Showing 33001 words to 36000 words out of 120733 words
yau take saka ran zuwa Baban, weekends yake zuwa Kano sai yayi kwana biyar a Abuja, ta gama duk abinda zatayi tunda tasan ko yazo ma sai ya gama da mutanen sa a waje sannan yake shigowa ciki, jidda tayi kulewar ta a daki yan miskilancin sun motsa sai ta kyale ta tayi nazarin abun sosai.
Yanke shawarar zuwa wajen Yaya tayi kawai ta rage zaman kadaitar, ta yafa mayafin ta ta nufi shashen Yayan, ta sameta a zaune ita da aabu suna zare ganyen zogale daga jikin sa, sa hannu tayi aka cigaba tare da ita suna hira har aka gama tas abu ta dauka ta tafi kicin ta dafa mata. Fitar abun ya saka Auntyn yin shiru tana tunanin sanarwa Yayan abinda yake faruwa da yake ya nukurkusar zuciyar ta, yanke shawarar sanar da Yayan tayi kawai dan idan abu na cin ka idan baka fada ba baka taba jin dadi.
"Yaya kin gane kawar Jidda Safeera ko?"
"Na gane ta, bikin ta yazo ne?"
"A ah, su ai yan boko ne Yaya."
"Ai sai ayi tayi dai, yaran nan jiran Alhaji nake yazo ayi wacce za'a yi, ko zasuyi karatu sai sun fara fidda miji, dazu muna maganar da jiddah dariya ma ta mayar da abun."
"Gaskiya ne yaya."
"Toh Allah,zaka bar zagada-zagadan yan mata ne a gabanka haka? Wannan ai shirme ne."
"Ita Jidda dama maganar da zan miki kenan, Yayan kawarta ta, Ismail yazo yace yana son ta."
Da sauri Yayan ta kalle ta kamar bata shirya jin hakan ba, kamar kuma ba ita ke maganar a samu miji yanzu ba
"Ita Jiddan ce tace yazo?"
" A'ah, shine dai ya sameni da maganar, shine nace bari na fara fada miki."
"Toh ita Jiddan tana son shi ne?"
"Wallahi Yaya ban sani ba, amma dai kinga yadda suka shaku da kanwar sa, kuma suna son Jiddah sosai har mahaifiyar su wallahi, shiyasa nayi mata sha'awar shi."
Shiru Yaya tayi, ta bata fuska nan da nan tayi kicin kicin, hakan ya bawa Aunty mamaki ta rasa dalilin hakan daga Yayan, kasa hakuri tayi tace
"Baki ce komai ba Yaya."
"Toh me zance? In dai tana so kuma an tabbatar da halin sa ai shikenan."
Shiru duk sukayi, ganin kamar ran Yayan ya baci sosai ya saka Auntyn tashi ta tafi, tana fita Yayan ta mike itam
"Ai ba zata sabu ba wallahi, gida be koshi ba a kai dawa, yarinya me hankalin zan bari ta kubce mana ina, bari ubansu yazo."
A fili take maganar tana tsaye, sai ga Fauwaz kamar wanda aka jeho hannun sa rike da ledar wayar Jidda da Baba ya siya musu ita da amira na gama school, sai kuma sakon snacks da Mama ta bayar a kawo ma Yayan. Tafiya yayi da dan sassarfa kamar zai rungume Yayan ta goge tana dariya
"Shakiyin banza, shakiyin wofi, rungume ni fa zakayi da ko?"
"Eh wai irin na turawa ba, irin nayi missing din nan naki."
"Allah ya shirye ka kaji, zuwan Kenan?"
"Wallahi Yaya, zuwan kenan dan Baba ma ya tsaya wani meeting ga wata gaisuwa da zasu kawai nayi gaba dan na matsu naga my heart beat."
Ya tallafe zuciyar sa, bugu ta kai masa ya zille yana kyalkyala dariya
"Zo ka zauna dama neman wanda zan fadawa damuwa ta nake sai gaka."
"Faduwa tazo daidai da zama, ga sakon ki inji Hajiya Mama, part din ki kuma ya kusa kammaluwa na daina missing dinki."
"Toh ajiye nan tukunna, an gode."
Ajiyewa yayi ya zauna, itama ta zauna tana tattaro hankalin ta waje daya kana gani kasan magana zatayi me muhimmanci
"Ya labarin Yayan ku?"
