Showing 45001 words to 48000 words out of 120733 words
Daddy."
"Ok, ba damuwa ka bari ka kara samun sauki, sai muyi maganar fixing date din."
"Ai na warke, please Daddy."
"Shikenan, ka same ni a falo idan ka gama."
"Nagode."
Tapping bayan sa yayi, ya fita shi kuma ya fada toilet.
Tun last two months Daddy yake masa maganar masters da zai fara, ya dinga jan abun saboda ya samu Jidda idan yaso suka daidai ta, sai ya tafi tunda ba yawa just two years ne be ma kai ba, har yaje ya dawo lokacin ta shiga university ta fara karatun ta itama, that was his plan, sai gashi komai ya ruguje a cikin yan awowin da ba su gaza ishirin da hudu ba. Ganin haka ya saka shi yanke shawarar tafiya kawai tunda hatta admission yana dashi a hannu da komai, visa kawai zai yi applying wadda yake saka ran in a week ma zata zama ready, babu amfanin zaman sa tunda har Jidda ta k'i shi, bashi da amfanin cigaba da zama gwara yaje ya amfani lokacin da yake dashi.
***Duk da Jidda taga kiran Safeera kuma ta sake gani ma da safe amma ta kasa kiran ta, bata so ko kad'an su samu matsaala, ta san kuma d'aga wayarta a lokacin zai iya zama matsala tunda ta san a yadda Ya Isma'il ya fita ta kuma tabbatar da sun san abinda ya faru.
Aunty ce ta shigo daga part din Baba, ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, a yanayin da taga Mama zata iya komai dan ganin auren nan ya baci, bata so jiddah ta shiga matsala ko kad'an musamman a irin wannan karancin shekarun nata, dama dai duk abinda ta guda kenan, dan dai su iyaye maza basa bawa ire-iren wadannan abubuwan muhimmanci ko kadan, tayi mamaki da har Maman ta dauko kafa tazo, har kuma suka samu sabani da Baba akan hakan wanda ko lokacin aurenta da Baban basu samu irin wannan matsalar ba dan Mama mutum ce me matukar kissa da iya takunta a wajen Baban dan duk wuya bata taba bari yaga aibun ta, amma kuma a yadda ta kasa dauke idon ta akan wannan auren ne ya sakata sake tsorota da lamarin.
Wayar Jidda ce ta sake kara a karo na uku tun shigowar aunty, ta kalle ta cikin son neman karin bayani tace
"Ki daga mana ana ta kiranki kina ji."
Yadda Auntyn tayi sounding yasa ta gane ranta a bace yake, daga wayar tayi sannan tace
"Hello Safeera."
Wani kallo Aunty tayi mata, sai ta tashi sum-sum-sum ta bar falon zuwa dakin ta, girgiza kai kawai Aunty tayi,ta shige daki itama ta hau tunanin yadda zasu fara hada kayayyakin da zasu bukata a chan din dan ba komai zasu dauka ba.
***Shiru jiddah tayi tana sauraron banbamin masifar da Safeera take akan kin daga wayarta bayan tasan dole ne ta kira ta, sai da ta gama tas duk da bata sako maganar Isma'il din ba sannan tayi shiru Jiddan ta bata hakuri
"Bana kusa da wayar ne, kiyi hakuri."
"Ko dai kika ki dagawa ba, kar nayi miki maganar Ya Isma'il."
"Ba haka bane ba fa."
"Toh me? Ni dai ban ce miki dole ki so shi ba, babu dole ai a soyayya, dama kiran ki nayi muyi wata magana amma shikenan."
Ta wayance kawai dan bata ga amfanin dawo da maganar baya ba, ita da kanta Jiddan idan taga ta share zancen zata saki jikinta har ta bata labarin abinda ya faru.
"Dan Allah fada min, wacce maganar ce?"
"Ah ai kuma shikenan, idan kin matsu kina so kiji ki kirani da kanki."
"Toh zan kiraki, kinsan me ya faru? I'm clueless gaba daya, bansan ma wanne irin tunani zan ba."
"Oya,tell me ina jinki."
"Uhm... Jiya aka daura min aure."
