Showing 63001 words to 66000 words out of 120733 words

Chapter 22 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

38897

ba zata ba da sun kyale ta shikenan, amma sai da ta hakura har tazo make up sannan yace ba zata ba..

"Oya, muje ko na daga sama, kinsan kuma zan iya."

Waigawa tayi ta hango wasu saurayi da budurwa a chan gefen su, ta sake waigawa dayan barin shima wasu ne a zaune suna hira, sai kawai ta nufi motar tana had'a hanyaa.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (32)

***Kofar motar a bud'e take, taje ta shiga ta sunkuyar da kanta k'asa zuciyar ta na tururi, agogon hannun sa ya kalla ya kalli cikin motar, ya kad'a kansa ya tako zuwa wajen motar, ya rufe mata kofar ya zagaya ya shiga ya zauna.

"Ki daura seatbelt."

Yace yana jan tasa ya daura, ya kunna motar, hawaye ne ya shiga sauko mata na bakin ciki, duk kawayen su na school zasu je Amira ta fada musu Safeera ma zata wuce daga chan dan ta shigo tana gidan aunt dinta. Sake kallon ta yayi yaga bata daura seatbelt din ba, matsowa yayi jikin ta,ta dago ya kalle ta yayi mata murmushi, irin murmushiin na ci karfin ki, kauda kanta tayi ya jawo belt din ya daura mata, ya tsaya daf da ita bayan ya daura matan, k'in juyowa tayi tana jin ji daf da ita, k'ashin wuyan ta ya kalla, yaga rami, hannu ya kai ya taba ta juyo da sauri

"Har ajiya za'a iya yi a wuyan nan naki."

Yace hannun sa yana kan wajen, fuskar sa a sake yana so ya kure ta, banza tayi masa tana jin yadda yake tafiya da hannun sa akan wuyan nata, wani irin take ji amma ta fuske dan sosai take cikin bacin ran hanatan da yayi wanda bata ga dalili ba.

"Kina wannan kamshin turaren zaki shiga wajen da yake da garadan maza? Baki san darajar aure bane?"

Yace yana kokarin saka idanun sa acikin nata,

"Haramun ne, ki bari mu samu solution sai kiyi ma duk abinda zakiyi, amma dai yanzu na hana,."

"Sai ayi sauri a samu solution din, I'm sick and tired, na gaji."

Sai ya fashe masa da kuka dan ba karamin haushi maganar sa take bashi ba, kullum sai yayi kokarin shiga rayuwarta haka kullun sai ya jaddada mata jiran lokaci yake, ta gaji kawai ya yanke hukuncin da duk ma zai yanke dama ta riga ta shirya. Tsayawa yayi chak yana kallon ta, kukan take bil hakki da gaskiya, ya rasa kwakkwaran dalilin da zai saka ta dinga irin wannan kukan, be sani ba ko zama kusa dashi ne bata so, ko ganin shi ma gaba daya ne bata so. Gashi shi kuma yana jin shi very comfortable duk sanda suke tare, yanzu ma yana samun labarin zasu dinner ya taho hankalin sa ba a kwance yake ba, baya so taje wajen ayi ta kallon ta, ba kuma dan yana so ko kishin ta ba a nasa tunanin, sai dan kawai ya kare martabar auren sa da yake kanta.

"Komai kuka, kuka baya maki wahala ne?"

