Showing 12001 words to 15000 words out of 219361 words

Chapter 5 - AJIYA A DUHU COMPLETE HAUSA NOVEL

13 Jul 2025

5196

 Okay bari na barki. Amma Please anjima na kira to? . Da sauri ta ce,  Uhm-uhmm .
? ??  Why? .
Ya tambaya kamar zai yi mata kuka. Banza ta masa. Dan ta matu?ar gajiya da shi. Sake haWa ido da sukai da Ammie ya sata yanke wayar tama kasheta gaba Waya tana wani sake tsuke fuska. Shifa wannan mutumin ta kula sai ta masa fatattakar karan mahaukaciya zai ?yale rayuwarta ta huta shima yaje ya hutama ransa. Bai san yanda tai matu?ar tsanar maza bane a duniyarta ta yanzu daya kama kansa tuni. Amma ba komai, tunda yanzu tabar garinsu tana da damar da zata buga masa warning na ?arshen ?arshe da kakkaSesa daga jikinta gaba Waya, yama barta taji da matsalar gabanta...
? ??  Tunanin mi kuma kika tafi? .
? Ammie tai maganar tana taSata. Ajiyar zuciya ta sauke da Wan laSe lips Winta tana kaiwa zaune kusa da Ammien. Kwantar da kanta tayi a kafaWarta tare da rungumota. Cikin son kauda wancan yanayin ta ce,  Ammie yau tare da ke zanyi barci nayi kewarki .
? ? ? ? Murmushi Ammie tai da kai hannu ta shafa ?ya?y?yawar fuskarta.  Nima nayi kewarki Auta. Amma babu yanda zanyi tunda wataran ma inaji ina gani gidan miji zaki wuce ki barni .
? ? ? Tsam ta mi?e batare data ce komai ba ta Wauki wayarta ta fice. Da kallo kawai Ammie ta bita. Wani irin tausayinta da ?aunarta na sake ratsa mata zuciya. Mi?ewar tai itama ta fito. A kitchen ta samesu su dukansu har Manaal Win. Ta Wan duba abinda suke dafawar ta fita ta barsu. Yanzun ma a tare sukaci abincin daren bayan sun kammala. Suna tsaka da ci sai ga Yazeed ya shigo sashen. Duk gaisheshi sukai bayan shima ya gaida Ammie, yayinda Maanal tai kamar bata gansa ba tanata wasa da spoon a cikin abincin. Shiko hankalinsa duk yana kanta, duk da dai magana suke da Ammie wadda su Maanal Win basa jin mi yake faWa mata. Bai wani jima ba yay musu sai da safe ya fita. Wata ?ar ajiyar zuciya Maanal ta sauke a hankali. Babu wanda yay mata magana sai ma Ammie data shiga musu bayanin da Yazeed Win ya mata. Ashe zasuje Zaria ne gobe idan ALLAH ya kaimu ita da shi halartar wani Waurin auren ?ar abokin maigidan. Sunyi addu'ar ALLAH ya sanya alkairi su duka. Sai kuma ta Wora da faWin Maanal Win ta shirya sai ta mata rakkiya ita da Amrah dan shi Yazeed Win zai rigasu tafiya ne da abokinsa. ?ata fuska tayi zatai magana Ammie tai mata da??uwa.  Sai fa kinje daddawar gida da bata son fita .
? ? ??  Nifa Ammie ba cewa zan bazanje ba. Amma gyaran jikina fa? .
? ?  Ki tashi da wuri ayo miki, tunda sai sha biyu ma zamu wuce in sha ALLAHU  .
?? Badan taso ba dai ta amsa da to, dan taji Yazeed shima zai je. Sai dai sau?inta tafiyan nasu ba Waya bane...

? ?? Kamar yanda ta faWa a Wakin Ammie tai kwanciyarta manne da ita kamar za'a ?wace mata ita ko wata ?ar goye can. Dan da Ammien ta tashi sallar dare ma da ?yar ta Sangare ta a jikinta. Bata kuma jima da fara sallar ba itama Maanal Win ta tashi tayo alwala. Haka take itama akwai yawan ibada kamar Ammien, dan ko sanda take tashen rashin jinta dama Maanal akwai son addini, tun bata kai girma ba zatace zatai azumin litinin da Alhamis, ko an hanata kuma sai tayi sai dai ta kaisa a galabaice. Kusan ?arfe uku da rabi barci ya fara rinjayar idonta, addu'a tayi ta koma saman gadon ta kwanta tabar Ammie anan.....

