Showing 24001 words to 27000 words out of 120733 words

Chapter 9 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

45451

abinda ya sakashi chanja mind dinsa haka,

"Ka kyauta sosai."

"Nagode Daddy."

Sai suka jera zuwa cikin gidan a tare tamkar wasu abokai.

***Tun daga ranar kullum shi yake kai Safeera school Malam Sa'idu ya dauko ta, kuma kullum sai ya labe yaga zuwan su Jiddah. Be taba bari sun ganshi ba, a hakan ya sha daukar ta a hoto dan a yanzu hotunan ta da yake dasu a wayar sa ba zasu kirgu ba, duk da yayi ma kansa alkawarin sai sun shiga ss3 sannan zai mata maganar a time din yana da yakinin zata karbe shi, hannu biyu su fara soyayyar su wadda ya tanadar mata da zazzafar soyayya.
Duk sanda yake free idan a daidai lokacin short break dinsu ne sai ya siyo abubuwa ya kai ma Safeeran school yace ita da jiddah, duk da ko be fada ba ma taren zasu ci amma sai ya sake jaddadawa har Safeera ta fara suspecting dinsa, he care so much akan jiddah har ya fita ma, duk sanda suka zauna a gida sai yayi mata maganar Jidda, me tayi a school yau, me tace hirar su kenan duk sanda suka zauna ko zai koya mata assignment.
Bangaren Jiddah kuwa sosai take picking karatun fiye da yadda kowa yayi tunani, duk da kusan kaso hamsin cikin dari Safeera ce dan kaf class din babu me kokarin Safeera shiyasa kawancen su ya taimakawa jidda sosai ta fanni daban -daban, hatta yanayin yadda take magana da yanayin shigar ta Safeera take kwaikwayo, shiyasa cikin kankanin lokaci ta washe a cikin class din har take iya tsayawa a tsakanin yan class din tana jin itama daidai take dasu. Abubuwa da yawa tare Mom din Safeera take siya musu na gyara da gayu,tun tana jin kunyar karba har ta dawo bata jin komai.
Wani weekend tace ma aunty zata je gidan, bata hanata ba sai dai dole ta rakata har gidan ita da Usman, anan suka gaisa da Maman Safeera sannan ta bar Jiddan, suka ce zasu kawota. Murna wajen Safeera ba'a magana, da farko ganin irin gidan ya saka jikin jiddan sanyi amma kuma yanayin yadda aka karbeta ya saka ta sakin jiki dan hatta masu aikin gidan sun san labarin Jidda a bakin Safeera da Isma'il, ita kanta mom kamar zata goya ta dan murnar ganin ta, labari ya kare yau dai taga Jiddan da Safeera take bala'in so kuma kwarai ta yaba da nutsuwar ta shiyasa taji dadi da ya kasance irin kawayen da yarta take mu'amula dasu.
Kamar wanda aka jeho haka Ya Isma'il ya shigo gidan,waya suke da Mom tace masa Jidda tazo ai ba shiri yayi sallama da su Farouk ya taho gida yana Allah Allah ya iso bata tafi ba. A dakin Safeera ya iske su, ya tsaya daga bakin kofa yana yin kasa da idanun sa sanda suka hada ido da Jidda a lokacin da take kyalkyala dariya, dariyar da ta saka bugun zuciyar sa tsaya chak na dan wasu dakiku.

"Ya Isma'il." Safeera tace tana mikewa daga kan gadon

"Look who's here."

"Jidda." Ya kira sunan ta kamar wani dolo

"Na'am, ina wuni?"

"Lafiya lou, ashe zaki zo da gaske."

"Umm.." Tace tana wasa da hannun ta, hannun ya kalla yaga yatsun ta zara-zara, juyawa yayi da sauri ya bar kofar, Safeera ta dawo ciki suka cigaba da hirar su, daga nan suka dauko books din Safeeran sukayi karatu, wajajen karfe biyar Mom tace Ismail suje su kai ta, kafin ma ta rufe baki ya mike cike da zumudi, kallon sa tayi, ya dauki car key din motar ta, ya ajiye nasa sannan yace

"Bari na jira su a mota." Yayi gaba yana kada key din motar, tashi Mom tayi taje dakin ta, ta hadowa jiddah sha tara ta arziki tun daga kan underwears zuwa turare da kayan kwalliya, sai atamfa da veil, sannan ta saka mata 5k a cikin envelope ta fito ta iske su a dakin Safeeran tace su taso, turo baki Safeera tayi cikin shagwaba ya hau bubbuga kafarta kamar zatayi kuka

"Dan Allah Mom ki bari sai anjima 😭."