"Lafiya kalou, ya gama ai har ya fara training, kinsan wasu awowi ake so ka hada kafin ka zama babban matukin jirgi."
"Shi kuma abin da ya dame shi kenan, saboda tsabar rashin son mutane shine ya zabi bangaren da ba zai dinga zama ba kenan koyaushe yana sama kamar tsuntsu."
"Da dadi fa Yaya, babban aiki ne."
"Kai ka sani, ni ba wannan ba, zaka iya kira min shi yanzu?"
"Yanzu nasan baya kusa dan dazu muna magana ma ya kashe zai kirani."
"Toh shikenan, wai kuwa yana da budurwa ni Hajara?"
"Tab! Ba dai Ya Tariq ba, karatun ya saka a gaba idan fa ba gani yayi ya karbi cert dinsa a hannu ba, toh fa ba zai nutsu ba, yana da naci duk abinda yasa a gaba."
"Toh Masha Allah, wani tunani nayi. Zan je takanas na roka masa auren Jidda a wajen mahaifin ta."
"Jidda kuma Yaya?"
"Ita, dan Malamin da ya bashi rubutu ya fada min, idan aka basshi haka sakaka toh ko auren ma ba zai ba, haka zai kare rayuwar sa, ni kuma sai na duba kaf dangi babu me halin Jidda, ita kadai zata iya taimaka mana ta rufa mana asiri."
"Amma Yaya Jiddah fa, da Ya Tariq?"
"Menene a ciki?"
"Ba komai, amma a fara jin ta bakin ta kar ayi mata dole."
"In sha Allahu ma babu wata matsala, ina ji a raina zasuyi rayuwar aure ingantacciya."
"Toh yanzu ta yaya hakan zata kasance?"
"Ni dai kai zaka taimaka min, ka sami Jiddah da maganar naga kuna shiri sosai, ni kuma zan fadawa Baban KU."
"Toh Ya Tariq din fa?"
"Karka fada masa, irin matsalar sa ai baa fada musu sai dai kawai ayi dan aka daka ta tasu wallahi ba za'a yi ba."
"Auren dole kenan za'a masa."
"Dallah ana kaika."
"Toh ai Yaya abin ne, nasan halin ya Tariq da taurin kai, kar ya bata ma yarinya lokaci azo ba'a barta ta zabi miji da kanta ba shi kuma yazo yace ya fasa."
"Ai wallahi ina me tabbatar maka be isa ba, kai dai kawai kayi abinda nace, sauran ka bar komai a hannu na, Dijengala nake me abun mamaki "
"Toh Allah ya taimaka dije."
"Ka fadi sunan uwarka."
"Hahaha, Allah sai na fasa taimaka miki."
"Yi hakuri toh."
"Ban hakura ba, sai kince please."
"Ni zaka wulakanta dan zaka taimaka min?"
"A ah, amma sai kin bani hakuri da turanci."
"Kasan dai bana son shegen turancin nan? Kaga ana ciccize baki wai a dole ana turanci, mtswws! Aikin bur inji tusa."
"Shikenan tunda bakya son taimako na, kuma sai na fadawa Ya Tariq abinda kike shirya masa idan yaso ya hawo jirgi yazo ya sameki."
"Yazo din mana, tsoron sa nake? Karka taimaka din idan baka taimaka ba ai ubanka zai taimaka tunda shi na isa dashi."
"Calm down My heart beat, wasa fa nake miki, ai ban isa naki abinda kike so ba, yanzu zanje na fara aikin ki."
"Yawwa dan albarka, yi maza ka gama kai ma na samo maka taka ko a karkara ne."
"Wait what? Wallahi kar ma a fara dan ina da fine babe dita idan ba haka ba kuwa zan bar gari na hada kayana na tafi karkashin gada."
"Ka tafi bangon duniya ma, dan nema."
"Maimakon ki lallaba ni,o matar nan."
"Ba zan lallaba din ba, nima ba uban da ya lallaba ni da za'a auran min dunkum din kakanku."
Da sauri ya sa hannu ya toshe bakin sa saboda yadda ta bashi dariya sosai, ya mike ya fice dan idan ya biye mata ba zata gaji ba sam.
Tsohon part dinsu ya shiga, ya ciro sabuwar wayar Jidda ya bude ta, ya tura hotunan Ya Tariq masu yawan gaske sai nasu dasu Amira dan kar ta kawo komai, sannan ya kashe ta, ya maida ita kwalinta, ya nufi bangaren Auntyn.