? ? ? Koda suka idar da sallar asubahi ma sake hayewa gadon tayi tai kwanciyarta, dan barcine sosai a idonta, sai kuma jikinta dake mata kamar babu daWi. Da ?yar Ammie ta tasheta wajen ?arfe takwas akan ta tashi ta shirya taje gyaran jikin nan, idan ba hakaba sai dai ta bari sai gobe idan ALLAH ya kaimu dan babu fashi da ita za'aje Zaria. Dole ta tashi badan taso ba ta kimtsa. A falo ta samu ?an uwanta suna hira da karyawa, saboda saurin da take gaishesu kawai tayi ta haWa shayi a wani gora mai ?yau na ?an gayu ta wuce tana faWa musu saita dawo.
? ? Tsokanarta suka shiga yi akan ko gayyata ma babu. Ta fice tana faWa musu susha zamansu baza'a cinyema Ammie kuWin account Winta ba. Idan kuma suna da kuWi su taho. Babu kowa a harabar gidan sai masu gadi su biyu da mai bayin fulawoyi daketa yi, da alama sauran ma'aikatan duk sun kammala nasu aiki sun wuce. Dan dama mai sharan tsakar gida ne da mai wanki. Kamar yanda ta saba cikin girmamawa ta gaidasu, suka amsa mata da kulawa da tambayarta gajiyar tafiya. Koda ta fito tana kallon titin da fatan samun napep da wuri dan gidan nasu a bakin titi yake sai kawai idonta akan Yaya Yazeed dake tsaye jikin motarsa yana waya, sai dai shima idonsa a kanta. Sai da gabanta ya faWi, amma sai ta dake tana ambaton sunan ALLAH. Tafiya ta farayi a ?afa tana mai fatan zuwan napep yanzu, sai dai ko taku goma batai ba taji horn a bayanta. Sosai ta rumtse idanunta tare da cije lips, sai kuma ta sake Waga ?afa zata cigaba da tafiyarta ya Wan sha gabanta da motar tare da sauke glass Win. Cikin gizagonsa da tsare gida ya furta,  Wai nikam yaushe raini yay ?arfi tsakanina da ke haka Maanal? .
? ? ? ? Fuska ta Wan sake tsukewa da juyowa ta kallesa.  Toni Yaya minai maka na raini? .
? ? ? Cikin tsareta da kaifafan idanunsa ya ce,  Oh bama ki sani ba ko? Zan gyara miki zama ne. Ina zaki je da wannan safiyan haka? .
? ? (Kama gyaran tsaiwa ba zama ba) ta faWa a ziciyarta. A fili kam sai ta amsa masa da,  Nan zanje kusa wankin kai .
? ? ? ??  Okay, bismillah shigo na ajiyeki .
? ? Baki ta buWe zatai magana ya harareta. Dole ta shiga hankalinta dan tasan halinsa shi baya son wargi. Zagayawa tai ta Wayan side Win da har ya buWe mata, haka ta shiga tana ?un?uni cikin ranta. Jan motar yay suka cigaba da tafiya yana wani shegen tu?i a hankali kamar baya so, zatai magana wayarsa ta shiga ?ara alamar kira. ?aga wayar yay ya saka a hansfree tare da yin sallama. Daga can aka amsa masa da faWin,  Oga kayi ha?uri ka jini shiru jiya da nace zan kira .
