Showing 12001 words to 15000 words out of 85260 words
tsaye yafita ya rufe office d'in"wajen security yanufa yasanar musu da babbar murya daga yau karsu koma barin mohd ya shigo"idan kuwa suka barsa ya shigo bakin Aikinsu"yana fad'in hakan yanufi parking lot"mota yashiga ya jata Atsiyace ya nufi gida.....yana isowa gidan yasami zarah zaune a main parlour tana kallo"yaya sannu da zuwa"ta fad'a cikin ladabi"tsaki yaja ya zauna kan kujerah 2seeter cikin daka tsawa yace"tashi ki kashe tv d'in"jikinta na kirma taje ta kashe"meya hanaki zuwa skul?"ciwon ciki nakeyi"fuska Ad'aure yace duk'a ki fara tsallon kwad'o.....dan girman Allah....idan kin gama kije ki share compound d'in gidan nan"shiru tayi tafara kuka sbd dama shi tsarinsa ba'a bashi hak'uri idan Anbashi mutum yak'ara ma kansa laifi.....tunda ya zauna kalaman mohd ne ke Amsa kuwa cikin kunnansa"gefe guda na zuciyarsa yana tunanin wane munafukinne yaje yasanarwa da suhan wannan labarin??".......laifin me kikayi kike tsallon kwad'o keda kike ciwon ciki?"cewar mama data shigo cikin parlourn dawowar Asibiti kenan sbd 12 pm tayi"kasa mgn zarah tayi sbd tsabar galabaitar datayi..... Lamid'o yayi kicin kicin da fuska"mama ta kallesa ta kauda kanta ta zauna"tashi kije"be rufe bakiba zarah tabar parlourn Asukwane"mama sannu da zuwa"yauwa"dama inason na maka mgn Alh yace"ka kwashe kayan ka da Abinda zaka buk'ata ka koma side d'in bak'i kafin Agama ginin part d'in naku"sbd part d'in ka da filin dake baya za'a had'a"kasa mgn yayi zuciyarsa na zafi....sai batun lefe ni zaka bama kud'in nanda sati guda zamu had'a Akai"dubu d'ari nawane?"da mamaki mama ke kallonsa sai sannan ta lura da yadda idanuwansa sukayi jajir"ga rashin fara'ar sa nayau harya zarce na kullum"ta girgiza kanta kafin tace"oh hakama zakace?"to bari kaji million ukku zaka bayar ,dama na siyi set d'in akwatuna guda 12"zamuje nida hadiza(k'anwarta) a had'o kayan million biyu"sai Asiyi sark'a da y'an kunne da zobe na million guda na baka ka Ajiye idan tazo kabata"dato ya Amsa ta tashi ta wuce d'aki "ya girgiza kansa tare dashan Alwashin bazai bata sark'an ba suhan zai Ajiye ya siyo y'an hannu yabata Aranar daren farkonsu.....
Ab'angaren yasmeen kuwa washe garin dasu sadeeq sukazo ta bud'e wayar ta fara Amfani da ita"Abin mamaki tana kiran sarah ta saki jiki da ita suka sha fira kamar sarah damq can ta santa"itacema tace mata ta bud'e what's app "badan tasoba ta bud'e saidan shawaran da lami tabata"akan ta bud'e zata k'ara samun haske da sanin wasu Abubuwan"batak'i ba ta bud'e "sarah ta tura number nata aka sakata online class na koyan girke girke"wanda yayar sarah Hanan itace da grp d'in"cikin kwana 2 kacal yasmeen tafara koyan girki.... kasancewar umman lami ke kulawa da yasmeen ta fannin gyaran jiki yasaka ta buk'aci zuwa gidansu"dalilin daya sa ta kira mohd kenan sbd uban gayyar yace karta fita gidan uban kowa"tasan yayi hakane sbd ya k'untata mata....saidai tayi dana sanin kiransa"sbd irin bak'ak'en maganganun daya yayyab'a mata"ita damuwarta rantsuwar da yayi game da za'a kawota zata sani shine yafi komai d'aga hankalinta"bata san lokacin data kama kuka ba"ta d'auki wayar ta goge number d'insa...tana zaune lami ta shigo tsakar gidan" kasancewar mlm na soro"tana k'arasowa d'akin kallo d'aya tayiwa yasmeen ta tabbatar da cewa Akwai matsala"yasmeen lafiya?"tana kuka tasanar mata komai"kinga ya Isa karki koma kuka sbd shi"shawarata biyu dake"na farko komai tsoron dakike masa karki nuna sbd idan yagane rainaki zaiyi"sai Abu na gaba karki koma shiga huruminsa idan kinje gidan ki nuna masa baki damu da Allah yayishiba kiyi hidimar gabanki"ta haka zai fahimci baya gabanki"shiru yasmeen tayi tana tunanin zata d'auki shawara ta biyu Amma banda ta farko...sun jima suna mgn kafin lami ta wuce gida sbd ta Amso mata duk Abinda zatayi Amfani dashi na kayan gyaran jikin.....