"Wait what!!!" Ta fada da dan karfi dan yadda maganar tayi shocking dinta
"Kamar ya? Ban gane ba, aure kuma, da wa?."
"Ya Tariiiiq."
Dip Safeera ta dauke wuta, kamar bata kan wayar, sai da ta ja wasu yan sakanni sannan tace
"Yanzu dama all this while jidda kinsan yayanki za'a aura miki amma kika ki fada min,haka kika dauki friendships dinmu? Baki yi trusting dina ba ko? Shikenan nagode."
Ai kafin Jiddah tayi magana ta katse kiran, ta kalli wayar ta girgiza kai kawai, me neman kuka ce dama aka jefe ta da kashin awakai, dama zuciyar Safeern a kusa take da abinda ya faru tsakanin su da Ya Isma'il, sai kuma katsaham tace mata an daura mata aure bayan dah tana dan da hope din ko aka kara turawa Ya Isma'il din ya samu kanta, duk da tasan Jidda kaifi daya ce tun basu kai yanzu ba,idan tace yes toh babu abinda zai sakata dawowa tace no, haka ma vice versa.
Sanin cewa sarai ko ta kirata ba zata daga ba, ya sakata tura mata sakon text message, tayi mata bayanin abinda ya faru a takaice, ta ajiye wayar daidai lokacin Aunty ta kwalo mata kira, da saurin ta, ta amsa ta fita dan ta lura sarai Auntyn a wuya take akan maganar auren nan.
A daki ta sameta ta fito da kayan wardrobe dinta gaba daya, tana ware su,zama Jiddan tayi ta shiga tayata, anan take fada mata maganar tafiyar, shiru tayi dan bata kuma san kalar sabuwar rayuwar da zasu fada ba, tun bayan komawar Maman Abuja aunty ta samu yancin kanta, bata da wata damuwa dan idan ba sallah da akayi ba suka zo babu wani abu da yake hada su waje daya, shima har a gama hutun sallar su tattara su koma ba wani zama Maman take a gidan ba,kullum cikin fita take.l shiyasa yanzu take hasaso irin zaman da za'a yi, gata kuma, wanne irin tarbar Maman zata yi mata? Shin zata taba karbar ta kuwa a matsayin matar Baban danta? Toh wai me da sanin ta kuwa akayi auren nan? Sai ta tuna da sunan bararojin da ta taba kiran ta dashi cikin son nuna kaskancin ta, ajiyar zuciya ta sauke, dan tasan tabbas akwai kalubale babba a gabanta, amma koma menene tana rokon Allah ya duba ta, ya kawo mata sauki.
Suna aikin Aunty na kokarin nuna mata rayuwa da kalubalen da yake cikin rayuwar aure, taana ji tana kuma daukar komai a kanta, har suka kammala aikin taje ta zuba abinci ta koma dakin ta, taci sannan itama ta hau ware kayan nata, tana daukar wanda zata bukata ta. Hakan ya jata har yamma dan sai da ta hada komai kaf dan zataje tayi kwana biyu a gidan su kafin ranar tafiyar da zata dawo ana I gobe. Sai da ta gama tas sannan ta dauki wayarta, taga reply din safeera, tayi murmushi kawai ta sake tura mata wani,
_"Wednesday zamu koma Abuja."_
Sakon na shiga ta biyo shi da kira, ta dauka tana murmushi dan tasan wata masifar ce
"Nima wallahi dazu na san da tafiyar." Tayi saurin cewa tana dariya
"Allah Jidda ko? Yanzu dan Allah shikenan tafiya zakiyi ki barni? Ni kadai ga Ya Isma'il shima tafiya zai,haba dan Allah."
"Zamu zo sallah fa, ko weekend nasan ba wai mun tafi gaba daya bane, ni ma ba son tafiyar nake ba, kinga achan zamu fara school ni da Amira shiyasa ma."
"Ai shikenan, zan shigo gobe."
"Ok Allah ya kaimu, sai kinzo."
"Amin, bye."
"Bye."
