Showing 3001 words to 6000 words out of 85260 words

Chapter 2 - _NIDA_BARRISTER_SADEEQ_Complete

04 Apr 2025

7411

yakuma karesa daga dukkan Abin k'i"ya k'are maganar yana tari"wai bakada lafiya ne?"kusan hakan, inada hawan jini dana kamu dashi sanadin mutuwar jummai"ga rayuwa ta sauya sai godiya"Ina *yasmeen*?be rufe bakiba wata kyakykyawar budurwa warkan tarwad'a"da zatayi 18yrs ta shigo cikin soron da sallama tana rik'e da bucket da zunbulelen hijab Ajikinta"tana ganin Abba taji fad'uwar gaba ta duk'a da sauri ta gaishesa cikin girmamawa"lafiya qlau yasmeen"idan kin shiga ciki kika klwowa babanki ruwa"dato ta Amsa ta wuce ciki"Abba yabita da kallo harta shige ciki kafin yace "na d'auka kamata Aure ma?"dan naga nan mu da wuri akema yaran Aure "hakane tanada 17yrs tayi SSCE d'inta, kuma son cigaba da karatunma takeyi"Abinda yafaru bayan mahaifiyar ta fara rashin lafiya mun tafi babbar Asibintin dake cikin birnin katsina......mlm Auwal da bala uwa d'aya uba d'aya suke"iyayensu sun mutu tuni"mlm shine yagado mahaifinsu wajen ilimin Addini harma ya zarcesa"hakan yasa yaba tilon y'arsa guda fatima(yasmeen) ilimin Addini me zurfi"tayi saukar Alkur'ani me girma ta haddacesa ,tasan littattafai da dama na Addini"sunan yasmeen yasamo Asali sbd tanada sunan kakarta"yasmeen yarinya ce me hazaka da biyayya, tanada saurin d'aukar Abu a kanta"shiyasa kaf Anguwarsu babu me hankali da k'ok'ari kamarta Acikin sa'anin ta"ita kad'aice Allah yaba mlm Auwal daga ita be koma haihuwaba"ta sami gata da ingantacciyar tarbiya me kyau Awajen iyayenta"tanada sauk'in kai da sanyin hali"wasuma malama yasmeen suke kiranta dashi"sbd ilimin datake dashi"mlm Auwal beda wata sana'a saita kiwo kawai"wannan malintar yana yinta sbd Allah ne" ya koyar da maiso dan Allah"yanada Almajirai da yamma yake koyar dasu"lokacin da jummai ta fara rashin lafiya Aka fahimci tanada breath cancer sai suka tafi Asibintin dake cikin katsina da ita"Aka fara yimata magani"daga baya mlm yadawo yasiyar da dabbobinsa suka koma Asibiti"yabar yasmeen Agidan bala k'aninsa"tana komawa samari suka mata caaa"saidai bata son kulasu"shi kuma bala Ido ga kud'i"da Anbashi kud'i zai tursasata ta fito"Ana cikin haka wani rabe yanada mata biyu da Abin hannunsa da yaransa 11"dan zai kai kusan sa'an bala dan yahaifi yasmeen"yazo rigi rigi sonta yakeyi da Aure"babu wanda yasani yanata bama bala kud'ad'e saidai kawai yasmeen taji Ance gobe d'aurin Aurenta Ansakata a lalle"lokacin dataji labarin wanda zata Aura saida ta sume"gashi babanta baya nan"wanda bala yayi hakane koda mlm yadawo yayi fad'a Aidai baza'a warware Auren ba"kuma yasan yanada hak'uri"sannan yakama waya yakashe koda mlm yakirashi baya samunsa.... yasmeen batada wata nutsuwa hankalinta Atashe aka d'aura Aure "tanata koke koke itada k'awarta lami"wacce tabata shawaran ta gudu"ta nuna bazata iyaba"kuma rabe shine yasiyi gado da ledar k'asa da kabit bala be siyi komai ba"nanfa Akayita zind'en bala Anata surutai"matarsa uwani babu yadda batayi dashiba kan A hak'ura mahaifin yasmeen yadawo Amma yak'i yadda"yasaka aka kaita gidan rabe"wadda