"A ah kar dare yayi, ni nayi ma Maman ta alkawarin zaa kawota, gwara ido na ganin ido ko Jidda? Kar babanku ya dawo yayi fada."

"Eh." Jidda tace tana yafa dan madaidacin veil dinta

"Allah ni...." Ta cigaba da buga kafarta, dariya kawai Mom tayi ta mikawa jidda kayan ta russuna har kasa ta sa hannu ta karba tayi godiya

"Kuje yayanku yana mota yana jiranku, sai yaushe Jidda?"

"Wataran." Tace tana murmushi

"Kice ma ba zaki sake zuwa ba." Safeera ta fada tana hararar ta

"Sorry mana."

Tace tana kallon ta, shiru tayi dan taji haushin tafiyar da jiddan zatayi, ta bude wardrobe dinta ta dauko veil ta dora akan inner cap din dake kanta ta zura slippers suka fito hannun ta rike da ledar kayan da Mom ta bawa jiddan.
Yana zaune a mota ya hango sun fito, ya cire lock din motar ya fita ya budewa Jidda baya ta side din driver, ita kuma Safeera ta shiga gaba, ta sama Mom ta hango duk abinda ya faru, ta girgiza kai kawai tayi murmushi dan dama tana suspecting Isma'il din son yarinyar yake, sai dai bata tabbatar ba sai yanzu da taga abinda ya faru, sakin curtains din tayi bayan sun fice daga gidan.
A hankali sosai ya shiga driving din kamar baya tafiya ma, sanyi da wakar da ke tashi motar ta saka duk basu lura da yadda yake tukin ba, maimakon ya wuce gidan su Jiddan kai tsaye sai ya tsaya dasu sahaibco stores ya siya musu chocolates masu yawa da ice-cream sannan suka cigaba da tafiyar wahainiya har suka iso ba dan ya so ba, yayi parking suka fita tare da Safeera ta rakata har cikin gidan sannan ta dawo suka tafi gida.

***A harabar gidan sukayi kicibis da Mama, tana fitowa daga part din Yaya wanda tun sanda tazo gidan be fi sau biyu taga Maman a bangaren Yaya ba, kallon ta Maman take dan ta kwana biyu bata ganta ba, sai taga tayi shar da ita ta kara wayewa tamkar ba ita ba, durkusawa tayi a tsorace ta gaida Maman, ta amsa kamar taga kashi ta wuce ta bata sake ko kallon ta ba. Bata ji komai ba dan dama ba wai suna haduwa bane tunda ba zuwa wajen ta take ba, haka kuma ko a compound din gidan basu cika haduwa ba dan idan Mama na gida ko yaushe tana part dinta itama kuma Jiddan ba yawo take ba wajen Yaaya kawai take zuwa shima ta dayar hanyar take bi taje ta dawo. Ita har ga Allah tsoron Maman take dan ba karamin kwarjini take mata ba musamman da taga hatta Aunty ma shakkar ta take shiyasa ta shafawa kanta lafiya bata taba shiga part din ta ba ko da wasa duk nacin su Amira sun gaji sun hakura dan ita bata cika son shishigi a in da ba'a son ta ba.
Rayuwar ta, ta chanja a dan lokacin nan babu abinda zata ce sai godiyar Allah dan ko a haka Allah ya barta ta gode dan bata yi tunani ko hasashen ta a irin wannan rayuwar ba, rayuwar ta ta baya ta tuna ta girgiza kanta ta furta alhamdulillah, daga haka ta wuce wajensu ta samu Aunty tana bude kayan da Mom din Safeera ta bata cike da yabawa dan ba karamin kaya tabata ba masu kyau kuma da tsada, ita kanta Auntyn tayi mamakin gidan su Safeeran dan yadda suke babu girman kai ba zaka taba zaton haka gidan su yake ba

"Bafa karamin kaya matar nan ta baki ba jidda, ko wannan atamfar Babba ce wallahi."

"Taki ce ai atamfar Aunty."

"Tawa?" Ta waro ido tana daga

"Eh cewa tayi na kawo miki."

"Kai, kai hadda ni kuma?"

"Eh."

"Kai amma naji kunya, Nagode zan kirata dama in sha Allah nayi mata godiya, hade kayan ki kai daki."

Toh tace ta tattare kayan ta kai daki sannan ta dawo suka zauna da Auntyn suka cigaba da hira. Daga nan ta kira musu Baffa suka gaisa sannan suka tashi don yin sallar magriba da aka soma kira a wasu masallatan.