Ya tambaya yana maida kansa ya jingina a jikin kujerar motar yana duban ta, kamshin turaren ta, na fuzgarshi zuwa gareta, sai dai yayi matukar kokarin hana kansa, yana jaddadawa kan nasa cewa . Kokarin daidaita kanta tayi, ta goge fuskar tana hana kukan cigaba da zuwa, kukan bakin cikin abinda yake mata ya kuma nuna sam be san ma me yake ba, yanzu da tayi magana maimakon ya amsa mata sai ma ya tsaya kawai yana kallon ta, ya kuma sauya zancen zuwa wani na daban. Jin tayi shiru ne yasa shi tashi ya sake kunna motar ya ja suka fice daga wajen.
Kasancewar babu nisa tsakanin nan da gidan ya saka su saurin isa, hakan ya kara tabbatar mata da ba zata je din ba kenan. Sai da ya shiga har cikin gaban part din Auntyn sannan yayi parking, bata jira komai ba, ta bud'e kofar ta fice, maimakon ta shiga nasu bangaren sai ta chanja hanya zuwa part din Yaya. Parking ya gyara ya bi bayan ta da sauri dan ya hango wasu samari a wajen suna zaune, kasancewar da sauri yake tafiya yasa yayi saurin cimmata, ya rufa mata baya yana kakkareta. Ta ganshi sarai amma tayi kamar bata ganshi ba, suka cigaba da tafiya tana daga kafa yana sauke tasa har suka shiga. Yaya na zaune ita da Gwaggo da wasu a falon ta shigo, ta shige dakin Gwaggon da saurin ta, bude baki Yaya tayi zatayi magana sai gashi ya shigo

"A ah, tare kuke ne?"

"Eh." Yace yana shigewa ciki shima bayan ya gaishe su a gajarce

"Ina wajen bikin kuma?"

"Ko har an dawo? Gwaggo tace

"A ah be isa an dawo ba, bari naje naji dan yadda Jidda ta shigo kamar ba kalou ba."

"Toh Allah yasa lafiya."

"Amin." Tace tana mikewa da k'yar dan kafarta ta fara matsa mata sosai. A tsaye ta same shi daga kofar ita kuma jiddaa na saman gadon ta rufe fuskarta, duk kwalliyar da akayi mata ta baci ga shi sai kiran wayarta su Safeera suke Aunty ma ta kirata ta kasa dagawa.

"Ya akayi me ya faru?" Yaya tace tana kallon sa

"Wai dan nace ba zata je dinner ba, shine take kuka."

"Kamar ya ba zata je b? A wanne dalilin yasa ba zata ba?"

"Menene amfanin zuwan toh?"

"Abinda suka dade ana shiryawa zaka hanata fisabillillah, gaskiya baka kyauta ba wallahi, Jidda tashi kinji, daina kukan haka nan kiyi hakuri, kai kuma sai ka gaya min kwakkwaran dalilin da ya sa ka hanata wallahi, dan ni banga dalili ba."

"Ni ba wani dalili, kawai bana so ne, ta bari taje idan babu aure na akanta."

"Ahayyye!"

Tayi shewa tana tafa hannu, kicin-kicin yayi da fuska Yaya ta rasa me ma zata ce

"Ai be kamata ba, tunda dai shi aure daraja ne dashi, kuma ni bana son irin wadannan abubuwan, ta bari a samu hanyar da za'a kawo karshen komai."

"Kai tafi chan, wacce hanya ce da ba za'a iya samar da ita ba har sai an ta maganar ta, ai kawai yanke hukunci ake idan har da gaske har zuciya ana neman hanyar, ba a fatar baki ba.".

"Tashi kinji Jidda, ki rabu dashi bakin hali ne yayi masa yawa da mugunta, idan ba haka ba a gama shirya abu dan gadara ya hanaki zuwa haba."

Tashi tayi idonta har sun daga saboda kukan bakin ciki, gaba Yaya tayi tazo zata raba ta gefen sa ta wuce ya tare hanyar yana mata wani irin kallo da idanun sa suke a shanye,

"I'm sorry."

Ya samu kansa da furtawa dan da gaske yaji babu dadin abinda yayi mata, kin amsa wa tayi zata wuce ya sake tarewa

"Please kiyi hakuri."

"Zan rungume ki idan baki hakura ba."

Kallon sa tayi da sauri, ya gid'a mata kai,

"Da gaske nake Allah."

"Na hakura."

Tace ganin yana matso ta, amma duk da haka sai da yayi hugging din nata,abinda yake taso tun dazu, yana so ya shaki kamshin jikin nata sosai amma kuma yana hana kansa, daga karshe yaga ba zai iya ba, tunda dai ba wani abu yayi ba, kuma ai ba haramci ya aikata ba. Yaya ce tayi saurin fita dan da ta labe a falon, dariya ma ya bata dan tasan dama wuyar ta yazo hannu, irin su masu sum-sum din nan sun fi kowa iya shege

"Almuri." Tace tana zama a in da ta tashi,

"Me ya faru Yaya?"

