Showing 48001 words to 51000 words out of 120733 words
fa, kuma ba arna bane kawai dai basa jin hausa ne."
"Toh dan tsabar iyayi a rasa irin ma'aikatan da za'a dauka sai wannan zandara-zandaran zawarawa? Wai na shiga uku na lalace."
"Fito na rakaki bangaren ki, kin ga yadda aka miki kuwa, harda katuwar TV ta bango gas fridge dinki cike da kayan dadi, kuma Baba yace zaa dauko miki gwaggo kuyi zaman ku."
"Da gaske?" Ta washe baki tana fitowa gaba daya,
"Muje ki gani, Anty sai mun shigo."
Yace yana rike hannun Yayan, ita kuma Aunty ta nufi part din da jiddah ta shiga, wanda yake da yar tazara tsakanin su da wani hadadden part da yake a tsakiyar gidan wanda aunty ta tabbatar na matar gidan ne.
A tsaye ta samu su jidda suna karewa yar karamar daular tasu kallo, ita kanta Auntyn sai da ta jinina, yayi kyau sosai duk da ba wani katon gani bane, kayan su aka shigo musu dasu, sannan Auntyn ta lallaka dakunan ta nunawa jiddah nata ita ma ta shiga nata.
Amira ce kawai ta rage a gidan duk sun tafi school itama bacci ta koma bayan tayi sallah tunda tasan zuwan su jiddan ba lokacin bane. Wajen sha daya ta tashi, tana sakkowa daga gado tayo waje, suka hadu da Mama a falo tana duba wayarta, da kallo tabi Amiran kamar ta fuzgo ta, ta dake ta haka takeji dan yadda take son jiddah ko ciki daya suka fito sai haka. Bata dai kulata ba har ta fice ta kuma san in da zata dan taga shigowar su gidan ta window, ta kuma ga duk abinda ya faru tsakanin su da Yaya duk da bata ji me suke cewa ba, sakin curtain din tayi kawai ta cigaba da abinda takeyi.
Da sassarfa ta isa part din sannan tayi knocking, Jidda ta zo ta bud'e suka rungume juna cikin tsananin farin cikin ganin juna. Fitowa Aunty tayi da murnar ta, Amiran ta gaishe ta sannan suka kule dakin jiddah ta tayata hade kayan ta waje daya a cikin wardrobe suna yi suna labari, yawanci akan school din da zasu fara zuwa ne next week da kuma yanayin rayuwar garin da yadda zasuyi mingling da yaran manya, ita dai jiddah ta san matsayin ta, bata sa a ranta zatayi rayuwa irin ta su ba, saffa saffa dai kar ta zak'e, duk da haka tasan dole ne ko taki ko taso rayuwar ta sai ta sauya ta sake daukar ta zuwa wani bigire na daban.
***Dawowar su Abuja ya sauya abubuwa da dama daga rayuwar Jiddah, sati daya cif da zuwan su suka fara zuwa wata private university a abujan, course daya sukeyi sai ya zama kullum tare suke duk in da kaga daya zaka ga daya. Sai dai a wajen da Jiddan tasan zai iya shafar matsayin ta na matar aure, wanda ta rike hakan da matukar muhimmanci, bata kuma sakaci bare ta yi wani abu da ya sabawa Allah.
Sau biyu taje gaida Mama a satin da suka zo amma da kyar take amsawa, tayi saurin barin wajen, haka Jiddan zata tashi jiki a sanyaye ta bar part din, na farko aunty ce tace taje ta gaishe ta lallai dan da, da yanzu ba daya bane, akan haka taje amma sai data gwammace bata je ba, haka dai ta daure ta sake zuwa a karan kanta bayan Amira tazo wajensu tayi mata korafin zuwa nasu part din, nan ma dai same abinda ya faru da farko shi ya sake faruwa. Duk abinda ya faru bata fadawa Aunty ba, boye mata kawai tayi a matsayin babu komai dan taga yadda Auntyn take tada hankalin ta akan maganar auren.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (25)
1 year later
Bayan shekara daya
***Abubuwa masu yawan gaske sun faru a cikin shekara gudun nan, Jidda ta samu sauyi na ban mamaki, yanayin society din, da yanayin rayuwar school da mutanen da suke mingling ya taimaka kwarai wajen karuwar wayewar ta, ta goge sosai musamman da dama bata da duhun kai, mutum ce da take kokarin tafiya da yanayin da yazo mata na sauyi cikin nutsuwa da karantar rayuwa.