matarsa ta biyu me zafin kishi ta kori y'an kai Amarya"sannan ta shiga d'akin tayiwa yasmeen tatas"sai wajen k'arfe 9:30 Ango ya shigo da ledar tsire da kilishi yanata washe baki yana sanye da yadi irin na y'an k'auye green"baki jage jage da miyan goro"matarsa ta biyu Laure ta fito tana binsa da kallon wulakanci tace"kaji kunya zaka shiga d'akin y'ar cikinka Amatsayin mijinta"kinga Laure wlh ki rabu dani ko jikinki yagaya miki "dan na dokeki ba k'aramin Abu bane Awajena"taja tsaki tana fad'in bissimillah mana"shareta yayi ya yaye labulen d'akin yasmeen yana washe baki yashigo"tana zaune tanata kuka"wai har yanzun baki dena wannan kukan ba Amarya ta?"ta yaye mayafin ta kallesa hawaye na zuba tace"kayiwa Allah ka sallameni bana sonka na tsaneka! zan iya kasheka"ya d'aure fuska yana Ajiye ledar hannunsa yana fad'in koda zan rabu dake dole na mori sadakina"yana fad'in hakan yanufeta"da sauri ta sauka daga saman bed d'in"yakama dariya yana koma nufarta"ta d'auki kwano nashan ruwa sabo dake saman mirror ta kwad'a masa iya k'arfinta a tsakkiyar kai"yafasa k'ara zai rik'eta ta turashi tana sakin ihu ta fito daga cikin d'akin Aguje ya biyota"matansa da yaransa suka fito tsakar gidan"lami ta dinga dariya tana fad'in bakaji kunyaba yanzun dan Allah?afusace yanufeta yafara jibgarta"tasaki ihu tana fad'uwa k'asa "saidai ganin bata motsi dayake Akwai nefa yasaka yatsaya da dukan nata,yana kallonta shida uwar gidan da sauran yara"yayinda yasmeen na daga tsaye gefen k'ofar fita daga cikin gidan.... innalillahi wa inna ilaihir raju'un ta mutu wlh! cewar uwar gidan tana girgiza ta"babban d'an Laure yafita yana kururuwa babansa yakashe mamansa"yasmeen najin hakan ta fita daga cikin gidan ta nufi gidansu k'awarta lami "hankalin rabe yatashi matuk'a da wannan Aika Aika da yayi" Adaren ranar aka kamashi"washe gari Aka mik'a Laure makwancinta"iyayen lami suka b'oye yasmeen babu wanda yasan inda take"hankalin bala yayi bala'in tashi"kwana 3 da faruwar haka rabe ya Aiko da takardar sakin yasmeen da cewar bala yabiyashi kud'insa daya kashe yabama iyalansa"sbd shi Anyanke masa hukuncin shekara 20 Agidan yari tare da horo me tsanani sbd yayi kisan kai bisa rashin sani"kasancewar babban d'ansa bejin mgn yatarama bala mutane k'ofar gidan sunata Aikato masa da jifa da zage zage "ana cikin wannan yanayin mlm da matarsa suka dawo garin"hankalinsu yatashi da suka sami labarin Abinda yafaru"mlm yaje yayima bala tas,da sanar masa duk inda y'arsa take yaje nemota nanda kwana 2 ko yayi k'ararsa"iyayen lami najin labarin dawowar mlm sukazo suka damk'a masa y'ar sa"sati ukku da faruwar hakan jummai ta rasu"mlm yakamu da hawan jini"ga halin rashi da suke cikinsa"wani daga cikin d'alibansa yamasa hanya yasmeen tafara koyarwa wata a islamiya dake Anguwar" duk wata Ana biyanta dubu goma"dasune suke samun rufin Asiri"mlm kuma yak'iyin Aure sbd beson Amatsama yasmeen"kullum da dare gidansu jummai take zuwa ta kwana"da safe saita dawo gida....tun bayan hakan yafaru manema har daga birni sunata zuwa Amma yasmeen sai tasaka kuka ita batason su"hakan yasa mlm yazuba mata Ido"da