***Kwanan sa hudu yana avoiding yarinyar, ta shiga rayuwar sa sosai komai yake ko ina yake sai ta bishi, gashi shi mutum ne da baya son a shiga rayuwar sa idan har ba shine ya gayyato mutum ba. Nacin ta shi yafi komai damun sa gashi sam bata da zuciya duk yadda ya kai da nuna mata baya son yadda take bin sa amma bata ganewa, shi ko sunan ta be sani ba sai ranar da ta fada masa da kanta, daga ranar be kuma sake tuna sunan nata ba ya manta. Zaman sa ya cigaba da yi a daki duk da yana da lectures amma baya son ya fita su hadu shiyasa ya hakura ya zauna yana bin lecture din online yana following komai, baya so ko kadan ya dauke idanun sa daga kan system din baki daya ya tattara hankalin sa waje daya yana yi yana jotting down key words din. Door bell dinsa ce tayi kara alamun yana da bako, ya daga kai ya kalli agogon dake makale a saman table din nasa, be san wanda zai kawo masa ziyara a irin wannan lokacin ba, duk da yasan bazai wuce Ishaq ko xuo kaiy ba, amma kuma ya san suna class a wannan lokacin kuma babu abinda zai fito dasu, sake kad'a bell din akayi, ya tashi yana jan siririn tsaki, ya shiga takawa kafarsa sanye da white socks zuwa kofar dake gaban dan corridor kafin main cikin gidan. Budewa yayi ya kalleta cike da mamakin ganin ta, basket ne a hannun ta me kyau, ta sakar masa murmushi ya dan saki fuskar sa kadan yana tsaye still akan kofar

"Zan iya shigowa?" Tace tana kallon cikin gidan, da sauri ya girgiza mata kai

"Ba zan iya ba?"

"Eh." Yace kai tsaye, dan jim tayi a tsaye, shima ya cigaba da tsayawa a wajen sai tayi murmushi ta mika masa basket din

"Lunch nayi maka naga baka fita school ba"

Sai ta mika masa ya miko hannun sa ya zai karba hannun su ya hadu da na juna, da sauri ya janye yana bata fuska saura kadan basket din ya fadi abinda yayi matukar bata mamaki.

"Shikenan?" Yace yana rike da basket din a kaikaice, kasa magana tayi dan tsabar takaici, ta daga masa kai alamar eh

"Ok, thank you."

Yace ya juya rike da basket din, ya tura kofar sa ya barta a tsaye a wajen kamar wadda aka dasa saboda tsabar mamakin sa. Kusan minti biyar ta dauka a tsaye a wajen ta gaza aiwatar da komai, kafin daga bisani cikin yanayi na bacin rai ta bar wajen fuuuu.

A gaban kofar ya dire basket din, yai gaba abinda ko budewa be yi ba bare yaga abinda yake cika.


[03/10, 21:28] Mamuh: _ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
[05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*


*ZAFAFA BIYAR BACTH A*


1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350
*(Bilyn Abdul)*


2.. _KAI MIN HALACCI_ 350
*(Miss xoxo)*


3.. _BURI DAYA_ 350
*(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350
*(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350
*(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*


1... _DAURIN GORO_ 350
*(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350
*(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350
*(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350
*(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350
*(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350
*(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350
*(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350
*(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350
*(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350
*(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350
*(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*


_Duk biyar 1500_

*______________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_
*(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_
*(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_
*(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_
*(Mamu gee)*

5... _BABU SO_
*(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_
*HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_
*_2270637070_*



_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*



*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_*
[11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (15)

***Shiru yayi bayan ya ajiye wayar, mamakin sa na karuwa idan ya tuna yanayin yarinyar, tsaki yaja ya mike ya rasa dalilin da yasa shi damuwa da al'amarin ta har haka, ya kuma rasa dalilin da duk lokacin da ya ganta sai ya ji duk maganar dake dauke akan harshen sa ta dauke. Tsaki ya sake ja a karo na biyu yana dan murza saman goshin sa. Tunawa yayi da abinda yake kafin shigowar wayar, kashe datar sa yayi dan kar a sake damun sa ya cigaba da duba takardun sa har zuwa lokacin da yaji ya gaji sosai sannan ya hakura. ID card dinsa ya dauka da wayar hannun sa ya fito, ya bi ta wajen office din masu apartment dinsu da suke zama kullum Monday to Friday, jinin su ya hadu da ogan dan sosai yake son shi suna ganin shi suke fara murna shiyasa yake yawan tsayawa idan zai fita su gaisa. Ogan ne yau shi kadai a office din yana duba sabbin washing machines din da za'a kawo. Daga jikin kofar ya dan yi knocking, ya taso da sauri

"Hello James."

"Hello Tariq, please come in." Yace yana nuna masa ciki

"No thank you, just want to check on you, i'm on my way."

"Ohh, not bad."

