Showing 27001 words to 30000 words out of 120733 words

Chapter 10 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

45457

da gida suke, amma kiga fa ko tafiya Abujan nan Mama ce fa zata koma, tsakani da Allah mu ajiye son zuciya muyi maganar Allah, menene laifin Halima?"

"Mimi bana son maganar nan dan Allah, a barta ranar farin ciki ce bana son abinda zai bata min rai."

Mama tace tana mikewa

"Nayi shiru." Ta rufe bakin ta, tabe baki sauran sukayi dan duk basa goyon bayan Anty Mimi kawai dan dai babu me ce mata komai kowa yana respecting dinta dan kaf gidansu babu kamar ta a kirki da son yan uwanta.

***Duk suna zazzaune wasu na danna waya wasu kuma na hira Amira ta shigo tare da jiddah,

"Maryam yau ga jidda na sakata shigowar dole."

"Kai Amira da kai na fa nace zan biyo ki."

"Ban yarda ba wallahi." Umaima tace tana dariya

"Wace ita?"

Salma da tun shigowar ta taji sam yarinyar batayi mata ba, in dai taga wadda ta fita kyau a waje sai kawai taji tana jin haushin ta, tafi so duk in da taje ta zama ontop

"Jidda ce, yar gidan Auntyn mu ce."

"Daga kauye take kenan." Tace tana dariya

"Salma." Ya Safiyya dake gefe tana chatting tace tana bata fuska

"Bana son irin wannan maganar, jiddah shigo ki zauna."

Ta dora tana yi wa jiddan murmushi abinda yayi matukar daure mata kai, toh ko dan dama bata cika magana bane shiyasa Jiddan ta zata ko bata da kirki ne? Jikinta a sanyaye ta zauna kusa da Maryam, sai Salma ta tashi fuuuu ta fice daga dakin.

"Yarinyar nan bata da hankali, amma zan yi maganin ta."

Safiyya tace tana mikewa, ta bar musu dakin ya rage daga Jidda, Amira, Umaima, Maryam sai yar gidan Aunty Mimi Nu'ayma. Sukayi zaman su har jiddah ta saki jikinta sosai dan dama Salma ce tasa ta darare da farko, tare suka ci abinci a dakin sukayi zaman su har lokacin tafiyar su Nu'ayma yayi Salma ta shigo tana kumbure-kumbure tace tazo su tafi. Biyo ta sukayi ya rage saura jidda a dakin tayi zaman ta, suna fita suka ji Aunty Nafi na fada

"Akan wata bare Safiyya zata wulakanta yar uwarta yanzu Ya Aisha"

"Kiyi hakuri zamuyi magana, duk wannan ba abin tada hankali bane dan Allah."

Mama da bata cika son irin wannan abubuwan ba, ta fada tana kallon gefen da Safiyya take akan dinning tana duba wata magazine kamar ba da ita ake ba. Ashe biyo Salman tayi ta rar rankwashe mata kai tace kuma kar ta sake musu irin haka, shine harda kukan ta, ta fadawa uwarta shine ita kuma taji haushi take ta banbami.

***Babban Album jidda ta hango akan wata akwati, ta tashi ta dauko ta bude ta fara kalla, hotunan su ne tun suna yara zuwa girman su, sosai wasu hotunan suka bata dariya, ta dinga dariya tana kalla, har tazo kan hotunan Ya Fauwaz da Ya Tariq, tsayawa tayi tana kallon hoton idanun ta akan sa, fuskar sa kamar sanda yazo part din Antyn a duk hotunan, kamar dole akayi masa baya so. Taba kofar dakin taji anyi, ta tsaya da abinda take tana kallon kofar, turo kofar Safiyya tayi ta shigo tana kallon hannun Jiddan

"Kina ciki dama jiddah?" Tace tana zama daga gefen ta, cikin rashin sakewa Jiddan tace

"Ina ciki hotuna nake kalla."

"Kin ganmu muna yara kanana ko?" Tace tana murmushi

"Amira duk tafi bani dariya."

"Ai Amira muguwar mummuna ce taana yarinya, ni da Ya Tariq ne kawai dama masu kyau."