Jidda na kwance a daki tayi rigingine taji usman na ihun ya Fauwaz, da sauri ta duro ta fito ta same shi a tsaye ya daga Usman sama yana dariya.
"Ya Fauwaz." Tace ya sauke Usman yana mata murmushi
"Jidda ce tayi kiba haka?" Yace a sigar tsokana, dariya ta saka
"Kai Ya Fauwaz yaushe ka ganni last zaka ce nayi kiba."
"Allah kuwa, idan na ganki a hanya ma ai ba zan gane ki ba."
Dariya kawai take dan tasan hadda tsokana, duk da tasan tayi mugun chanjawa sosai dan baki daya jikinta ya murje duk ramukan nan sun ciko sai wanda ba za'a rasa ba. Bangaren chest da bayanta a lokaci daya tayi su dan bata taba ma tunanin zata yi ba, girman lokaci daya yazo mata shiyasa yanzu koyaushe da Hijab dinta take yawo a cikin gidan saboda ma'aikatan da masu gadin gidan.
Ledar wayar ya mika mata ta karba tana leka ciki, tayi tsalle cike da murna,
"Sakon Baba,."
"Mungode Allah ya kara budi."
"Amin Amin, Amira ma jiya aka bata tata, number ta na ciki tace ki kirata kina kunna wayar akwai gist."
"Toh shikenan, yau ba zan iya bacci ba, kusan kwana zamuyi muna hira nasan."
"Lallai gandoki, zaku yi ku bari ne, ina Aunty ta shiga?" Ya waiga yana kallon bangaren bedroom din Auntyn
"Tana part din Baba."
"Ok, gidan shiru,kuma ku tattara ku dawo ma dinga zuwa hutu kawai."
"Aikuwa."
"Shine, dama akwai plan din Baba, amma wannan zuwan nasan har da magaanar tafiyar ma, kinga ya maida hankalin sa waje daya ya dinga zuwa ko duk after two weeks ne, yanzu kuwa yana chan hankalin sa na nan."
"Ai kamar Yaya ce bata son tafiya ko?"
"Haka zata hakura, an gama.mata part dinta ma fa."
"Lallai dole ta hakura."
"Aikam, in baki labari." Yayi kasa da murya
"Nayi new babe wallahi."
"Dan Allah, aina take?"
"A chan Abujan ne."
"Lallai, Masha Allah."
"Ki bari kawai, zuwa zan na shige daga ciki, na bar Ya Tariq tunda shi ya tsaya kure wa boko guda."
"Be gama ba har yanzu? Ya dade."
"Ya gama wani course yake, kinsan pilot ne."
"Wai, ban ma sani ba ai."
"Aiko yana chan ya kusa ma, dazu muka gama waya ma."
"Allah sarki, idan kunyi waya ka gaishe shi."
"Gaki da sabuwar wayar ki, na ma saka miki number kowa har tasa, ki kirashi kawai."
Zaro ido tayi
"Wai... Tsoron sa nake ji, ba zan iya ba wallahi."
"A ah zaki iya mana, menene abun tsoro?"
"Uh um, ka gaishe shi kawai."
"Toh shikenan, zaiji."
"Nagode."
"Bari na dubo Jamil mu gaisa, zan dawo idan aunty ta fito."
"Ok sai ka dawo."
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (18)
***Tunda suka shigo mota be kara magana ba, tsoron sa daya kar Jiddah taki shi, be san ya zai yi da rayuwar sa ba idan har tace bata son shi. Da kyar ya kaisu gida suna zuwa yayi saurin yin hanyar dakin sa, jiki a sanyaye itama Safeeran tayi nata dakin tana fatan kar a samu matsala dan ta san yadda Ya Isma'il yake son Jidda.
Tunda ya shiga dakin ya kasa zaune ya kasa tsaye,duk da ba wai tace bata son shi bane, amma kuma ai be kamata ta rikice haka ba, ya kamata ko yaya ne ta bashi amsa. Wayar sa ya dauka ya kira Farouk yace ya shigo dan Allah, nan da nan sai gashi, ya kwashe komai ya fada masa , shiru yayi yana nazari kafin yace
"Kila shock ne, kasan har yanzu fa da sauran su, kila bata taba tunanin hakan ba shiyasa tayi acting haka, give her some time, in sha Allah Khair."