"I'll see you later."

"Ok Tariq, i sent you an email, see ya."

"Ok , bye."

Wayar sa ya bude ya shiga mail dinsa, sai yaga wai ashe gift card ne me dauke da £80 suka bashi a matsayin lucky winner na duk yan gidan da suke bayarwa duk karshen wata, murmushi yayi kawai ya maida masa reply da

"Thank you, I hope it's not cheating."

Dariya James yayi dan da gaske cheating din ne, wata baturiya ce taci dan shi Tariq ko participating be yi ba amma ya bashi, reply yayi masa

"It's cheating bro. Lol😅"

Murmushi Tariq din ya sake yi kawai, ya maida wayar yana kara sauri akan tafiyar da yake a dah.
A dan garden din cikin school din ya hangi Yasmin suna zaune da wani dan kasar ghana, so close kamar zasu shiga jikin juna, tabe baki yayi yazo zai wuce su ta tashi da sauri tana kiran sa

"Tariq please ka tsaya."

Dan rage tafiyar yayi har ta daidaita dashi, yaki kallon ta suka cigaba da jerawa har zuwa cikin building din, I'd card dinsa ya ciro yasa a kofar itama tasa nata suka shiga still be kalle ta ba suna dai tafiya a tare, sai da yazo in da yake son kaiwa sannan ya ja ya tsaya yana mata kallon me faru?

"Please magana nake so muyi."

"Ina jinki."

Yayi folding hannun sa a kirji ya jingina da bangon wajen

"I want us to be friends, pleaseeee."

"Kin taba ganin friendship mace da namiji?" Yace yana kallon ta

"Na'am?"

"Yes, kin taba gani?"

"Sosai, ina da friends both maza da mata, and I see nothing wrong with it."

"Ok, ni I'm exceptionally different, bana friendship da other gender, it's haram in Islam, sorry."

Yayi gaba abin sa ya barta a tsaye cike da takaicin wulakancin sa, juyawa tayi taga babu kowa a wajen sai su biyu, ta yi saurin barin wajen tana jin kamar ta kwala ihu, bata taba ganin dan rainin hankali irinsa ba, but ba zatayi given up ba zata cigaba da gwada sa'ar ta.


***Kanwar Yaya ce wadda ake kira da Gwaggo tazo dan taya Yayan murnar Baba ta kuma yi kwana biyu, halin su daya sak da ita da Yayan wajen surutun su, sai dai ita tafi Yaya sauki wajen fada dan Yaya akwai masifa bata ragawa kowa duk girman ka sai dai idan baka tabo ta ba. Kwanan su Mama biyar suka dawo suka bar Baba achan, a ranar kaf yan uwan Mama suka zo taya ta murna, tamkar ana shagalin biki haka aka taru Yan uwan da abokan arziki aka ci aka sha. Aunty da jidda suna bangaren Yaya anan suke nasu zaman su isu dan basu da hurmin shigarwa Maman abu. Amira ce ta kawo abinci a yar madaidaciyar kula inji Aunty Mimi tace a kawo ma Auntyn, sai kuma na Yaya shima daban.

"Zo muje part dinmu, su salma sunzo duk muna dakin mu."

Amira tace wa Jidda, kallon Aunty jidda tayi alamun taje? Ta daga mata kai dan ba zata iya hanata ba dan ita tun dama chan bata taba hanata zuwa ba ita dai Jiddan ce bata so,. Tashi tayi ba ason ranta ba dan dai kawai kar Amiran taji babu dadi ne shiyasa. Ta bita suka shiga part din nasu. Duk suna zazzaune a falon an baje ana ta hira suka shigo sai duk suka bi Jiddan da kallo, aunty Mimi ce tace

"Amira kawarki ce tazo?"

"A ah Jidda ce fa, ta gidan nan."

"Ku wuce malama."

Mama tace tana bata rai,

"Wacece?" Suka tambayi Maman bayan su jiddan sun wuce ciki

"Yarinyar chan ce ta dauko ta, yar brother dinta ce daga kauye."

"Inyee samun waje tusar asuba."

Aunty Nafi tace tana rike haba

"Tubarkallah Masha Allah, me kyau da ita wallahi."

Aunty Mimi tace tana kokarin dauke maganar Nafin

"Ai ke Mimi bansan wacce irin zuciya ce dake ba, har wani kod'a kyawunta kike a gaban Yaya."

"Toh laifi ne Ya Nafy? Ni fa ban ga abin tada hankali ba anan, beside har yanzu fa Ya Aisha ce a sama wajen his excellency, ko wannan kadai ya isa ai mutum ya hakura, wasu in sun yi auren ai wulakanta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login