"Wai ya hanata zuwa wajen bikin dan shegen kishi."

"Abinda kake so ai shi kake kishi Yaya."

"Bar dan bantan uba, yana so yana yare, zai gane shayi ruwa ne, dama ai dan hakkin daka raina..."

"Haka ne, kina ga a yadda ya shigo fa, kamar ma da fari be lura damu ba."

"Ina zai lura so ya rufe masa ido."

"Kai Yaya."

"Allah kuwa, yaga yar karamar yarinya duk ya rude babban kwabo, da yana cika bakin shi baya so yan-yan-yan."

***A yadda yake ji kamar kafarsa ba zata dauke shi ba, gashi duk yadda taso ya kyale ta, ya kasa, sai da wayar sa dage cikin aljihun gefen rigar sa tayi kara sannan ya saketa yana matsawa baya, da sauri ta koma cikin dakin ta kule chan karshen gefen gadon shi kuma ya d'aga wayar ganin Mama ce

"Wai Tariq me kake nufi dani ne?"

"Na'am Mama?"

"Eh, Jidda bata zo wajn nan ba, sai naji labari na yawo a wajen wai kaje ka dauke ta a gidan makeup kace ba zata ba, me yasa zaka je ka dauke ta? Kuma me yasa zaka hanata zuwa? Bangane maka ba kwata-kwata."

_"Ba zan iya bari tazo wajen nan ba."_

yayi maganar kasa kasa amma duk da haka sai da taji shi,

"Ba zaka iya bari ba? Saboda kana kishin ta ko?"

" Ni? Noo ba haka bane, kawai dai tunda ba wai an riga an rabu bane, dole na kare martabar auren, shine kawai amma ba wani abu bayan nan."

"Kasan da yake kai ka haife ni TARIQ, son yarinyar nan kake."

"Mama!"

"Ka dauka ana wa namiji auren dole ne kuma baya son matar yayi hakuri ya cigaba da bin ta kamar jela, ina lura da kai wallahi, duk take-taken ka na gani."

"Amma Mama ba haka bane, ni ba haka bane, ba spec dina bace ba, no ba haka bane gaskiya."

"Sai kayi kuma, na bar baki."

Ta katse kiran, rike wayar yayi saroro a hannun sa yana jujjuya maganar da Mamsn tayi masa a ransa. Duk maganar da sukayi tana ji kuma ta san akan ta ne, kekashewa taji zuciyar ta, tayi lokaci daya, babu amfanin cigaba da zubar da hawayen ta akan mutumin da ya cika da son kanshi, tasowa tayi tazo har gaban sa, ta tsaya sannan tace.

"Kayi sauri ka kawo karshen wannan drama din, kaga sai ka samo daidai da kai din."

Daga haka ta wuce shi kawai ta fice daga dakin, ta wuce part din Aunty ta shiga dakinta,tayi kwanciyar ta,tana hana kanta sake kuka akan sa.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (34)

***Wajen Yaya ta nufa dan tasan itace kai tsaye zata saka Baba ko ta hanashi. Ta kuma san ta yadda zata bullo mata ta daina ragawa Mama dan ta lura shirun ta yasa take ganin har yanzu tana da ikon taka ta. Bedroom din Yayan ta shiga ta sameta a kwance tana hutawa bayan ta idar da sallar walaha, tashi tayi zaune suka gaisa sannan tace magana tazo su yi

"Ina jinki Halima, mecece matsalar? Dan nasan dole akwai magana."

"Yaya dama akan maganar Jidda ce, ni a gani na tunda har Tariq ya dawo Jidda ya kamata ta tare a gidanta, dama taron bikin ake so ayi kuma ya nuna baya ra'ayi ni a ganina kawai ta tare shine mafi a'ala."

"Ni kaina nayi wannan tunanin kuma jiran Alhaji nake ya shigo, dan na ga alama dan ku bashi da ta ido sam, gwara su je chan su karata."