? ? ? ? Amsa masa yay da,  Eh ai harna sha?a ma. Dan yanzu kamar ma bazan Waga kiranka ba dai na daure na Waga Win. Kasan ni bana son wasa da abu mai muhimmanci Hashim .
? ?  Na sani oga kayi ha?uri. Wlhy ina gaya maka sai kusan 2 na samu ganawa da AA Win. Shima mintuna ashirin ya yarda zai ganni da ?yar da taimakon yaron nan nasa da nake gaya maka cousen Wina ne .
? ? ? ??  Mtsoww! Mutumin nan fa na lura Wan wula?anci ne Hashim. Kodan yaga muna bu?atar kayan nan yake ta garamu haka ne? Shi ana tattalin customers shi yana yan?wana mutane .
? ??  Tom oga sai dai ha?uri, sai dai kuma ni yanda na fahimcesa kamar ba wula?anci bane ba. Yariga da yayi ?arfine sosai. Dan wlhy manyan ?asashen Larabawa nan yake huWWa dasu sosai. Kai harma turawan tako'ina kayansu shiga sukeyi. Gashi abin mamaki yaro ne ?arami dan indai bakuyi shekaru dai-dai ba to kai zakama iya girmarsa wlhy. Amma yana da wayo da ban mamaki. Yanzu dai na ta?aice maka batu ya bamu damar haWuwar da shi a cikin Companyn *_MAWAAD_* Win. Ya kuma tabbatar min da in dai mukabi ?a'idar komai daya dace zamu dinga samun kayan nasu fiyema da yanda muke bu?ata .
? ?? Ajiyar zuciya ya sauke mai ?arfi da faWin,  Alhamdulillahi Hashim naji daWin wannan labari. Kaga an gama da wannan matsalar kenan. Nasan Daddy ma zaiji daWi sosai abu kusan shekara munata fama .
? ? ? ? ??  Wlhy kuwa oga ai dole ai farin ciki. Yanzu dai na tura maka komai ta email sai ka duba .
? ?  Okay ba damuwa zamuyi magana . Daga haka ya yanke kiran tare da juyowa yana kallon Maanal da duk ke sauraren wayar tasu amma a zahiri hankalinta nakan wayarta tana duba sa?on da RK ya tura mata.
? ? ? ??  Madam! .
? ?? Ya faWa a hankali cikin katseta. Jitai kamar ya dakar mata zuciya da guduma. Amma sai ta daure ta amsa da faWin,  Kai yaya minene kuma wata Madam? .
? ?? ?an dubanta yay yana murmushi mai ?ayatarwa, sai kuma ya maida hankalinsa ga titin yana faWin,  Ai Madam Win ce. Kwana nawa ya rage kuma Manaal. Ke yanzu a yanda muken nan bakiji inama ace mu Win ma'aurata bane? .........
'?