"Gaskiya."

Tace tsakanin ta da Allah dan safiyyan kamar su daya da Tariq din hatta yanayin shirun su da yadda suke magana.

"Bari kiga sabon Album din kwanan nan." Ta tashi ta dauko mata sabon da suka yi ranar graduation din ta, ta dora akan kafar jiddan ta bud'e mata

Shine a farkon page yana sanye da dogon jeans da farar t-shirt, fuskar sa sake yayi murmushi wanda yayi matukar yi masa kyau,

"Dama yana murmushi?" Ta samu kanta da tambaya

"Kai sosai ma, sai dai ba kowa yake ma ba, wannan ma ni na saka shi yi wallahi."

Bata ce komai ba, ta bude next page ta cigaba da kalla, kusan dukka hotunan su ne shi da Safiyya, sai wanda Safiyyan da su Amira amma nasa yafi yawa. Hotunan sun yi kyau dukka kamar zaka yi musu magana su amsa ta ciki dan yadda ya dauku sosai.

Dawowa sukayi daga rakasu suka tarar da jiddan tana kallon hotunan suka zauna aka cigaba da kalla tare ana tuna baya,wanda zaa yi dariya ayi

"Kinga na Ya Tariq yana karami?" Maryam tace tana dariya

"A ah." Ta girgiza kai

"Ya Sofy ina album din Ya Tariq dan Allah."

"Salon kuyi masa dariya,ajiya ya bani ba zan baku ba."

"Dan Allah jidda ce zata gani, Yaya boss yana karami."

"Noo ba zan ci amana ba."

"Jidda kice kinaso ki kalla zata dauko, musha dariya"

" A'ah kar a dauko ni dai ba ruwana."

"Kin kwafsa, da mun sha kallo wallahi."

"Dan dai baya nan ne, kunsan da baku isa ba wallahi."

Ya Safiyya tace tana dariya, abinda ya sake bama jiddah mamaki ganin yadda ta sake tare dasu kamar ba ita ba.

Har bayan magriba tana wajensu,dan ji tayi ma kamar tayi ta zama a chan yadda taji dadin yinin ranar. Sai da Aunty ta turo tazo sannan suka rankaya tare da Amira suka koma wajen aunty, basu ga Mama a falo ba kamar ma bata nan dai.


***Kwana biyu Baba ya kara ya dawo cikin rakiyar mutane da yawa, a hanya sukayi magana da Tariq dan tun ranar be samu kansa ba, tare yake da sababbin masu kula dashi DSS har su hudu, sai wasu motocin, dole zaman sa a unguwar ba zai yiwu ba musamman yanayin aiki dole ya zama yana kusa da Mr President sannan kuma da yanayin yadda kasar ta zama dole yanzu sai an samu wadanda zasu zauna da family dinsa su kula dasu kafin ya tattara su dukka su koma chan saboda security purpose.
Gidan a cike yake taf, Baffa da Iya Lami sunzo duk da be so tahowa da ita ba amma ta nace a dole sai tazo ba yadda ya iya suka taho tare har da Innar su Saude da Sauden, duk sun zo taya Aunty murnaz Baffa kuma Baba. Kafin isowar Baban gidan ya cika ba masaka tsinke hatta bangaren Yaya a cike yake da yan uwanta da na Malam, Mama ma wajen ta aciken yake da kawaye da yan uwa. Mom din su Safeera ma tazo da kanwar Daddy da Safeeraan. Aunty ce fa gayyato su duk dai dan itama bangaren ta kar ya zama babu kowa tunda su ba yawa ne dasu ba, ba kuma ta san mutanen anan din ba
Duk girke-girken da akayi Mama ce ta saka akayi order ta fitar ma da Yaya na part din ta haka ma aunty sannan ta bar nata a wajenta. Ta shirya cikin shiga ta alfarma wadda tayi bala'in karbar zubi da tsarin ta, dama Mama yar gayu ce tun da bare yanzu da likafa ta daga ta zama matar minister wadda take jin a yanzu ne tayi daidai da level dinta.
Itama Aunty tayi shigar ta daidai da ita tayi kyau kuma abinka da dama chan kyayyawa ce sai ta fito fes sosai. Iya Lami tana ta zak'ewa a wajen Auntyn duk da taki yarda sam da ita, Jiddah kuwa daga gaisuwa ko kallon ta bata sake yi ba, tayi zaman ta a daki ita da Safeera.
Part din Yaya, Baban ya fara shiga kamar yadda ya saba ya gaggaisa da mutane. Yaya kamar ta zuba ruwa a k'asa tasha, dan farin ciki. Daga nan ya shiga wajen Mama itama da nata mutanen suka gaisa sukayi masa Allah ya sanya alkhairi, sannan ya shiga wajen Aunty a karshe. Daga nan ya dawo wajen su Baffa da aka saka rumfa a harabar gidan suna zazzaune a wajen.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (14)