Rayuwar Abuja ba kamar rayuwar Kano bace musamman da suke mingling da mutane mabanbanta masu gogewa da wayewar sanin rayuwa, duk da haka bata yi wasa da martaba da darjaar da alalh ya dora mata ba, a matsayin ta, na me aure, dan iyakar kokarin ta, tayi wajen kare kanta da duk wani abu da tainakon aunty da nasihar Baffa da baya kwana biyu sai ya tisa mata matsayin ta, da ita din wacece. Bata da matsala kowacce iri ce, duk wani abu na jin dadin rayuwar Baba yana musu musamman ma ita da ya dauke responsibility din Tariq, hatta abinda bata ce tana so ba yi mata yake yi, tsakanin ta da Mama babu shiru daga gaisuwa shikenan shima ba wai tana amsa mata kai tsaye bane. Hakan tun yana damunta har ta hakura ya daina damun ta, bayan Aunty ta zaunar da ita tayi mata bayanin dalilin daukar zafin Maman na rashin sanar da ita komai sai bayan an daura, wanda Aunty tayi mata uzuri sosai dan tabbas tasan baa kyauta mata ba, hakan yasa Jiddah cire damuwar yadda Maman take mata cike da fatan watarana zata so ta, ta karbe ta kamar yadda sauran iyayen miji ke karbar matan yayan su.
Fitowar ta kenan daga wanka sun samu hutun end of semester saboda haka basa fita musamman ma ita dan su amira an samu kafar yawo ba'a zama kwata - kwata, tun wanchan satin labarin dawowar Ya Tariq ya sameta, sai taji gaba daya ta rasa nutsuwa da sukunin ta, duk abinda take tunanin yadda zata kaya take, duk da a kullum Ya Fauwaz da Amira na kara mata kwarin guiwar babu namijin da zai ki ta, a yadda take a yanzu, da haka ta samu dan peace of mind har take biyewa aunty da Yaya wajen shirya ta.
Riga da skirt na cotton material ta dauko ta saka, sai taji skirt din ya matse ta, kusan dukka skirt dinta sun matse ta saboda yadda ta samu sauyi a jikin ta, a lokaci daya, duk da har yanzu bata da wata kiba ta azo a gani amma babu laifi tana da front and back shape dinta me matukar kyau da daukar hankali shiyasa a kullum take cikin shigar kirki haka idan Ya Fauwaz zai shigo takan saka madaidacin Hijab akan kayan ta, ita kanta mamakin kanta take da yadda a lokaci daya ta ciko ta bayan amma cikin ta kamar bata zuba masa komai saboda yadda yake flat a koda yaushe. Zare skirt din tayi da kyar ta dauko doguwar riga plain ta saka kawai ta yafa medium veil a kan dogon gashin ta wanda ta nannade shi ta tura shi a cikin gashin saboda yadda yake sakkowa gadon bayanta duk lokacin da ta sake shi.
Part din Yaya ta nufa in da ake mata gyaran jiki, a chan ta samu su Amira dukkan su tare da me gyaran jikin. Bikin Safiyya da Umaima za'a yi, sai Baba yace sai a hada da na su Jidda din suma ayi shagalin bikin tare, sanda ya fada sai da fuskar Mama ta chanja sosai dan ko sunan Jidda bata so taji ana hadawa da na Tariq, dan dai ma ta shirya nuna musu itama nata karfin ikon akan Tariq din, shiyasa take bin komai a sannu kar ta bata goma biyar bata gyaru ba.