wuya ta fita batare datayi saurayiba....mlm na dasa Aya Azancensa yashare y'an guntayen hayawayen sa"shi kansa Abba yayi kukan zuci"kuma yasha Alwashin saiya d'aga darajar yasmeen ta zama Abin kwantance a wannan k'auyen nasu"Abban na k'ok'arin mgn yasmeen ta shigo soron da sallama cikin sanyin muryarta ta duk'a gaban Abba"ta Ajiye ruwa pure water guda biyu dake cikin wani plate da gidauniyar fura"tanata d'an murmushi "godiya nake y'ata kinji?"zoki Amsa "yafad'a yana zaro rafar y'an 1k guda biyu yamik'a mata"sbd yasan koya bama mlm da wuya ya Amsa "dan tun suna yara yasanshi me gudun duniya ne"itama murmushi tayi cikin ladabi tace"dan Allah Abba kabarsu"zan dai Amshi dubu d'aya sbd babu kyau maida kyauta"ta fad'a kanta Ak'asa" indai da gaske ni Abbanki ne ki Amsa yasmeen"mlm kasaka baki y'ata ta Amshi kyautata"Ai Alh sunyi yawa Asali tunda take bata tab'a ganin irin wa'annan kud'ad'en ba"hakane nidai kyauta na bayar kuma dan Allah na bayar"shikenan Allah yasaka da Alkhairinsa"ki Amsa mama nah"cewar mlm yana kallonta"yasmeen ta Amsa itama tana godiya ta koma cikin gidan....bayan Abba yasha ruwan da furan babu nuna wani k'yama"sbd kallo d'aya zaka yiwa gidan da ita kanta yarinyar kasan sunada tsabta"hak'ik'a na tausayawa yasmeen dakuma kai"saidai Ayanzun inada wani mgn me girma idan harka Amince"idan Abin ya tabbata dole na kwana Anan zuwa gobe in sha Allah saina koma dakai muje kaga likitah"to Masha Allah! Ina jinka"Abba ya sauke numfashi yana fad'in idan har zaka Amince mun inaso kabama sadeeq Auren yasmeen....dam ! k'irjin mlm yabuga"ya kalli Abba da sauri batare daya furta komai ba"kayi shiru?"ya sauke Ajiyar zuciya yana fad'in Ina mamakin yadda ka Aminta dani baka gujeniba sbd tazarar dake tsakaninmu Ayanzun"sannan kuma Ina tsoron kar na Amince sadeeq yanuna baya sonta kasan yaran zamani"dukda nasan halin mamana koda bataso idan dai na bata umarni zata Amince ta kasance meyin biyayya"idan har kabama yasmeen irin wannan shedar nima na bama sadeeq irinta"bazai musamun ba nasani"to Amma bayada wacce yakeso?"yanada ita zancen gaskiya"kuma tarbiyan yarinyar bemun ba"saidai zan barsa in har yana buk'atar Aurenta ya Aureta"ta hakan zai iya canzata"batun tazarar dakace ka hango niban gantaba"sadeeq befi k'arfin yasmeen ba"in sha Allah Ina ji Ajikina zamuyi Alfahari da wannan had'in mlm"kasaka Albarka kamusu fatan Alkhairi " inaso Ad'aura Auren gobe kafin na wuce"may be daga baya sadeeq zaizo suga juna sannan Akawo kayan lefe saita tare"kuma Anan wajenmu zasu fara zama sbd naga irin zaman nasu"sannan zan saka yanema mata university Acan ta dinga zuwa.....kukan farin ciki mlm yasaka yana yiwa Abba godiya"karka damu yiwa kaine"dama kai tsaye Anan nafara zuwa"zan wuce gidan kawu isihu(k'anin mahaifinsa) saina sanar masa goben su kawo kud'in sadaki dana neman Aure Ad'aura da k'arfe 2:00pm"daga nan zuwa dare saika sanarwa mutane"to shikenan saima Ad'aura a masallaci "inaso abiya sadaki dubu 50"dubu hamsin mlm ?"eh sadaki mafi k'aranci yafi saka Aure yayi Albarka"hakane Amma kayi hak'uri ko dubu 100 abiya"sannan babu Abinda muke so sai