya shiga yana kiran Ya Tariq din a waya amma sam taki shiga, key yayi ma motar ya bi bayan su yana cigaba da gwadawa.

Yana kwance a falo lokaci zuwa lokaci yana lekawa ya dubo Jiddan amma sai yaga tana bacci, sai ya dawo. Har bacci ya soma daukar sa yaji ana knocking a chan kofar main entrance din, Godiya ce ta fito daga kitchen taje ta bud'e sai ya mike ya fito daidai lokacin da Mama, Aunty Nafi, Salma sai Fauwaz dake bayan su suka shigo, da kallo ya bisu irin kallon mamakin nan, kafin ya karaso yana nazarin fuskar Maman da take a hade tamkar an mata mutuwa.

"Mama? Welcome."

"Ina ka ajiye wayar ka nake da kiran ka?"

"A falo na barta."

"Good, zauna." Tace tana nuna masa wajen zama ya zauna a darare duk jikinsa yayi sanyi dan be san dalilin zuwan nasu ba

"Salma, maimaita abinda kika fada mana ni da mamanki."

"Na'am?" Tace tana kallon TARIQ din da itama shi yake kallo

"Kiyi magana mana ba kallon sa zaki tsaya yi ba." Aunty Nafi tace tana tamke fuska

"Dama, dama ya Tariq ne."

Saukar da kai Mama tayi wani irin abu na taso mata tun kafin Salman ta yi maganar da ta gigita ta, ta kuma hanata bacci a daren jiya ko runtsawa bata yi ba.

"Muna jinki."

"Dama shine ya ke taba ni yana min wani abu shine jiya da ya dawo ya fara min wata irin magana ni kuma nace bana so sai ga jiddah nan ta fito shine ya kore mu yace mu bar masa gida."

Wajen sakwanni biyar maganganun nata suka dauka kafin su kai sakon zuwa kwakwalwar Tariq wanda ya kura mata ido kawai ya kasa furta ko kalma daya.

"Kaji abinda tace?"

Mama tace cike da kunya da takaicin hali irin na Nafi

"Ya Tariq kana ji kuwa?"

Fauwaz yace ganin kamar be san me ake cewa ba.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (48)


A hankali yanayin fuskar sa ya shiga chanjawa zuwa tsananin bacin rai, cikin kankanin lokaci kamannin sa suka sauya ya koma tamkar wanda be taba dariya ko murmushi ba a rayuwar sa, kallon yarinyar yake yana jin zai iya kakkaryata ya zubar a wajen idan har ya biyewa zuciyar sa.

"Baka ce komai ba." Mama tace tana kallon sa

"Me zai ce? Bashi da abin cewa ai, ni wallahi an cuce ni wallahi an cuci rayuwa ta."

Anty Nafi tace tana fashewa da kukan munafurci, be ko kalli in da take ba, ya cigaba da kallon Salman ita kuma ta sunkuyar da kanta kasa dan kallon nasa ya fara bata tsoro, ba ita ba har Anty Nafin tsoro ya shige ta ganin yadda kirjin sa yake dagawa.

"Tariq!!!" Mama ta kwala kiran sa, ya juyo a nutse yana kallon ta tar,

"Na'am Mama."

"Baka ji me Salma tace ba?"

"Naji Mama." Yace yana kokarin daidaita calmness dinsa

"Amma ba zaka ce komai ba?"

"Bani da abinda zan ce Mama, in dai har wannan dakikiyar kazamar kuchakar yarinyar nan zata zauna ta tsara wannan maganar kuma ku zo dan tabbatarwa, bani da abinda zance akai."

"Tariq karka yi kokarin chanja maganar nan, kasan dai Salma ba zata maka karya ba ko?" Anty Nafi ta fada ganin kamar yanayin da yake ciki ya sassauta

"Da mahaifiyata nake magana ban sa dake ba!"

Yace mata a fusace, da karfi. Tsit tayi bata kuma cewa komai ba, ya maida hankalin sa kan Mama ya cigaba da magana

"Idan har yarinyar nan ta kara minti daya a gidan nan wallahi wallahi sai na ajiye alaka da komai na kakkaryata na zubar a wajen nan,."