Maimakon ta ajiye wayar sai ta samu kanta da shiga photos din wayar, ta bude hotunan sa, tana dubawa,tana tuna wai mijin tane,an daura musu aure, bata san me take ji game da hakan ba, kawai tasan tana jin ta at ease, bata da wata damuwa ko fargaba a zuciyar ta. Ba kamar idan taga Isma'il ba, ba kuma kamar ace Isma'il aka aura mata ba, ta tabbatar zata iya bori akan hakan.
Ya Fauwaz ne ya kirata, tana dagawa ya hau yi mata kirari
"Kaga amaryar Ya Tariq, kaga amaryar Captain Tariq, kaga amaryar international pilot, eh Masha Allah, ban taba ganin perfect couples irin ku ba, kun yi matukar dacewa, da za'a bada award za'a iya baku award din perfect couples of the year."
Dariya take tunda yafara maganar,
"Kai Ya Fauwaz." Tace farin ciki na mamaye zuciyar ta
" Allah da gaske Jiddo, auw Aunty Jidda."
"Na shiga uku, nice Auntyn?"
"Emana, kin zama matar Big B, ai dole ace miki Aunty."
"Kai dai Ya Fauwaz ka iya tsokana wallahi."
"Allah ba tsokana bace, da gaske nake. Har Allah, Allah nake ya Tariq ya dawo yaga amaryar sa, nasan ji zai yi kamar an tsunduma shi a aljanna."
"Hum umm." Tace tana giggling
"Toh ya ake ciki?"
"Alhamdulillah wallahi."
"Toh Masha Allah, dama nace bari na kira matar yaya, kar ya dawo yace mun bar masa mata babu kulawa."
"Ya Fauwaz ko?"
"Na barki lafiya toh."
"Nagode."
Wani irin dadi ne ya rufe ta, dan ba karamin dadin kalaman Fauwaz taji ba, ya bata kwarin guiwa sosai wanda har ta soma hasaso rayuwar ta anan gaba kad'an. Murmushi tayi tana lumshe idanun ta, ta furta a hankali.. Matar Ya Tariq
***Washegari da wuri Safeera tazo, suka shige daki suka shiga hira, har kusan azahar sannan ta je ta kawo musu abinci suka ci sukayi sallah, sannan Safeeran tace zata tafi dan Mom ma da kyar ta barta tazo dan dai tana son duk abinda suke so ne, mayafi ta yafa ta rakota gate in da driver gidan su yake jiranta. Hakurin abinda ya faru tsakanin ta da Ya Isma'il ta bata dan duk yadda taso dauko maganar da suna ciki Safeeran taki yarda da ta dauko maganar sai ta goce da ta sake daukowa sai ta shashantar da maganar ko ta nuna bata ma ji ba. Yanzun ma tsaki tayi kawai ta harare ta,ta shige mota. Part din Yaya ta wuce ta sameta kafarta na mata ciwo, ta dauko maganin da ake shafa mata, ta shafa mata a kafar sannn ta zauna tana rage mata zaman kadaitar.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (24)
***Kwanan ta biyu a gidansu, Baffa yayi mata nasiha da kashedi sosai akan abinda ya faru, ya kuma ja mata kunne sosai akan kar yaji kar ya gani, duk a tunanin sa zata bijire, be san da gaske take son abun. Wuni tayi ranar da tazo a gidan Saude wadda akayi bikin ta da kaka, bata samu zuwa ba lokacin suna examz, gashi hadda tsohon cikin ta, sun sha hira suka tuna da sannan ta dawo da la'asar sakaliya.
Iya Lami nata haba-haba da ita,ta share ta kamar bata san Allah yayi ruwan ta a gidan ba, dan ko kad'an bata son matar dan babu kalar azabar da bata gana mata ba, akwai wani duka da tayi mata har yanzu da ragowar shatin dukan a gadon bayan ta abunka da fara. Shiyasa taki sakin jiki da ita sam bare ma su zauna suyi doguwar magana. Ranar da zata tafi Aunty ta turo aka dauketa, dan ta karasa abubuwan da bata karasa, dan da safe zasu tafi washegari.
A tsakar gidan Yaya ta tarar dasu ana ta fama da Yaya tayi tsalle ta dire babu shegen da zai sakata shiga jirgi, idan kuwa akace dole toh ta fasa tafiyar, duk yadda Fauwaz da yazo yaso ya fahimtar da ita sam taki fahimta, kamar ma a tsorace take da al'amarin, gashi a wannan yanayi na insecurity babu yadda za'a yi a barta ta shiga mota, haka kuma a barta ita kadai ma matsala ce.