***Da sauri ya karasa gaban table din,ya zauna yana jawo system din, ya cigaba da bin lectures din har zuwa sanda malamin ya gama, ya zare headphone din dake kunnen sa ya mike ya tattare komai ya ajiye a gefe ya kashe system din ya zare flash din dake makale a jiki, ya nufi wajen da kayansa suke ya dauko dambun naman da ya taho dashi ya ajiye sannan ya samo chilled juice ya hada ya zauna yana ci yana browsing a wayar sa.
   Ya dade a zaune a wajen har lokacin sallah yayi, ya mike bayan ya zare socks din dake kafarsa ya nufi toilet yayi alwala ya fito ya wuce zuwa dan madaidacin masallacin da yake kusa da apartment din nasu, yana cikin dalilin da ya sakashi karbar apartment din saboda kasancewar masallacin da yake kusa da wajen, baya taba missing sallah duk da ba wai ana kiran sallar bane amma kuma yana amfani da wayar sa yaga time din idan yayi yaje yayi sallar.
    Ajiye takalmin sa yayi a cikin wasu lockers sannan ya dauki wani na shiga cikin masallacin ya saka ya haura sama in da ake sallah, ka'idar su ce baa cika cikin main building din da takalmi sai dai ka ajiye shi a farkon shigowa in da aka tanadi lockers masu kyau kowa ya ajiye nasa a wajen tunda ba wai yawa ne dasu ba, Ishaq ya hango a gaban sahu ya karasa kusa dashi sukayi sallar sannan suka fito a tare, anan yake tambayar sa abinda ya hanashi zuwa lectures yau, shafa kansa yayi kafin yace

"Haka nan naji bana so fita yau."

"Manyan kwari dama ai haka ne, ko basu yi attending class ba lafiya lou."

"Ba wani, kuma ma nayi following online, banbancin mu kawai zama a class din ne."

"Eh haka Mr David yace, kayi joining class din tun daga farko."

"Eh." Yace suna cigaba da tafiya.

"I'm hungry wallahi, ko kana da wani abun naci?"

"Muje ba za'a rasa ba ai."

Yace sanda suke haura stairs din maimakon lift, ba ko yaushe yake bin lift din ba musamman idan ranar be wani yi exercise sosai ba sai ya hau stairs din kawai ko ba komai ya motsa jinin sa.

"Da lift da komai amma ka bamu wahala,."

"Ka motsa jini ai."

"Duk wanda nake yi kullum."

"Ka kara wani." Yace yana manna card dinsa a jikin kofar, ta bude suka shiga ciki, kallon basket din Ishaq yayi kafin yace

"Wannan fa?" Ya nuna basket din

Tabe baki yayi kafin yace

"Yarinyar nan ce ta kawo."

"Yasmin?"

"Oh eh ita."

"Wai kace nazo adaidai, har abinci take kawo maka kenan."

Juyowa yayi da sauri ya harare shi

"This is the first and last time, nasan ba zata sake iyayin kawowa ba."

"Baka da kirki sam, yarinyar nan fa she's serious akan ka."

"She's not my type."

"Then wace type dinka? Kowacce kace she's not your type, sai ka fada mana type din naka muji ai."

Zura mishi ido yayi, be ce komai ba kawai ya girgiza kai

"Ehen ina jinka, fadi muji type dinka."