('ZAFAFAN DAI ('

1 ?ALBIM (Mamu gee)
2 ?IRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)


Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000

0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

?an NIGER 1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu =?-?=?O?_*
*_Typing=???_*








*_=؞?AJIYA A DUHU....=؞?_*




*_Bilyn Abdull ce >??

*_(P3REP 'DDQNGP 'D1QN-RENpFP 'D1QN-PJE_*
_Da sinan Allah, Mai rahama, Mai jin ?ai._

*_My TikTok account =?G?_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram=?G?
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30


_Duk wanda bai fallowing Wina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama=??=??



______________

Assalamu alaikum
Ina Neman mutane 20 dazasuyi register da company 52u a karkashin link Dina akan $21 wato 35k a kudin mu na Nigeria account din zaibude a cikin 5-6 weeks idan account din yabude nikuma nayi alkawarin zanbiya mutum 20 dinnan salary 10k kowani mutum na tsawon wata 5 kunga riba biyu kenan kuka samu ga ribar kudin ku yadawo harda riba ga account din kun na 52u zanbude a wata na shida sai kudin ga kwasa duk kudin ku duk wata =؃?
https://chat.whatsapp.com/K0ECLn6O3WS1fnfCggOeu5

08083531881

______________

.......Shirun da tai na kusan minti biyu batare data amsashi ba ya sashi Wan kallonta. Kanta tai saurin kaudawa tana mai ?o?arin haWiye Wacin daya mamayeta. Shima sai ya Wauke kansa bai sake magana ba. Babu jimawa suka iso gaban gidan da take zuwa gyaran jikin, wanda yasani ne tuni saboda yanda take ma'abociyar zuwa gidan kusan duk ?arshen wata. Jikinta har tsuma yake nason ta fita a motar, dan bata so ya sake mata wata magana amma sai taji motar a Same alamar ya saka luck. Dole ta Wan dakata tana rumtse idanunta. Sai kuma ta juyo ta dubesa, ganin shima ita yake kallo ta maida kan ta du?ar. Murmushin ya sake saki kaWan da Wauke idanunsa a kanta cikin son basar da yanayin ke bashi a jikinsa.  Ki tayani murna? .
? ? Batare data sake kallonsa ba ciki-ciki ta ce,  Tami? .
? ? ? ?  Akan albishir Win da akai min yanzu a waya. Mutumin nan kusan shekara guda kenan muna son haWa Bussines dashi amma ko ganinsa ya gagara a gareni. Amma yau kinji har zan samu ganinsa, nasan Daddy zaiji daWi akan hakan shima matu?a .
?? Karo na farko tai Wan murmushi. Sai kuma ta ce,  ALLAH ya tabbatar da alkairi a haWuwar taku to .
? ? ??  Amin ya rabbi dear. Ammafa nasha wahala sosai. Mutumin ya riga yayi nisa ne matu?a saboda yanda yake huWWa da manyan mutane na wajen ?asar nan dama cikin gida Nigeria. Nasan dai bazaki rasa jin Mawaad ba .
? ? ? ? ? ?  Ina dai ganin sunan Companyn a jikin buhunan shinkafa, ban sani ba ko sune ko kuma da banbanci .
? ??  Yes sune. Dan yana harkar noma yanzu matu?a a ?asar nan. Kuma Kinga wannan harkar ma bai wani jima da farata ba. Amma da yake ALLAH ALLAH ne cikin ?an?anin lokaci nan ma yayi zarra.
? ? ? ??  ALLAH sarki . Kawai Maanal tace dan bataga ma'anar bata wannan labari ba ita kam da dam bata da ala?a da shi. Cikin marairaicewa ta ce,  Yaya bara naje kada na makara Ammie tace zamu rakata anguwa .
? ?? Amsa mata yay da  Okay bari na barki ki wuce. Inata baki labarin abinda bai shafeki ba, haka nake bu?atar rayuwata Manaal, wato iyalinna su dinga sanin komaina dan su kasance masu min addu'a. Dan haka sai ki shirya, dan zaki dinga raba farinciki da mijinki hakama akasinsa idan ya gitta ya ?are maganar yana mi?a mata atm card Winsa. Kanta ta girgiza masa da sauri.  A'a yaya ga Ammie ta bani nata zanyi amfani da shi. Hararta ya Wan yi da zare atm Win Ammien ya ajiye mata nasa a cinyarta.  Kiyi amfani da na mijinki, dan nike da hakkin hakan ba Ammie ba. Idan kin kammala ki kirani dan ba nisa zanyi ba .
? ?? Yanda ya tsatstsareta da ido yasa ta kasa magana. Dole ta buWe motar ta fita dan shi in baiso wasa ba dole kaji shakkarsa. Bai bar wajen ba har saida yaga ta shige. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali da jingina jikinsa da kujera yana mai lumshe idanunsa. Ya jima a hakan dan yaci kusan mintuna biyar kafin ya tada motar yabar wajen yana mai danne abinda ke tsikarar zuciyarsa game da ita.....