yasmeen banda wasu kayan d'aki"nine zan mata komai Amatsayin kai kayi batare da kowa yasaniba"gaskiya hidimar tayi yawa Alh Amadu"karka manta mlm kaima kabama rayuwata gudun muwa ,kataimakeni lokacin danake buk'atar taimako.....ninama manta da Anyi hakan"Toni Ai ban mantaba"yafad'a yana murmushi ya mik'e tsaye yana gyara malun malun d'in sa sukayi sallama yafita"mlm ya sauke Ajiyar zuciya yana fad'in ikon Allah kenan! kira ya k'walama Almajiransa guda biyu ,bayan sunzo yace"su kwashe kayan Abincin su wuce ciki dasu"har suka mayar da kayan yana zaune yana tunani"dukda k'asan zuciyarsa gani yakeyi kamar sadeeq bazaiso yasmeen ba sbd tana y'ar k'auye"saidai zai sanar mata idan har Akwai wulak'anci ta sanar masa sbd shi baya kwad'ayi"yana jin tausayin y'arsa kodan maraicin rashin uwa datake dashi.....baba gashi kaci Ankusan kiran sallar la'asar"yaji muryar yasmeen "yakalleta yaga plate d'in jalop na taliyar Hausa ne ta Ajiye masa da spoon Asama"da Alama yanzun tagama"dama suna rayuwane idan Akwai suci idan babu su hak'ura "zauna mamana muyi mgn kinjiko?"babu musu ta zauna"kinga mutumin nan daya tashi?"babban Abokinah ne tun muna yara"sai Allah yasa yatafi kano....baba ko shine Alh Amadun danaji kana yawan fad'a?"Eh shine"yazomun da zance me girma yasmeen"yazomun da zancen yanaso nabama d'ansa sadeeq Auren ki....zaro Ido tayi k'irjinta na wani irin mugun bugawa"kanta a sunkuye batace komai ba"na Amince masa mamana sbd nasan keme biyayya ce"kuma naji yace"zaki cigaba da karatunki Acan"dukda haka zanbi dare nayi istihara naga ko Akwai Alkhairi Aciki"sbd gobe da rana za'a d'aura Auren....gobe kuma?"ta fad'a tana d'ago kanta da sauri"yanata kallonta yace"k'warai in Allah yasa"saidai bawai goben zaki tareba ,saima yazo kunga juna"karki damu inaso ki nutsu ki kwantar da hankalinki sadeeq saurayine beda mata, ba tsoho bane kamar rabe"kuma Agidansu zaku zauna zuwa gaba ku koma gidanku kamar yadda mahaifinsa yasanar mun"kinfi kowa sanin halina yasmeen bana kwad'ayi Akwai manyan dalilai da suka saka na Amince da wannan Auren"saidai idan naga da matsala wlh da kaina zance Arabashi ba fata nake ba"babu komai baba duk Abinda kayi game dani daidai ne"ta fad'a cikin k'arfin hali tana b'oye hawayen dake mak'ale cikin k'wayar idanuwanta"Allah yayi miki Albarka yasmeen"insha Allah zakiyi farin ciki da wannan Auren......
washe gari misalin karfe 2:00 pm jama'a suka shaida d'aurin Auren *Sadeeq Ahmed Lamid'o da Fatima Auwal charanchi* Akan sadaki nera dubu d'ari.....Ana gama d'aurin Auren bayan sallar la'asar mlm da Abba suka d'auki hanyar komawa kano"bayan mlm yabar yasmeen gidansu k'awarta lami"bayan sallar magrib suka iso gida"kai tsaye wata private hospital aka nufa da Abba"bayan sun gama bincikarsa suka bashi gado sai yayi kwana 2 ana kulawa dashi"bayan Abba yabiya komai yamasa sallama da nufin da safe zai zo...... Agajiye Abba ya iso gidan"sai Akayi sa'a doctor keda girki"sadeeq na zaune kan kujerah da lap top Agabansa da Alama wani Aiki me mahinmanci yakeyi"Farooq na zaune kan carpet ya nutsu sbd tsawa guda yamasa yanutsu"su zarah kuwa tsoronsa