"Saboda baka son gaskiya ko? Wallahi ba zan yarda dake ni sannan a hanani kuka ba, wallahi mahaifin ka zan gyayawa, ko ka auri Salma wallahi ko na fada masa, kunsan dai dan siyasa ne baya so sunan sa ya baci ko?"

"To hell with you!" Ya dake mata tsawa

"Ki fadawa duk wanda zaki fadawa wallahi, I don't care!"

"Fauwaz, take them out."

"Calm down Ya Tariq."

"Su fita nace!"

"Tashi Nafi, ma karasa maganar a gida." Mama tace tana kallon yadda yake huci

"Dole ya auri Salma wallahi dan ba zai lallata min rayuwar yarinya kuma yazo yace ba zai aure ta ba."

"Muje."

Tashi tayi tana cigaba da kumfar baki, Jidda da tun dazu take jin muryar sa a sama ce ta lallabo ta fito sanye da rigar sa sai yar hular da ta rufe gashin kanta,sun tashi kenan ta fito kallo ya dawo kanta, da sauri ta juya zata koma a tunanin ta basu ganta ba, sai jin Fauwaz tayi ya kira sunan ta

"Aunty jidda."

Tsayawa tayi ta juyo cikin matsananciyar kunya ta karaso falon ta duk'a kad'an tace

"Ina kwana?"

A gajarce Maman ta amsa tana kauda kanta dan kallo daya tayi wa Jiddan ta gano wani abu, Anty Nafi ta gaisar amma bata amsa ba sai Salma da ta banka mata harara, suka fice daga falon ya rage saura Tariq din da Fauwaz, zama Tariq din yayi yana tallafe kansa da hannayen sa biyu.

"Ya Fauwaz ina kwana?"

"Lafiya lou Jidda, pls ki kula da Ya Tariq bari na dawo."

Sai ya juya shima ya fice daga falon ya same su har sun shiga mota.

A gaban sa tayi kamar kneel down tana kallon hannun sa da ya tallafe fuskar sa dashi, hannu tasa ta kama hannun nasa ya dago idanun sa da suka rini sukayi jajawur ya zuba mata tsoro ya kamata ganin yadda suka koma.

"Ya kike jin jikinki?" Ya fada muryar sa a dashe kamar wanda yasha wani abu

"Naji sauki."

"Ok."

"Baka da lafiya ne?"

"I'm furious Jiddaaaa."

Sai ya saka hannu ya jawo ta jikin sa, ya rungume ta ko zai samu saukin abinda yake ji.

Fauwaz ne ya dawo ciki sannan ya cikata yana gyara mata jikin rigar

"Jeki ciki kinji? Karki damu."

Jiki a sanyaye ta shige ciki ya kalli Fauwaz yana tashi tsaye

"Ya za'a yi Ya Tariq? Menene abun yi? Kasan irin wannan sharrin issue ne very complicated, sannan kamar bata sunan mutum ne, hatta Baba idan abun nan ya fita sai sunan sa ya baci sosai duk da ba gaskiya bane."

"Fauwaz I don't care duk abinda duniya zata ce wallahi, this is a great lesson da ya kamata Mama ta dauka, da tun farko ba'a turo yarinyar nan gidan nan ba, ya hakan zata faru? But sai ta biyewa Anty Nafi which ita da kanta tasan how evil that woman is, duk saboda kishi, kishin da bashi da maaana bare tushe."

"But Aunty Nafi zata iya aikata komai to tarnish your reputation in dai har bukatar ta zata biya."

"Har abadah wallahi, kuma in dai ta cigaba da pushing akan maganar nan wallahi sai na bata mamaki ita da ballagazar yar ta."

"Calm down dan Allah, don't frustrate your self mu zauna a samu solution."

"Ba wani solution Fauwaz, tunda hakan suke so hakan za'a yi, muga wanda zai fasa ni dasu."