"Yaya menene?" Tace tana matsawa kusa da ita
"Yawwa gwara da Allah ya kawo ki, kiji dan wulakanci wai jirgi zamu hau idan zamu tafi."
"Eh Yaya, ba bata lokaci nan da nan zaki ga anje."
"Aikuwa banga uban da ya isa ya sakani hawa jirgi ba wallahi."
"Har Baba?" Fauwaz yace yana dariya
"Ko Kaka ne, ehe."
"Ah abun azimun ne, bari na kira Baban da kansa yayi miki magana, kila shi yayi convincing dinki."
"Duk ma me zakayi kayi, na gama magana."
"Muje ki zauna Yaya, ki daina yawan fada kina tada hankalin ki dan Allah."
"Toh yaran nan ne duk hanyar da zasu birkita min lissafi sun santa, ina dalili za'a ce dole sai na hau jirgi? Ai ba dole bace Habujan ko? A kyale ni dan Allah.".
Sai ta fara tari da karfi, saurin tallafa mata jiddah tayi, ta mika mata ruwa tasha tarin ya lafa, zata cigaba da sababi Jidda tayi saurin cewa
"Kiyi shiru karki sake tarin, ba in da zaki a jirgi, a mota zamu tafi ni dake sai su suyi ta hawa jirgin su."
"Yawwa toh idan hakan ne na amince."
Kallon Jidda Fauwaz yayi, kallon kunfi kusa ya juya yana ayyana yadda zai yiwa taurin kan Yayan. Be kira Baban ba kamar yadda yace, sai kawai yaje ya samo maganin bacci, ya ajiye a daki, da safe bayan sun shirya tsaf, sun fito ya dauko lemon exotic madaidaci ya saka mata maganin baccin dan daidai wanda ba zai bugar da ita ba, ya shiga part din ya sameta ta saka sabuwar atamfar ta, da sabon Hijabin ta fari kal, sai takalmin shima sabo tana cike da jin dadi ga sabon lalle a kafar yayi har ya soma duhu-duhu.
"Ya ka gani?"
"Kin fita fes fes ko ba sabula mutuniyar."
"Godiya nake kaji, kasan fa kakanku tsabar dunkum dinsa ko yaba abu bayayi, ni bansan dadin kayi abu miji ya yaba ba, sai bakin rai da turbune fuska kamar shi aka dorawa baki daya matsalar Nigeria."
"Innalillahi, wai Yaya ba zaki kyale bawan Allahn nan ya huta ba, ko me yayi ai yaci ace an yafe masa haka nan."
"Toh ubana, sai ka fada min abinda ya kamata nayi tunda kai ka haife ni, ko kai kake bani ci da sha."
"Allah ya huci zuciyar Hajiye Dije, ga exotic na kawo miki kisha idan kun shiga mota, sai mun hadu a chan dan mu dai jirgi zamu hau."
"Ah ka kyauta, kasan kuwa dama na kwana biyu ban sha ba, shegen likitan nan bakin mugu wai a hanani shan kayan zaki kamar shine ubana, shikenan Alhaji yasa akai daina siyo min."
"Yanzu dai gashi nan na kawo miki, kisha karki bawa kowa fa, naki ne ke kadai tawan."
"Uban yan dadin baki, naji ni kira min jiddah mu dau hanya, kar muyi dare duk da dai ance sannu sannu bata hana zuwa sai dai a dade ba'a je."
"Gani ma Yaya." Ta shigo sanye da atamfa lemon green and orange tayi mata kyau sosai har sa da Yaya ta kasa dauke ido daga kallon ta
"Wai wai wai, chanchadi."
A kunyace ta karaso ciki, Fauwaz yayi mata signal da ido yana nuna mata juice din hannun, ya fita. Bata gane komai ba, sai ga message dinsa bayan ya fita
"Make sure tasha juice din nan, sai mun hadu a airport."