yasaka suka kasa zama cikin parlourn"yana sanye da fara k'ar d'in jallabiya Ajikinsa wacce tayi matuk'ar yimasa kyau "gaba d'aya parlourn ya rikice da k'amshin turarensa"Aikin yakeyi ya tura lip nasa na kasa cikin bakinsa yana tsotsa"tun wayewar safiyar yau yakejin fad'uwar gabar dabai san dalili ba"ga suhan ta damesa da zafin waya be picking, sbd ita yakashe babbar wayarsa gaba d'aya"yana cikin Aikin Abba yashigo da sallama yana rik'e da ledoji"farouq yasaki ihu yaje ya rungume Abba "mama ta fito tasha shirinta tana murmushi tace"Alh sannu da dawowa ,ta fad'a tana Amsar ledojin hannunsa"yauwa Dr "yafad'a yana satar kallon sadeeq daya rufe laptop d'in ya sakko k'asa cikin taushin muryansa me dad'in sauti yace"Abba sannu da dawowa"yauwa babanah"dama kuwa inason mgn dakai da safe"tsintar kansa sadeeq yayi dajin fad'uwar gaba,itama mama haka"sai kawai ta wuce ciki"yayinda sadeeq ya Amsa dato yana d'aukar laptop d'in yanufi side d'insa"kai tsaye had'ad'd'en bed room d'insa ya tura k'ofar yashiga"ya Ajiye laptop d'in ya kwanta rigingine saman bed d'insa dayaji shimfid'u na Alfarma masu taushin gaske"yayi matashin kai da hannayensa"kodai Abba zancen suhan zai mun ne ?"yafad'a Azuciyarsa sbd jikinsa yabashi jiya yagansu tare"ya girgiza kansa yana jin mugun haushinta"yana ganin inhar iyayensa bazasu so ya Aureta ba saiya hak'ura "dama shi SO ba matsalar bace"yana wannan tunanin yabud'e babbar wayarsa ya hau online "tsaki yaja daya shiga what's app yaga suhan ta turo masa vedio d'inta da kayan bacci Ajikinta kanta bbu d'an kwali"tayi parking shukun da aka mata da gashin doki"rintse Ido yayi da sauri sbd jin yadda take k'aramin kuka na zallar tab'ara tana bashi hak'uri sai turo kirji takeyi"tsabar takaici da yanayin dayaji saiya koma kashe wayar"yanada burin hanata saka attached bayan ya Aureta"zai kuma sanar mata karta koma turo masa vedios tana a haka"gaba d'aya da b'acin ran data haddasa masa bacci ya kwasheshi batare daya yi Addua ba.....washe gari yana dawowa daga masjeed ya nufi d'akin dayake motsa jiki"ya kwashe kusan Awa guda yana motsa jikinsa duk yayi uban gumi" saidai yasaka handcheef yagoge"yana k'ok'arin fitowa daga ciki zarah ta shigo da sallama"ya had'e rai yana fad'in lafiya?"dama yaya Abba yace kazo"Ina zuwa"batayi mgn ba ta fita"tana gulmarsa Aranta"wai duk wacce ta Auresa ta shiga ukkunta.... Abba na zaune A parloursa da jallabiya Ajikinsa da farin tubarau yana karatun jarida"Ahaka sadeeq Lamid'o ya shigo da sallama cikin nutsuwa ya zauna kan carpet"Abba na murmushi ya Ajiye jaridar ya kallesa yace"sadeeq! k'irjinsa yabuga"sadeeq!! yakoma maimaitawa Akaro na biyu murya babu Alamar wasa"kansa ak'asa yace"na'am Abba "yafad'a zuciyarsa nasanar masa akan suhan Abba yakirashi"kasan mlm Auwal Abokinah dake charanchi?"da mamaki yace"nasanshi Abba"to Masha Allah"na had'aka Aure da y'arsa yasmeen! Ayau aka d'aura Auren "nayi hakane sbd yabawa da ingantacciyar tarbiyar yarinyar da ilimin addini datake dashi"na kuma nema maka Aurenta ne sbd nasan baza kamun musu ba"in sha Allah sadeeq zakayi farin ciki da wannan Auren.......โœ๏ธ