"Amma idan suka samu Baba da maganar fa? Kana ganin zai yarda?"

"I can't say ko zai yarda ko bazai yarda ba wallahi, ni dai tunda nasan ban aikata ba shikenan." Yayi maganar yana yarfa hannun sa gefe daya cikin bacin rai

"Nasan kana cikin bacin rai."

"Very! Kasan yadda sharri yake kuwa? Sharri irin wannan? ba zaka gane ba."

"I totally understand, nasan yadda kake ji, it's not easy amma kayi hakuri dan Allah, mu bi komai a sannu wasu matan are cunning yadda baka taba tunani, shaidan haka suke wallahi."

"Allah ya kyauta."

"Amin ya Allah, inaga bari naje duk yadda ake ciki zan fada maka."

"Ok thank you." Ya mika masa hannu sukayi musabiha sannan ya tafi shi kuma ya cigaba da zama a wajen ya kasa mikewa bare ya shiga ciki.

***Tunanin abinda ya kawo Maaman take tunda ta koma duk da taga Salma ta kuma san kila akan abinda ya faru jiya ne amma kuma ai be ci ace har sai Maman sunzo da kanta ba, bacin ran dake fuskar Ya Tariq din yasa ta tabbatar akwai matsala babba, wanda ta alakanta da yadda Maman bata son auren su. Shiru shiru be shigo ba gashi bata son komawa ko basu gama maganar ba, zama tayi ta cigaba da jiran sa har ta gaji ta shiga wanka tana fitowa ta ganshi yana duba wasu takardu, dagowa yayi ya kalle ta kad'an ya cigaba da abinda yake yi, wucewa tayi ta dauki kaya a closet ta saka daidai lokacin ya fice daga dakin ya dauki system dinsa ya fara yi mata processing visa!




*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*


*ZAFAFA BIYAR BACTH A*


1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350
*(Bilyn Abdul)*


2.. _KAI MIN HALACCI_ 350
*(Miss xoxo)*


3.. _BURI DAYA_ 350
*(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350
*(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350
*(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*


1... _DAURIN GORO_ 350
*(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350
*(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350
*(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350
*(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350
*(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350
*(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350
*(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350
*(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350
*(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350
*(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350
*(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*


_Duk biyar 1500_

*______________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_
*(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_
*(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_
*(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_
*(Mamu gee)*

5... _BABU SO_
*(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_
*HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_
*_2270637070_*



_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*



*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_*
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (50)

***A zaune Mama take kan ta yayi masifar daukar zafi, ta rasa yadda zata bullowa al'amarin gashi dole ba zata karyata Nafin ba ta zabi Tariq, tasan ba zai aikata ba, bata so kuma maganar ta kai wajen Baba dan tasan dama a ciki yake da ita, kuma zai ce menene dalilin tura yaran gidan Tariq din. Dakin da Nafi take ciki da Salmar ta tashi ta shiga, ta same su sun yi jingum jingum.

"Magana zamuyi Nafi."

"Maganar me Yaya? Bayan kin goyi bayan danki saboda ita Salmar ba taki bace ba."

"Ba haka bane ba, ban goyi bayan sa ba amma kuma ina tantamar Tariq da aikata irin wannan laifin, duk da an ce ba'a shaidar d'a."

"Dama a duk irin wannan abun mace ake cuta, yanzu shikenan haka za'a bar maganar? Ni da ban zafafa ba idan ma hakan ne ai shi sai ya aureta tunda shine ya fara bata ta."

Runtse ido Mama tayi maganar na shigar ta kamar an soka mata mashi, girgiza kai tayi ta karaso ciki ta zauna sosai tana kallon Salma

"Da yaushe da yaushe ne hakan ta faru? Kuma ke kadai ce a wajen ko tare kuke da Amira?"

Kallon uwarta tayi sai kuma ta kalli Maman

"Tun anan gidan ne."

"Yanzu me kike so ayi Nafi?"

"MU rufawa juna asiri, ki saka Tariq ya auri Salma kawai, kinga shikenan mun rufe asirin juna tunda dai ai uwa daya uba daya ba wasa bane."