Tare ake musu gyaran jikin da matar da maman ta dauko tayi musu dan shirin biki take gagarumi, kasancewar bata son abun magana shiyasa tace su zauna a wajen Yaya anayi musu dukka a chan dan bata son shige da fice a part dinta.
Tana shiga Amira da Maryam suka hau tafi
"Kinga yadda kike glowing matar yaya, lallai idan Ya Tariq ya dawo sai ya kusan susucewa akan ki, ji yadda fa fataarki ta zama kamar ta jarirai."
Dariya ta saka, ta kai wa Amira dake kusa da ita dundu ta goce
"Kun cika sharri wallahi."
"Allah kuwa, dan Allah Aunty Yagana baki ga yadda skin dinta ya kara komawa ba?"
"Na gani fa."
"Toh kinji dai, ba wai zuga ki muke ba."
"Yo idan ma zugar ce kuyi tayi mana, nan gani da nan bari dumamen mayya."
Yaya ta shiga zancen tana hararar su
"Kai Yaya, me yayi zafi har da bakar magana."
"Anyi din, iyayi ne ni bana so." Tace tana yatsine fuska.
Harara ta Maryam tayi tana juyar da fuskar ta gefen da babu kowa amma da Yayan take, shewa tayi ta buga zani, ta taso har gaban su tace
"Bansan anayi ba, kunu a wani gida, idan an isa dai a yi a gabana mana."
"Yaya dai kina son tarewa Jidda abinda mu fa wasa muke tsakanin mu, amma kin hakikance kamar gaske, haba!"
"Cewa tayi tana son wasa ne, kaji min yara, ba matar yayanku bace, ku bata girmanta"
"Kai innalillahi, wallahi Yaya zama dake sai an shirya, duk dai take-taken korar mu kike daga wajen nan, ba kuma in da zamu wallahi."
"Sai kuyi tayi ai, jaraba. Taso Jidda muje kiga wani abu, irin hade-haden tsofaffi ne amma yafi shirmen da ake baku na wannan zamanin."
"Ahaap, dama duk munsan kwanan zancen, shiyasa kike korarmu, wallahi Jidda ki kiyayi concoction din da Yaya take hada miki, sai kinje ta zugar miki da ciki kafin karshen sati kizo duk ki rame."
Maryam tace tana yin hanyar fita dan tasan ko ta zauna ma Yaya sai ta mata dundu
"Ba ruwanku, tsakanin mu ne da Yayata."
Jidda tace tana dariya,
"Shikenan mu yan kallo ne."
"Muje Yaya ki bani." Taja hannun Yaya, suka shige bedroom dinta, ta karbi hadin a wata robar ruwan nestle, ta ce zata je tasha a daki, da wayo dai ta lallaba yayan ta raba ta dashi, sannan taje ta ajiye a kitchen din part din Aunty ta dawo aka shiga yi mata gyaran jikin.
***Mama na zaune suna waya da Aunty Nafi tana sake kasheda mata kar ta kuskura yarda da zabin da akayi ma Tariq gwara ko Salma ce su hada su. Shiru Mama tayi tana jin ta, duk da dai bata son jiddah amma ba zata yi wa Tariq irin auren da Baba yayi masa ba, zata bashi damar ya kawo wadda yake so da kansa tunda ba wai ta gamsu da tarbiyyar Salman bane duk kuwa da alakar su.
Sallama sukayi ta katse kiran ta kira Tariq din da Ishaq ya jashi zuwa yin siyayyar abubuwan da zasu taho dasu gida, da fari ki yayi amma da yayi convincing dinsa sai ya yarda ya bishi. kayayyaki ya sissiyo nasa sai kuma ya siya ma yan gidan nasu kaf har Aunty da Usman. Suna hanyar dawowa kiran Maman ya shigo, ya daga yana gyara Bluetooth din dake kunnen sa
"Tariq." Ta kira sunan cikin yanayin nuna kaguwa
"Mama barka da gida, kuna lafiya?"