"Kana ganin ba matsala, tari ne fa ya sarketa kamar zata shid'e."
"Calm down, ina ji a raina ba matsala bace gaskiya, ka bata time ka barta da Safeera suyi magana, kawarta ce tafi kowa sanin ta, hopely zata iya convincing dinta ma."
"I hope so, I'm just nervous ne, ba zaka gane ba. I don't think zan iya daukan rejection."
"Ba matsala fa, ka kwantar da hankali ka, as you come fine like this akwai wata babe da zata ki ka ne?"
"A ah fa, banda irin Jidda."
"Hadda wadda tafi Jidda ma."
"Kana dai fasa min kai ne kawai."
"Da gaske fa "
"Toh naji, bari na duba me akayi a kitchen yunwa nake ji yau ko breakfast ban ba."
"Kaji ko?"
"Bari kawai."
Yace ya fita shi kuma ya mike kafarsa yana tausayin Isma'il din idan har aka samu matsala.
***Zaman jiran Baba yayi tayi har bayan isha, sannan ya shigo a gajiye duk da haka sai da ya tsaya a wajen Yayan dan yasan tana nan tana jiran sa, a zaune kuwa ya sameta tana kallo tana dan gyang'adi, sallamar sa ta sakata wartsakewa ta mike da sauri
"Yaya baki bacci ba, Allah yasa bani na rike ki ba nasan da wuri kike kwanciya."
"Kai nake ta jira wallahi, sannu da hanya."
"Yawwa, ai da kin kwanta idan Allah ya kaimu da safe sai muyi maganar."
"Ba zan iya hakura bane ai, magana ce me muhimmanci."
"Toh, Allah yasa lafiya "
Yace yana zama a kasan carpet din,daga gefen kafarta, baya taba zama kujera da mahaifiyar sa tunda ya taso, yana bala'in so da kaunar Yaya dan baya hada duk wani abu da ya shafe ta da kowa har kuwa da yayan cikin sa, shiyasa duk abinda take so shi yake mata. Gaba daya ya tattaro hankalin sa waje daya ya kara tankwashe kafarsa, dan yasan idan ba fada masa matsalar Yaya tayi ba ko baccin kirki ba zata iya ba.
"Maganar yaran nan ce Alhaji."
"Ina jinki Yaya."
"Ajiye 'yaya mata a gaba haka be kamata ba, ba daya ba har su biyar rigis, wanda duk cikin su babu wadda akayi wa aure ba zata zauna ba, abun nan kullum dashi nake kwana nake tashi, ya zama lallai duk su fito da miji ko da za'a yi karatun dai ya zama akwai maganar aure."
"Haka ne Yaya, dama dai akwai maganar Safiyya da Umaima a k'asa."
"Ah toh Masha Allah, ai ban sani ba, sai ayi abinda ya kamata, daga su sai azo maganar na k'asan."
"Wai da suma su fara jami'ar, tunda Maryam ta fara yanzu tana ajin farko, Amira da Hauwa'u kuma zasu fara suma bana,sai a hade su, su uku idan sun kai ajiye biyu ."
"Hakan ma yayi, amma ni ina da wata alfarma da nake nema a wajenka, buri na kenan idan ka cika min burin nan ka gama min komai."
"Babu alfarma a tsakanin mu Yaya, me kike so ayi? Fada kawai zakiyi ni kuma zan cika miki da yardar Allah."
"Magaanar yaron nan ce Tariq, da yarinyar nan Jiddah."
"Na'am!"
"Na duba na dubo gaba daya dangi kaf banga wadda ta dace dashi ba, sannan na gamsu da tarbiyyar yarinyar nan dari bisa dari, ina kaunar ta har cikin raina bana so mu rasa ta, shine nake so ka kaini wajen mahaifinta na nema wa Tariq auren ta."
"Toh Yaya, duk yadda kika ce haka za'a yi, da ni da yaran nan duk ikon ki ne."
Washe baki tayi cikin tsananin jin dadi tace
"Allah yayi maka albarka,ya raba ka da duniya lafiya, ya sa yaran nan su rama maka."
"Amin Yaya."
"Yanzu yaushe zamu je?"
"Toh Yaya, ko wani satin idan Allah ya kaimu, sai muje."
"Toh shikenan, Allah ya kaimu."