"Shikenan, zan masa magana."

Sai ta mike

"Mu bar maganar a tsakaninmu dan Allah, har zuwa lokacin da zamu samu bakin zaren."

"Ba matsala."

Fita tayi ta ja musu kofar, da sauri Salma ta tashi ta rungume Aunty Nafi tana kyalkyala dariya

"Ke da kin tsaya sokwanta, ina neman miki inda zaki huta kiji dadi, Allah na tuba gida be koshi ba zaa kai dawa ne? Itama Yayar duk da ita amma dama ina kai ina bari kishiya ta mallake ma da, in dai Tariq ya aure ki Jidda ta zama sorry wallahi, dan sai mun kore ta da kafarta"

"Allah Mami bana son yarinyar nan,."

"Ni kaina ba sonta nake ba,amma tunda uwar Tariq zata sashi auren ki ai dole ma ta tattara tayi gaba dan kin ganni nan? Bana zama da kishiya kuma ban taba bora ba, shi kanshi Babanku da matar sa na same shi amma wallahi da kanta ta nemi saki tayi gaba, ba zata iya ba."

"Yanzu Jiddan ma zata tafi?"

"Dolen ta, ai barewa ba zatayi gudu dan ta yayi rarrafe ba, duk abinda ake dan su wa ma tukunna ake yi? Dan 'yaya ne dama."

"Shiyasa nake son ki Mami na."

"Ki saki jikinki kamar anyi an gama, sannan ki cigaba da acting din da nace miki dan hankalin Maman ya cigaba da tashi, idan yaso kinga zata fi daukar mataki dan tana tsoron magaanar ta kai wajen Baban."

"zan cigaba kuwa."

"Good, haka nake son ji."

Da sauri Mama ta bar jikin kofar bayan ta gama jin komai, dama chan bata yarda da maganar ba dan tasan halin Nafi sarai zata iya shirya komai, kuma dama bata taba sha'awar Tariq din ya auri Salma dan sak halin uwarta take dashi, duk da bata son Jidda amma a yanzu sai take jin gwara Jiddan sau dubu akan Salmar.
    Zama tayi tana tunanin mafita, sai ga Fauwaz ya shigo, dakin ta suka shiga ya zauna sannan ta karanta masa komai da taji.

"Mah wai dama kin yarda ne?"

"A ah Fauwaz, kawai bansan wanne irin tunani zanyi ba."

"Toh wallahi ko kaffara ba zan ba Ya Tariq ko kallo bata ishe shi ba, bare har akai ga haka, kawai dai sharri suke son masa, muka mah ba dan ke ba nasan Ya Tariq sai ya rufe su wallahi."

"Naga yadda ransa ya baci sosai wallahi, shiyasa da yace su fita nace muje dan nima zama na bashi da amfani."

"Amma me yasa bakya son Jidda Mama? Wallahi Jidda bata da matsala kuma nasan zata chanja Ya Tariq fiye da yadda muke tunani,."

"Kawai bana son ta ne, a bar maganar."

"Yanzu toh me ya kamata ayi?"

"Nasan me zanyi."

"Shikenan, Umaima ta kira wai aakai mata wasu kayan ta."

"Eh Amira ta fada min, sai suje anjima da Maryam driver ya kaisu."

"Ok."

Wayar ta ce tayi kara Fauwaz dake gefen ta, ya miko mata.

"Baba ne, ko sun sauka?"

Tace tana daga wayar. Gajeriyar magana sukayi yace yana daf da shigowa gidan, tashi tayi tabi ta kofar baya zuwa shashen shi kuma Fauwaz yayi relazing a cikin kujerar yana karo volume din TV. Salma ce ta fito tazo ta zauna tana kin kallon sa, tashi yayi ya zauna yana ajiye wayar hannun sa a gefen sa

"Amaryar Ya Tariq."

Da sauri ta waigo ta kalle shi, ya kashe mata ido daya yana dariya

"Ashe kinsan sunan ki, sunan kuma yayi daidai dake fa."