"Alhamdulillah, ya shirye-shiryen tahowa?"
"Gashi fa, muna yi yanzu muke komawa gida daga shopping "
"Masha Allah, we all can't wait to see you "
"Nima Mama."
"Um um kai ai baka damu ka ganmu ba, tunda kiri-kiri kaki zuwar mana ko hutu ne, nima kuma ka hanani zuwa."
"Toh gashi Mama yanzu har an gama zan dawo ma."
"Still dai."
"Toh I'm sorry, ba zan sake ba."
Murmushi tayi me sauti ganin yadda Tariq din yake waya da ita, tabbas akwai sauyi sosai a dangane da mu'amular sa, yanzu kuma an kara girma dole abubuwa zasu chanja
"Shikenan toh, sai kun isa gida ka kirani akwai sakon kayan da nake so kaje ka siya ma sisters din ka."
"Ok Ma, ina komawa zan kira."
"Allah yayi maka albarka."
"Amin."
Ya amsa cike da jin dadin addu'ar da tafi masa kowacce.
***Sati biyu ya rage bikin gidan duk shirye-shiryen da ya kamata ayi duk an yi hatta wajen da za'a yi shagalin an kama komai dai cikin tsari dan ba karamin shiri akayi ba. Duk da kudurin Mama na ganin Tariq ya ki Jidda hakan be hana ta cigaba da duk shirye-shiryen tare da jiddan ba, hakan ma cikin kissar tace dan bata son ta sake nunawa Baba itace bata so, tafi so Tariq din yazo da kansa wanda tasan tilas ne yaki jidda.
Su uku ne a motar, Ya Fauwaz da yake tukawa, Umaima na gaba sai ita da Ya Safiyya a baya, hira suke gwanin sha'awa dan ita babu abinda zata ce tsakanin ta dasu sai godiya musamman tun bayan da aka daura auren ta da Tariq suka sake jan ta a jiki sosai.
A gajiye suke dan duk abinda suka san zasu bukata sun siya dan ba kuma sake fita zasuyi ba inji Mama, ita dai Aunty tana gefe tana kallon ikon Allah dan dai duk wani abu da ya kamata ayi wa Jiddan Mama da Yaya sun dauke, sai dan abinda ba za'a rasa ba. Kayan ta ta dauka a booth, Ya Fauwaz yayi saurin karbewa yana girgiza mata kai
"So kike Ya Tariq ya dawo ya hukunta ni kenan, na bar her royal highness da daukar kaya."
"Gaskia dai Ya Fauwaz." Umaima tace tana dariya
"Muje na kai miki dan nasan idan ya dawo gobe duk sai ya bincike mu yadda mukayi treating dinki idan ya samu daddad'an labarin nan."
"Ya Fauwaz kai ko?"
"Ai gaskiya ce." Safiyya tace suka saka dariya. Tare suka jera dashi yana sake tabbatar mata da yakinin sa na yadda zata sace zuciyar Ya Tariq a lokaci daya, duk da akwai tsoro sosai a k'asan zuciyar ta amma duk sanda Ya Fauwaz ya bata hope sai taji tana samun kwarin guiwa, sau tari ta kan hau kan profile dinsa tana duba shi, ta kan ganshi online wani lokaci duk da ba kasafai ya cika hawa ba, tasha gwada yi masa magana sai ta kasa, tayi hakuri sosai sai gashi har lokacin yazo.
Ajiye mata kayan yayi a falon Antyn, ya juya yana sake jaddada mata gobe ne fa, murmushi kawai tayi ta tattare kayan ta wuce dakin ta, ta ajiye su ta shiga toilet don yin alwala.
***Washegari da wuri kowa ya tashi a gidan, cikin shirye-shiryen tarbar shi, Mama ta kasa zaune ta kasa tsaye da gaske take cike da farin cikin dawowar sa, har ta gaza boyewa, sai da Baba ya tsokane ta. Bangaren Hajiya Yaya ma tana cike da farin cikin dawowar sa, wanda ko ba'a fada ba a cikin jikokin nata tafi son Tariq din, saidai yanayin sa tasa suke rigima sosai har ka zata ko bata yin shi ne.