Kallon juice din tayi ta kalli Yayan,
"Kisha lemon naki Yaya sai mu tafi, an gama saka kayan a mota."
"Auw toh." Tace tana bud'e murfin, ta kwankwade shi tas da dan sanyin sa dama, jidda ta karbi kwalin ta jefa a dustin sannan suka fito harabar gidan, ta taimaka mata ta shiga motar itama ta shiga, sannan suka fita daga gidan, suna fita motar su aunty itama ta bi bayan su ita da Usman sai Fauwaz din a gaba.
Bacci ne ya soma daukar Yaya sama-sama, jiddah na kallon ta, ta gyara mata ta jingina sosai bacci me nauyi ya dauketa. Suna isa airport din aka samo wheelchair aka dora ta, aka sakata a cikin jirgin suka lula sai Abuja.
***Sabuwar Rayuwa! Sabon Shafi***
Baki sake Jidda take kallon garin yadda ya tsaro, bata dai taba hasaso haka Abujan take ba, ta dai san tana da kyau amma bata kawo haka ba,sosai yayi mata kyau kwarai, ta kalli Aunty sukayi ma juna murmushi, har lokacin Yaya tana ta sharbar baccin ta.
Unguwar da suka shiga ita ta sake rikita Jidda har ma da Aunty duk da tana boyewa, babbar unguwa ce da manya manyan gine-gine tsararru, cikin tsari gwanin sha'awa. Shiru babu motsin kowa ba zaka taba cewa akwai halittu da suke rayuwa a cikin wajen ba
A kofar wani babban tangamemen gate suka tsaya, gate din ya bude da kansa suka kutsa kai cikin katafaren filin gidan, wanda yake dauke da motici manya daga chan gefe, sai shuke-shuke masu ban sha'awa.
Wani matashi ne yazo bayan sun tsaya, ya bud'e musu kofar ya russuna ya gaida Auntyn sannan yace
"Ga part din chan."
Ya mika keys din, karba Jiddah tayi, Fauwaz ya zagayo ya leka Yaaya da take ta sharbar bacci, ya kalli aunty ya kwashe da dariya
"Ya za'a yi da ita yanzu Aunty?"
"Ai baka kyauta ba wallahi,."
"Aunty bansan ya za'a mata ba wallahi, kinsan kafiyar Yaya."
"Ni dai kar a samu matsala fa."
"Babu in sha Allah, peaceful bacci fa take, kuje bari na kirawo masu aikin nan na bq su taimaka sai a kai ta part dinta."
"Je ka kirasu dai ina nan, Jidda jeki ke da Usman gani nan."
"Toh." Tace ta rike hannun sa suka nufi shashen da aka nuna musu,tun kafin ta karasa take admiring ginin bare kuma ciki. Wani security ne daga gate ya taso, ya dan russuna ya gaida Auntyn sannan yace ko akwai matsala, girgiza masa kai tayi tace babu, ya bata hakuri ta koma wajen aikin su, gwada tashin Yayan tayi ta dan tattabata sannan ta kira sunan ta, a hankali ta bud'e idon da kad'an kad'an har ta gama gaba daya,sai ta kalli motar da take ciki ta kalli Aunty
"Kar dai har mun karaso ina ta bacci."
"Eh Yaya, ai wai ashe tunda kuka dauko hanya kike bacci zuwan ku kenan, jidda tace kina mota kina bacci shine nace bari nazo na taimaka miki."
"Wai gaskia nasha bacci, awa nawa kenan ina baccin?"
Ta zuro kafarta waje ta sakko, sai taga kamar lokacin suka baro gida, kamar zatayi magana kuma sai ta fasa hango Fauwaz na nufo su da wasu mata kedaru su biyu, kana ganin su kaga karfafa.
"Ah ashe ma ta tashi."
Sai ya juya wajen su yace
"This is the second Madam, greet her."
"Good morning Ma'am."
"Good morning." Tace a takaice
"You can go." Ya ce suka juya zuwa in da suka fito, salati Yaya ta rafka tana tafa hannu
"Yanzu tsabar lalacewar ta kai lalacewa har da arna a gidan nan, na shiga uku ni Hajara yau naga abinda yafi karfi na."
"Kai Yaya, house help ne