Dariya ta saka Yayan ta cigaba da bayani

"Al'muri da yake munafuki ne ai kinga yadda yake ko? Irin masu halin nan ke dai kawai ki kalle su, sun fi kowa iya shakiyanci."

"Yanzu ki barmun komai, a yau ba sai gobe ba zata tare, dan babu amfanin zaman."

"Allah ya kaimu Yaya, dama dai maganar kenan abun ya soma damuna."

"Ai dole, yarinya ma tayi hakuri ki bari zanyi maganin shi a yau din nan, sai kisa ta shirya duk abinda zatayi zuwa anjima."

"Toh bari naje Yaya, Allah ya kara girma."

"Amin kinji? Allah yayi albarka."

***Komawa tayi ta saka jiddah a gaba, da Safeera da ita suka taimaka mata ta hade koman ta waje daya, hannu bata saka ba ita a lallai ba in da zata tunda be san worth din ta ba, babu wadda tabi ta kanta musamman Safeera da tasan munafurci ne kawai ba har zuciyar, take maganar ba. Falo ta dawo tayi zaman ta, tana kissisima yadda zata kaya a zaman nasu, duk da kaso hamsin tana tsoron Mama amma kuma sauran kason na kwadaituwa da son zama dashi din.
Fitowa Safeera tayi ta sameta a falon suka cigaba da zama sai ga Isma'il ya kirata, dagawa tayi jidda tayi kamar bata gane da wanda suke waya ba, suka dan jima suna magana daga karshe ta kashe tana murmushi

"Ya Isma'il ne, kinsan ya kusa zuwa gida."

"Allah sarki, Allah ya taimaka."

"Amin, ni tunda tafiya zakiyi ma ai ba amfanin zama na, zan koma gidan Aunty Sajida kawai."

"Wai waye yace miki tafiya zan? Ki jira mana ki gani, nasan ba in da zanje."

"Toh zamu gani, yarinya gwara ma ki saka ranki tafiya dole."

"Idan nace ba zani ba ai babu me daukata. "

"Wallahi tsaf zai dauke ki din, tab!"

"Ke kika sani."

"Ke ma kin sani ai."

***Ran Mama ya kai karshe a baci, dawowar ta kenan daga wajen Yaaya da ta turo aka kirata ta fada mata yau matar Tariq zata tare, da k'yar ta amsa da toh ta taso tazo ta fadawa su Aunty Nafi, suka kuwa hau fanfata akan karta yarda.
Kiran TARIQ tayi be daga ba, sai ta kira Fauwaz shima sai da ta katse sannan ya biyo kiran tace masa ina Tariq yazo maza-maza, baya nan dan tun safe da ya fita training be dawo gidan ba, gidan sa ya wuce a chan yayi wanka ya shirya sannan ya koma bacci dan yasan idan be more baccin sa ba ya koma sai ya samu matsala, shiyasa har Maman ta kira be ji ba.
Sai da rana tayi sannan ya tashi ya dan sake gyara jikin sa sannan ya hau mota ya dawo gidan. Tun a hanya dama Fauwaz ya fada masa Mama tana neman sa, shiyasa yana zuwa part dinta ya wuce tana ganin sa tace ya shigo suka shige chan dakin ta in da babu kowa.

"So nake ka saki Jidda a yanzu ba sai anjima ba."

Kawai tace masa ko zama bata iya yi ba. Kallon ta yake hankalin sa a tashe, ta hade rai taki bari ko kad'an yaga saukin ta, kasa furta komai yayi, ya dinga kokarin tattaro kalaman bakin sa amma ya gaza furta su, idan har yace zai iya sakin Jidda yayi karya, duk da ba wai yana mata son da ba zai iya rabuwa da ita ba, amma ba zai zo ya samu matsala da iyayen sa akan ta ba, haka kuma ba zai taba so hakan ta shafi iyayen sa ba

"Mama dan Allah mu bari mubi komai a sannu, dan Allah "

"Babu wani bin komai a sannu, yau kwana nawa kaana min alkawari amma ka gaza cikawa sai bin yar karamar yarinya a baya kamar wanda aka gama dashi."

"Wai Maama waye yace bin ta nake?"

"Kasan ni yarinya ce ai, bansan me nake ba."