"Ok, since you insist."

"Ina ji?"

Ya bude basket din ya shiga fito da kayan dadin da Yasmin ta aiko yana jin kamar an sashi a aljanna, ko kallo basu ishi Tariq ba, ya kishingid'a akan couch din dakin yana yin kasa sosai da idanun sa

"I'm all ears."

Hannun sa ya ware kamar me shirin lissafi yace

"Bana son mace ta cika rama da yawa haka kuma bana son tayi kiba."

"Yasmin is average.".

"That's not all."

"Ok ina jinka "

"I want a shy girl, me kunya sosai bana son wadda idanunta suke a bude,bana son yarinyar da zata ce tana so na, nafi son yarinyar da zata zama very very hard to get, bana son cheap girl"

"Ehen."

"Very beautiful with a soft and long hair, me addini sosai, mara son yawan magana da hayaniya, wadda ta iya girki me dadi...."

"Allahu Akbar."

Ishaq yace yana tura lomar chicken biryani

"Allah ya cika maka burin ka, amma fa banda hard to get din nan, dan za'a iya samun matsala."

"Haka nake so ba wata matsala."

"Toh Allah yabada sa'a Capt."

"Amin." Yace yaja bakin sa yayi shiru dan dama ba kasafai ya fiya doguwar hira ba idan ba da Ishaq din ba.
   Kallon sa ya dinga yi har ya gama cinye abincin tas ya sha ruwa yayi hamdalah sannan yazo suka shiga karatu wanda yawanci Tariq din ne yake guiding dinsa a duk abinda be gane ba, ya bala'in iya mathematics da physics shiyasa ma ya zabi bangaren aviation yana so ya gama yayi training din zama pilot in two years ya hada 1500 hours ya samu Airline transport pilot certificate. Target din shi kenan, kuma ya dauko hanyar cimma shi. Sai dare sosai ya kwanta bayan sun gama karatun Ishaq din ya tafi.

***Sabon part din da Baba ya siya aka soma ginawa wanda ginin yake sauri sosai, duk da cikin gidan aka shigo da ginin amma zai zama basu da wata alaka kowa zata zama tana bangaren ta. Mama ce zata koma sabon part din kowa ma yasan wannan, Aunty bata damu ba sam, tunda itama part din Maman za'a gyare mata a hade da main falon duk cikin nata, sai kuma a bawa su Fauwaz part din Auntyn. Sosai ginin yake sauri dan Baba so yake a gama da wuri Mama takoma a kalla ya san hakan zai rage wata matsalar.
Suna zaune tare da Malam Nura da Alhaji Adamu a harabar gidan, aka kira Baba a waya, ya daga ganin number ce ta PA din Mr President wanda ya kasance class mate din sa ne, tunda ya zama shugaban kasa yake kokarin jawo Baba jikin sa amma sam Baban yaki yarda har sai da ya gamsu dari-bisa dari da yanayi da tsarin mulkin nasa sannan ya amince har aka saka sunan sa a cikin sababbin ministocin da za'a nada, babu wanda Baban ya fad'awa ya dai ce musu zai shiga siyasa su taya shi da addu'a. Daga wayar yayi suka gaisa sannan yace an aiko masa da invitation ta email sannan an yi masa booking flight zuwa Abuja a ranar shima an tura masa e-ticket din. Tashi Baban yayi bayan ya sanar dasu dalilin wayar sukayi masa fatan alkhairi sannan ya shiga gida. Wajen Yaya ya wuce kai tsaye ya sameta da maganar. Rawa ta shiga takawa cikin farin ciki, dariya Baban ya dinga yi har sai da tayi rawar ta gama sannan tace

"Allah ya tabbatar da alkhairi,ya bada sa'a, ya raba ku da sharrin makiya ya baku ikon sauke nauyin da aka dora muku."

"Amin Yayah, Amin ya Allah. Adduar kenan."