"Ya Fauwaz banda tsokana."

"Kai I'm serious fa, Amma kinsan me?"

"A ah sai ka fada."

"Ki kyale shi kawai ki dawo kaina gani handsome guy ga naira gani single."

Tsuke bakin ta, tayi ganin kamar raina mata wake son yi

"Allah kuwa, gwara ki kama saurayi kamar ni bashi da yake da mata ba, kuma wallahi baya son ki..."

"Kuma ba zai taba son ki ba, kinsan mu maza mun fi son mace me aji ba wanda take tura mana kanta ta karfi da yaji ba, sam ba aji bare daraja! Darajeless wallahi."

Ya sake fashewa da dariya, cika tayi fam ta kasa bude baki bare ta maida masa, mikewa yayi yana tattare key din sa da wayar sa ya zo gaban ta ya karkad'a mata key din a fuska

"Duk sanda kika shirya ki tura application dinki zan duba naga ko zan iya manage."

Tana kallo yayi ficewar sa daga falon, ta tashi da sauri ta shiga ciki kuka na taso mata, kukan bakin cikin da ya guma mata kuma ta kasa bude baki ta rama.
Wajen Yaya yayi wucewar sa ya sameta kamar ko yaushe tana kulla lalle a kafarta, jan kafar yayi ta kai masa duka da hannun da yake daure da leda da tsumma.

"Jairi.",

"Ni dai idan dan ni kike kunshin nan na yafe wallahi, nafi son kafar taki a haka a dan ya mushe."

"Sai dai kafar matar kace a yamushe ba dai tawa ba."

"Ina da wata matar ne bayan ke gimbiya?"

"Uwar gimbiya, munafuki ai naji abinda kaje kana yadawa wai naje gidan Jidda Tariq ya wulakanta ni."

"Ni? Waye ya fada? Karya ake min."

"Kai tafi chan, ai duk abinda kaje kana cewa ya dawo kunne na tas!"

"So dai ake a hada MASOYA biyu, ki cire lallen nan kizo muje gidan Ya Tariq din muci girkin amarya, sai na barki ko kwana biyu kiyi dan naga alamar kina son zuwa."

"Allah ya tsare ni da zuwa gidan nan,marasa kunya kawai, kai ma ko auren kayi bani ba gidan ka."

"Toh ai bani da wata matar bayan ke."

"Mutan garin ku Fauwaz."

Baba yace yana shigowa, sosa keya ya hau yi ya durkusa ya gaida Baban ya amsa yana murmushi,

"Ka raina min uwata ko? Toh kaima sai an raina taka."

"Ba haka bane Baba."

"Ai wannan yaron ya maida ni kakar sa wallahi."

"Rabu dashi Yaya, yaran yanzu ne sai hakuri."

"Ko da yake ai gwara shi, shi wanchan da naje gidan sa ai kora da hali yayi min."

"Wai Tariq?"

"Shi fa, daga shi har Jiddan ashe fitsararru ne ban sani ba, jiran ta nake ai tazo har nan ta samen, taji maganganu wallahi."

Murmushi kawai Baba yayi yace

"Yaya kenan, Ina wuni, mun same ku lafiya?"

"Lafiya lou wallahi, ya hanyar? Hankali yayi gaba ashe ko gaisawa bamuyi, gashi ba hannu bare na miko ma ruwa."

"Karki wahala ma Yaya, tun safe muka dawo wani abun ne ya rike mu."

"Toh Masha Allahu, Allah dai ya bada sa'ar abinda ake nema ya raba ku da makiyanku lafiya yasa a gama lafiya."

"Amin Amin Yaya, addu'ar kenan."


***Tana nade a cikin blanket ya dauki towel ya daura a kugun sa fuskar sa fes gaba daya bacin ran da yake ciki ya neme shi ya rasa,sai farin ciki da ya mamaye ilahirin zuciyar sa. Jidda ta biya shi har da kari dan duk hasashen shi baya taba hasaso hakan sai yau da ya tsinci kansa a cikin duniyar Jiddan me cike

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login