? ? ? &&&

? ? Yanda Maanal ta samu tarba a ciki zai tabbatar maka akwai sha?uwa da sanayya sosai tsakaninta da mai gyaran. Dan duk miskilancintan nan sai murmushi take da Wan maidama mai gyaran hiranta dan tana mata tambaya ne akan Jos. Basu wani jima ba aka fara gyaran saboda tun jiya ta sanar mata. Kafin tazo ta haWa komai. Gyara sosai jikinta ya sha. Ga turarruka kamar wata amarya. Hatta kanta da ?afafunta zuwa farce an musu ?al. Haka Maanal take akwai son gyara jiki, ?ar gayuce sosai da son kwalliya, sai dai yanzu yanayi yasata Sarar da kwalliyar gefe gyaran jikinta da tsafta ne dai tana nan da abinta akoda yaushe. Sun gama a ?urarren lokaci, dan har Ammie na kiranta a waya ma. A gurguje ta bata ta cire kuWin aikinta tare da amso kayan ?amshin data haWa mata suka fito zata mata rakkiya. Turus taja ta tsaya da ganin motar Yaya Yazeed a ?ofar gidan, kafin ma ta samu abin faWa ya buWe mata gefensa alamar ta shigo. Ganin fuskarsa babu wasa sam yasa batai magana ba ta shiga kawai. Sallama sukai da mai gyaran bayan ta gaida shi ya amsa mata ciki-ciki yaja motar suka wuce. Shiru motar har sun Wan yi nisa a tafiyar cikin ?arfin hali ta ce,  Yaya dama baka wuceba ne? .
? ? ??  Mi kika gani? .
?? Ya faWa cikin wata irin kasalliyar murya data bata mamaki. Gashi ya?i kallonta sam a yanzu. Itama sai kawai ta ce,  Ba komai .
? ? ? Bai sake magana ba, itama tai shiru har suka iso gida. Sai da ya gama parking ta mi?a masa atm Win tana godiya. Kansa kawai ya Waga mata batare daya kalleta ba ko tankawa yanzu ma. Itama sai kawai ta buWe motar tai ficewarta. Da Hajiya Yaya dake daga can ?ofar sashensu da wata ba?uwa suka haWa ido, ganin irin kallon da suke mata yasa duk ta tsargu, amma sai ta dake ta nufesu badan taso ba, sai dan mahaifiyarta ta mata tarbiyya na girmama duk wanda ke gaba da ita. Sannan kodan Yaya Yazeed dake iya ?o?arin sa na girmama Ammie zata iya shanye komai daga mahaifiyarsa itama.
? ? ?  Tofa, kice agola kafi Wan masu gida an dawo kenan? .
? ? Matar da suke tare da Hajiya Yayan ta faWa cikin yamutse fuska idonta akan Maanal dai-dai tana isowa inda suke. Wani harbawa zuciyarta tayi har tsakkiyar kanta. Ba wai yau ne karo na farko da aka fara kiranta da sunan AGOLA gidan ba, amma har yanzu ta gagara sabawa. A duk sanda aka kirata da shi kuma tana jin matu?ar Waci da zafi a ranta. Har takanyi yunkurin son barin gidan, sai dai yin?urin nata baya zuwa ko'ina take komawa tai la?was saboda wasu dalilai. Hawayen da suka cika mata idanu ta haWiye, tare da dai-daita kanta sannan ta Wan risina fuskarta da murmushi ta ce,  Barka da gida Mamma. Aunty ina yini .
? ? ? ? Kafin Hajiya Yaya ta amsa wadda ta kira da aunty Win ta sauri ta cafe zancen cikin masifa,  Oh kaji wani Wan iskan gaisuwa wai barka da gida sai kace wasu sa'oinki? .
? ? ?Cikin sake hasala Hajiya Yaya ta ce,  Kinga da yawa ai, idan batai iyayi ba ai bata cika jinin Asiya ba, Amma wai a haka Alhaji ke neman ?a?abama jinina ita .
? ??  Humm kar kiga laifinsa wlhy Yaya, tunda uwarta ta shanyesa kina ganin shima Yazeed Win zasu barsa ne. Balle suna ganinsa shine gidan da uban gaba Waya . ta faWa tana mai ballama Maanal wata shegiyar harara.
? ? Tsamm Maanal ta mi?e kafin Hajiya Yaya ta bama ?anwar tata amsa. Cikin Wan sassarfa tabar wajen tana mai jin Waci da ciwo sosai a zuciyarta game da cin mutuncinsu ga Ammien ta. Tarasa mi Ammie ta tsare musu a gidan da su duka basa ?aunarta...?

? ? ?? Shikam Yazeed tana fita ya kife kansa a saman steering yana mai cije bakinsa da masifar ?arfi. Kai bazai yiwu ba, dolene ya zigirgiWi Daddy azo ayita ta ?are a bashi matarsa. Dan gaskiya yana cikin tashin hankali, da yasan ma abinda gyaran jikin nan zai zame masa yanzun nan daya hana yarinyar nan yinsa ko kuma ya?i komawa Wakkota. ?an buga glass Win saitinsa da akai da Wan ?arfi ya sashi Wagowa. Sai da ya Wan saisaita kansa kafin ya sauke glass Win. Da Hajiya Yaya yaci karo, ai da sauri ya janye idanunsa da sukai wani irin kaWawar da duk mai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login