Ana wata ga wata ๐Ÿค“๐Ÿ˜Ž

wannan book d'in na kudine

regular grp 300
vip grp 1000
special group 2k wato 3pages in a day

zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐Ÿ‘‰2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
kituro shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

300 kawai ake turo kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne

banason transfer d'in kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโ?

y'an nijar ku tuntub'i wannan number ๐Ÿ‘‰ +227 88 01 90 50
normal grp 500f
vip grp 1000f
special grp 2000f

dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biya ba
2/26/24, 14:08 - Ummu: ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

โคโ€๐Ÿ”? NIDA BARRISTER SADEEQ โคโ€๐Ÿ”?

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story &written by
mommyn fareesa

Free page 5&6

.........wani irin dummmm sadeeq Lamid'o yaji cikin kansa had'e dajin fad'uwar gaba! zuciyarsa na tsananta bugawa da k'arfi! yafara furta inna lillahi wa inna ilaihir raju'un Aransa" fatansa Allah yasa maganganun nan dayakeji Abakin Abba A mafarkine bada gaske bane"lokaci guda zufa ta fara keto masa Ajiki ,yayinda kansa ke Ak'asa Abba na binsa da kallo yana jiran jin ta bakinsa.....*ni sadeeq aka yima Auren dole*? ya tambayi kansa da kansa....kayi shiru ko baka jine?"da k'yar ya iya jarumta tattaro haruffan kalmar nagode Abba! yafad'a zuciyarsa Acunkushe" gaba d'aya ji yakeyi kamar An buga masa guduma saman kansa sbd tsananin sarawar dayake masa lokaci guda"saidai dayake namijin gaske ne,me tsananin dakiya da jarumta sai yab'oye yanayin daya tsintsi kansa Aciki"sbd baya fatan yakasance meyin musu da mahaifinsa har k'arshen numfashi.....kayi hak'uri babanah ! nasan ko yaya zakaji wani iri kamar yadda itama yasmeen d'in zataji"sbd daga kai har ita kowane biyayya zai mana"inaso ka rik'e yasmeen da Amana da mutunci"sannan bayan ita in har kana buk'atar k'ara Aure zaka iya k'arawa in har zakayi Adalci"Ina ji Ajikina sai yasmeen ta cika gidan nan da jikoki na....rintse Ido sadeeq Lamid'o yayi yana gizon lip nasa na k'asa kamar zai hudashi"Abba yaci gaba da cewa"yasmeen ba wata babba bace zasuyi age mate da zarah"ranar friday inaso kaje ku gaisa da ita kaji koda Akwai Abinda take buk'ata"sbd banaso tarewar taku ta wuce sati 4 zuwa ukku haka"kuma Anan gidan zaku zauna"bana so ka nunawa duniya baka son yasmeen "sannu a hankali zaka sota in sha Allah"da k'yar ya d'ago kansa yana fad'in to Abba zan wuce"shikenan Allah yayi maka Albarka yabaka masuyi maka biyayya kaima"be samu damar Amsawa ba yamik'e tsaye yana had'e hanya sbd jirin dayake d'ibarsa"babbar matsalarsa yanzun itace suhan"yasan halinta game da zafin kishi ba hankaline da itaba"karma taji labari tasamesa a office cikin mutane ,ko tace zata kashe kanta"sannan taya zai gujema wannan Auren?"kamarshi gemai gemai za'ayima Auren dole.....bakaji ne wai?"yaji muryar mama"da sauri yajuya yagansa Ashe har ya iso main parlour "saidai ganin su zarah zaune suna break fast a dining area yasaka yanufi d'akin baccin maman kawai"saman bed side drower ya zauna yana furta why Abba? nizan rayu da macen da bana so"kuma k'aramar yarinya sannan villager girl?? it can wlh!! yafad'a da k'arfi yana furzan da zazzafan huci daga bakinsa "mama ta turo k'ofar ta shigo fuskarta bbu walwala"sbd bataso yamata k'orafi game da wannan Aure "kafin yasani ita Abba yafara sanarmawa"yakuma fad'a mata tayi Addua da fatan Alkhairi in sha Allah ko bata san Auren wata ran zata soshi har tayi Alfahari dashi.....dukda sadeeq Lamid'o yakasance be cika yawan kamata k'orafi ko k'arar waniba saidai yau k'wayar idanuwansa kawai data kalla ta tabbatar mata da cewa yakawo k'orafe k'orafe masu matuk'ar yawa....mama Abba yasanar miki Abinda yafaru?"yafad'a cikin wani yanayi yana kallonta da jajayen idanuwansa "yasanar mun wani abu ne yafaru?"haba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login