Tsaye take a kitchen ita da Aunty suna shirya masa girki, mai rai da lafiya, baki daya ta bada dukkan attention dinta akan girkin, duk da sun fara da wuri amma har aka zo tafiya airport dauko shi bata gama ma bare ta samu tayi wanka, Amira ce ta leko kitchen din da ganta da doguwar riga zurum tana ta aiki ta kwashe da dariya
"An shirya fa, har ma mun fito nace bari na leko ki."
"Ai dama ba zuwa zan ba Amira, sauri dai nake naje nayi wanka."
"Auw har Ya Fauwaz yace ki fito."
"A ah kuje, sai kun dawo."
"Ok matar Yaya."
Dariya sukayi a tare ta fice ita kuma ta maida hankalin ta akan aikin, ganin lokaci na tafiya ya saka aunty cewa taje tayi wanka zata karasa ita da Badiya me aikin ta. Wanke hannun ta tayi a sink ta fice da sauri ta fada toilet.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (27)
***Chan wajen gate ya nufa, fuskar sa a hade,ya tambayi ina driver, ya taso da sauri ya bud'e masa motar ya shiga, ya tada motar suka fice daga gidan. Jingina kansa yayi a jikin kujerar ya saka hannu zai ciro wayarsa ya tuno ya barta a daki sanda Fauwaz yake masa magana, tsaki yaja kawai ya maida kansa da yake sara masa, daga dawowar sa sai a nemi a hanashi sukuni haka kawai, ya rasa me yasa Yaya take son kure shi, idan ba haka ba har shine za'a yiwa aure irin wannan? Shi da ko tunanin rayuwar auren ma baya yi yanzu yake son settling ya fara neman yarinyar ma.
Yasmin ce ta fado masa, ya tuna sanda ta rike masa suitcase tana hawaye, wai a dole bata so ya tafi, shi dariya ma ta bashi yadda ta hakikance ita tsakani da Allah take son shi, bayan yasan irin wannan soyayyar bata existing sam. Shi be ma yadda da irin wannan ba, kamar wani wason kwaikwayo haka ya dauki abun, yawo sukayi tayi akan street din Abujan daga wannan su sauka wannan sai da ya gaji kuma ya tuna Baba zai iya dawowa ya nemi shi sannan yace su koma gida.
Baba na harabar gidan tare da wasu mutane suka shigo, zuciyar sa ce yaji ta dan ragu da zafin da take masa ganin Baba, kallon motar Baban yake har suka samu waje sukayi parking ya fito da saurin sa, ya nufi wajen su. Fuskar Baban ce ta fadada da fara'a ganin Tariq din.
"Tariq..."
"Baba barka da warhaka."
Ya russuna k'asa yace
"Ina wuni?"
"Lafiya lou bakon turai."
"Ina wuni?"
Ya gaishe da wadanda suke tare da Baban, suka amsa sai sukayi masa sallama suka tafi. Hannun sa Baba ya kama ya rike suka shiga takawa zuwa part din Yaya suna tafiya yana tambayar shi hanya da sauran abubuwan da ya kamata ya tambaya.
Tare suka shiga Tariq kamar ya kwace ya gudu dan baya son abinda zai hada shi da Yaya a wannan lokacin, so yake ma yaje yayi tunani sosai akan maganar da Fauwaz yayi masa. Hannun sa da yake cikin na Baban ya kalla kamar ya kwace ya daure dai suka shiga falon. Tana kwance tana gyangyad'i suka shigo tayi firgigit ta tashi pretending kamar ba bacci take ba
"Yaya bacci kike ne?" Baba ya tambaya
"Um um, ba bacci nake ba, kallo ma nake abina."
_"Musun me bacci."_ Tariq yace a k'asan makoshin sa
"Dunkum sabon ango ashe tare kuke."
Gimtse fuska yayi, Baba kuma yayi