"Amin ya Allah, Allah ya tabbatar mana da alkhairi."
"Amin Amin,sai da safe."
"Allah ya tashe mu lafiya."
***A daki ya samu Aunty, ta tare shi da fara'arta, ya fara watsa ruwa ya zura sabuwar jallabiyar sa sannn ya dawo falon ya zauna, abinci ta kawo masa wajen da yake zaune, yaci kad'an dan cikin sa a chushe yake, ta tattare ta kwashe ta maida kitchen sannan ta dawo ta zauna a gefen sa, zuciyar ta na azalzalarta da maganar Jiddah, kallon ta yayi yaga kamar akwai abinda zata fada masa, sai ya ajiye remote din hannun sa ya tattara hankalin sa ya bata yana fuskantar
"Ya akayi Halimatu, kamar da magana a bakin ki."
Murmushi tayi ta sauke kanta k'asa,
"Yanzu na baro wajen Yaya, tazo min da wata magana me girman gaske, duk da na amsa mata da toh dan dole a lallaba ta, amma kuma ina hasaso gaba, duk da ni kaina na dade ina hasaso dama hakan ta kasance a raina, amma na share saboda sanin halin yaran yanzu ba irin mu bane, kar kayi musu abu su ga kamar ka takura musu, shiyasa nayi hakuri na bar magaanr a raina, amma kuma sai ga Yaya tazo da maganar, kuma ga dukkan alamu idan har aka ki yi mata abinda take so za'a samu matsala."
"Toh, Allah yasa ba wani babban abu bane."
"Babba ne a wajen yaran idan har aka samu akasi, amma kuma idan suka hada kansu zan fi kowa farin ciki da wannan hadin."
Kanta ne ya kulle bata gane in da Baban ya dosa ba, ganin bata fahimta ba ya saka shi yi mata gwari-gwari.
"Yaya ce take so muje mu samu Yaya, a nemawa Tariq auren Jidda."
Wani gingirim taji kanta yayi, ta kalli Baban sannan tace
"Tariq kuma?"
"Eh."
Ranta ne ya dan sosu, har Baban ya fuskanci bata ji dadin maganar ba, duk da bata ce komai ba amma fuskar ta, ta nuna rashin jin dadinsa. Ido ya zuba mata cike da mamakin yadda ta karbi maganar, a tunanin sa zata fi kowa murna da hakan dan ko ba komai Tariq dan dakin tane, sannan be yi tunanin zata ki jinin sa ba, tunda duk tsiya ai Tariq dan sa ne, kuma idan da kara itama ai dan ta ne
"Akwai matsala ne?"
Yace mata fuskar shi na sauyawa zuwa bacin rai, girgiza masa kai tayi kawai. Sai ta mike ganin ba zata iya rike abinda take ji ba, ta fice daga dakin ya rakata da ido cikin tsananin mamaki.
Daki taje ta zauna ta rasa abinda yake mata dadi, bata taba kin Tariq ba, ba kuma zata taba kin sa ba, amma Mama fa? Ya rayuwar Jidda zata zama a auren wadda mahaifiyar sa bata so ko kaunar ta? Har ga Allah tafi wa Jidda sha'awar Isma'il, tunda shi da mahaifiyar sa duk suna san jidda, zata fi samun nutsuwa dasu dan zasu tallafi rayuwar ta, sannan zata samu uwa da zata dubi lamuran ta.
Safa da marwa ta dinga yi a tsakanin dakin ta, shiyasa Yaya dazu ta bata rai kenan akan maganar, shine tayi saurin fadawa Baban, da tasan hakan ne zai faru da bata yi mistake din fara sanarwa Yayan ba, dama ance ciki ba dan abinci kawai aka yi shi ba, da ta sani ta rike sirrin su ya zama tsakanin ta ne kawai da Jiddan har zuwa sanda zasu fahimci juna daga nan duk abinda za'a yi sai ayi. Yanzu ya zatayi? Zata cewa Baba a ah ne bayan abinda yayi wa Jiddan da bashi da maraba da abinda yayi wa Yayan cikin sa, ko zasu ki dansa Tariq ne bayan shi be kyamace su ba. Ko kuwa Baffan Jidda zai hana dan Baba auren Jidda ne? Bata da mafita, mafita daya ce idan har jidda taki, amma kuma tayaya ma Jidda zata ki? Baba ko Yaya