"Ba haka bane Mama."

"Toh naji, duk ba wannan ba, bana son zaman ku karkashin inuwa daya, dan haka sai ka sawaake mata tunda ka kasa samun mafita."

"Baba fa? Zai yi fushi dani sosai."

"Ka barni dashi kawai, kai dai kayi abinda nace, ba zan iya jure ganin ta a matsayin sirikata ba."

"Amma Mama, mesa kika tsaneta haka?"

"Tambaya ta kake?"

" A'ah, kawai dai naga kamar yayi yawa ne mama, kiyi hakuri dan Allah mubi komai a sannu, Dan Allah muyi wa Baba biyayya kar muzo muyi abinda zai bata masa suna shi yanzu da yake a idon duniya abu karami zaki ji ana yi dashi."

"Ba zan ba, akan yarinyar nan zan iya batawa da kowa, idan har jinin Halima ce zata auri jini na, na gwammace komai ya faru."

"Mah?"

"Idan har na isa da kai, ka rabu da ita."

"Menene laifin ta a gareki Mama?"

"Babu komai, ba abinda tayi min kawai bana son ta ne."


"Shikenan mama, zanyi abinda kike so, amma ina zuwa Dan Allah."

Fuskarta ce ta fadada da farin ciki, t

"Dan Allah da gaske kake?"

Daga mata kai yayi

"Toh madallah, ka gama min komai Allah yayi maka albarka."

"Amin Ya Allah."

Ya juya ya fita ita kuma ta koma wajen su Aunty Nafi zuciyar ta cike da farin cikin zata kuntata wa Auntyn dan dama tayi alwashin sai ta mata abinda zata dade tana jin ciwon sa.

Ko da ya fita sai ya rasa abinda yake masa dadi, ko giyar wake yasha ba zai iya aikata abinda Maman take so ba, dan ba itace akan gaskiya ba, Baba yafi ta gaskiya dan haka dole ne yasan yadda zai yi be bata wa daya daga cikin su ba.
Iyaye dole ne ka bisu kayi musu biyayya kuma mahalifiya tafi karfin wasa shiyasa yake matukar yi mata biyayya domin samun rabauta. Amma kuma a wannan gabar be san me yasa ba, baya jin yana tare da Maman.
Zaman sa yayi a waje tare da masu gadin gidan lokaci zuwa lokaci yana dan saka musu baki a hirar dan yadda gidan yake cike da mutane bazai sake shiga ciki ba, tunda dai hankalin Maman ya kwanta for now zai tafi da ita a haka kafin yasan abun yi.
Sai da akayi la'asar sannan ya tashi daga wajen, ya shiga cikin dakin su ya hau tattare muhimman takardun sa waje daya, ya zuba su a yar karamar jaka ya saka a bayan mota, sannan ya tafi kiran Yayan da ta turo tana neman sa. Chan cikin dakin ta, ta kule dan ba kowa take so yasan maganar da zasuyi ba. Mamakin ganin ta a nutse a zaune yasa shi shan jinin jikin sa

"Lafiya Yay?"

"Lafiya ta kalou wallahi."

"Menene ya faru?"

"Takardr jidda zaka ban?"

"Takarda kuma Yaya?"

"Eh, tunda baka son ta ba, ka sakar musu 'ya taje ta auri wanda yake son ta."

"Wanene?" Ya bata fuska

"Ina ruwan ka? Wani ne yazo tun kafin ma ayi maganar ka, wai mu masu shishigi da son gwaninta muka ce gida be koshi ba,ashe zaka zo ka watsa mana ido?"

"Aina yake shi din?"

"Oho ba zaka ji ba, ka bata takardar ta ba sai ta sake kwana da igiyoyin auren ka akanta ba."

"Kuma ita ma tana son shi?"

"Kaji mun yaro, ina ruwanka da wannan kuma? Kai tunda ba da gaske kake ba, ai sai kawai ka yanke hukunci Amma ba zai yiwu ka hanata kula kowa ba kai kuma baka so."

Mikewa yayi ransa a baci ya fice be sake cewa komai ba, dariya suka kwashe da ita, Fauwaz dake makale ya fito suka tafa da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login