Daga nan ya wuce cikin gida ya kira Aunty da Mama zuwa falon sa ya sanar dasu, tashi Mama tayi ta rungume shi da sauri saboda tsabar mamakin maganar, minister fa? Baban matsayi ne sosai wanda yayi daidai da ita, ya kuma dace sosai da ita. Murmushi kawai Aunty take duk kunya ta kamata, sai da Mamaan ta sake shi sannan Aunty tayi masa Allah ya sanya alkhairi. Ya amsa ya saka musu albarka gaba daya, sannan yace Mama ta hada masa kayan da zai tafi dasu kasancewar ita ke girki ranar, dakin sa ta shiga ta barsu su biyu, ya nuna mata kusa dashi yace ta dawo, ta koma ta zauna ya kalle

"Har yanzu akwai abinda yake damunki ko?"

Girgiza masa kai tayi,

"Babu komai."

"Gobe Safwan ya kaiki asibiti a sake duba ki a duba bp dinki, ban yarda da yanayin ki ba."

"Allah ba komai."

"Toh shikenan, in sha Allah kafin na dawo zaa yi kokarin a gama gyara gidan nan, sai kuyi min duk list din abubuwan da zaku bukata, duk da nasan yanzu zaman namu anan ba zai dade ba, amma dai bari muga abinda Allah zai yi."

"Allah ya taimaka ya bada sa'a."

"Amin Halimatu." Yace yana murmushi, fitowa Mama tayi fuskar ta babu yabo babu fallasa dan farin cikin da take ciki ya danne haushin Auntyn da take ji, ciki ya shiga da nufin shiryawa ya barsu a zaune suna jiran fitowar sa, babu wadda tayi magana a cikin su, har ya fito cikin shigar manyan kaya da shadda da babbar riga,ya dora dara akan sa,ya kira Safwan tun kafin ya shiga wanka yace yazo ya kaishi airport. Sallama yayi daga kofa sai da aka bashi izinin shigowa sannan ya shigo, ya russuna ya gaida Baban,sannan ya gaida su Mama.

"Airport zaka kaini." Baba yace yana daga tsaye, Mama ce ta tashi ta dauko suitcase dinsa ta mikawa Safwan din, ya karba ya fita da ita, sannan shima ya sake musu sallama ya fita. Ya rage sai su biyu, Mama ce ta fara ficewa tana bata fuska, sannan Auntyn itama ta fita ta rufo masa part din,da bawa Usman key din tace ya kai wa Maman.


***Sati Baba daya a chan akayi komai ya saka hannu yayi approving aka saka ranar da za'a yi taron nad'a su wanda zai kama kwana biyu tsakani, be dawo ba sai kawai ya aika Mama da Aunty suka zo,sai Kawu Rabi'u da Alhaji Adamu da Malam Nura aminan Baban, sai Safwan.
Jidda, Amira, Umaima da Maryam suka tattara suka koma part din Yaya, ta samu abokan yi aikuwa sukayi ta fama. Washegari suna zaune aka dauko maganar Tariq, Yaya ta zage tana fada musu matsalar sa ta rashin lafiya, ita a lallai sai ta yi convincing dinsu sun yarda ba kalou yake ba. Maryam ce tace

"Yaya fa ras yake wallahi, kawai yanayin sa ne haka yanayin Malam dinki."

"Yo wannan ai har yaci uban Malam wallahi."

"Bari dai kiga a samu wata tayi wuf da kalbinsa, ba ma zaki gane shi ba."

"Kayya, masu irin bakin halin nan fa basu ragawa kowa ba,matan nasu ma su suka fi shan wahala dasu."

"Aiko Ya Tariq zai baki mamaki Yaya, ai shi na zamani ne ba irin Malam dinki ba."

"Toh zamu gani ai, ni wallahi da ma wayata tana irin kiran nan da ake ganin mutum da sai na kirashi na sake jaddada masa maganar shan maganin nan, ku kuma duk ba waya gwara ma ni da yar karama."

"Sai dai na karbo ta Ya Safiyya." Umaima tace tana mikewa

"Yawwa karbo, kice tazo nan nace itama dole na tashi tsaye dan kusan bakin halin su daya da uban gayyaar."

"Yanayin su ne a haka." Jidda tace ba tare da ta kawo komai ba, wani kallo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login