*2 weeks later*
shirye shirye Akeyi babu kama hannun yaro"tun kwana 2 da suka wuce aka Ida kammala gina part d'in su sadeeq"Ajiya kuma akayi jere kowa mamakin kayan da aka jerama yasmeen yakeyi sbd sun d'auka mahaifinta beda hali"Acan charanchi kuwa lokacin da aka kawo lefen yasmeen kowa yagani wasu kama cewa suka rik'ayi k'ilan mlm siyarda y'ar sa yayi sbd mamakin irin Abin duniyar da aka zuba cikin lefen"wanda Abba da Abokinsa mahaifin mohd suka kawo lefen"Agefen ma'auratan kuwa babu wanda keson Auren saidai kawai sun hak'ura sbd babu yadda zasuyi"yayinda feedyn ta zuge suhan kan cewar suje har gida bayan kwana 2 da kawo Amaryar su daki y'an kayansu"suhan kuwa ta d'auki shawaran musammun yadda yanzun taga sadeeq yana damuwa da ita harma kiranta yakeyi"sab'anin da kuwa itace ke kiransa"mahaifiyar ta kuma tasanar mata Anty ta gaya mata beson yarinyar mahaifinsa yasaka ya Aureta"hakan yasa hankalinta yad'an kwanta....mohd kuwa yasan duk wasu shirye shirye da Akeyi Amma be saka kansa acikiba sbd wanda zai saka kansa danshi beda matsayi wajensa"shiyasa ya janye kansa"tun yana tunanin sadeeq zai nemesa harma yadena"Abin mamaki daya nemi wayarsa suka sanar masa yayi blocking nasa"kawai saiya nufi office d'insa da yamma"Acanma security suka sanar masa Abinda Lamid'o yabasu umarni game dashi"tare da bashi hak'uri sbd sunsan wayeshi da matsayinsa"ransa yakai k'arshe wajen b'aci yasha Alwashin shida sadeeq har Abada "har kukan b'akin ciki yayi"daya tuna tun suna y'an 4 yrs a skul suka had'u da sadeeq "sukayi wata iriyar shak'uwa"sadeeq yasha kwana gidansu shima haka"wai yanzun sbd mace da gaya masa gaskiya shine har zai masa haka....wannan dalilin yasaka yaje ya nemi file d'in da case d'in Bilal lamis yake ya fidda sunan sadeeq Acikin wad'anda keda case d'in"Acikin kwana 2 hajiyar mohd da Abbansa da sarah sun kasa gane kansa"babu irin tambayar da basuyi masaba meke damunsa ? saidai yace babu komai..... sadeeq kuwa zafin kansa kawai yasaka be nuna damuwar yanke Alak'ar dayayi da mohd ba"Amma Azuciyarsa yadamu"musammun idan yatuna yarintarsu"saidai dayake yanada kafiya kan ra'ayinsa sai yaketa k'ok'arin tunzura zuciyarsa kan yabasar da zancen"gashi jibi za'a je d'aukar yasmeen besan su waye zai turaba suje?saidai k'asan zuciyarsa yana jin dad'in zuwan nata ,kodan sbd ta Amshi hukuncin daya jima yana k'udurin yimata.....washe gari da safe misalin k'arfe 7 na safe sadeeq Lamid'o ya shigo cikin parlourn Abba "yana sanye da jallabiya coffee brown yanata zuba k'amshi"yak'ara haske sosai saidai idanuwansa jajir suke"ga sabon Aski da gyaran fuska da aka masa"tunda ya shigo Abban ke kallonsa fuskarsa bbu walwala "da k'yar ya Amsa gaisuwarsa yana fad'in na kiraka ne sbd ka tura mota biyu da yamma su kwana Acan washe gari da safe sutaho da y'an kawo Amarya "nasan zuwa Azahar sun iso da yamma saisu mayar dasu"sbd mlm yasanar mun befi mata goma bane zasu rakota tunda wuri ba kusaba.....yanzun dan Allah komai lallacewar Amarya Ance mutum goma ne zasu rakota gidanta?"Lamid'o yafad'a Azuciyarsa....baka jine ?"to shikenan Abba zan tura d'in "su waye zaka tura?"drivers"Ina mohd?"gabansa yafad'i yakasa mgn dan k'arya ba halinsa bane"Abba yaja tsaki yana fad'in Ashe bakada mutunci mutumin banzane kai sadeeq??"me mohd yamaka da zafi harka buk'aci rabuwa dashi?"iya sanina shekara 29 kenan kuna tare shine zaka yadda mak'iya su shiga tsakaninku?"to jiya mahaiifinsa yazo office yasameni kan kusan kwana 3 kenan sun kasa gane kansa "kodai na maka mgn ka tuhumi meke damunsa?"nace insha Allah zan kiraka yanzun "dana tashi ban neme kaba sai mohd d'in na nema"be sanar mun komai ba sai kuka daya kamayi yace"na tambayeka "hakan yatabbar mun da cewa matsala kuka samu ,kuma kaine bakada gaskiya"gashi kuma na tambayeka kak'i cewa komai"haba sadeeq koma miye yaka mata kabari shed'an yashiga tsakaninku da Abokinka"karka manta sanadin Abotarku yasaka nima nida Alh bara'u salisu muka zama Abokai.....shiru kawai sadeeq yayi Ayanzun ya tabbatar da cewa mohd Amini ne nagari "tunda gashi be fad'i Abinda yamasaba yace shi a tambayesa"yasan kuma muddin Abba yaji Akan suhan ne da yasmeen suka sami matsala ransa zaifi na baya b'aci"kayi hak'uri Abba dan Allah komai ya wuce"yak'are maganar cikin wani yanayi"shikenan bazan zurfafa bincike ba"saidai mohd d'in na kan hanya sbd saida na kirashi sannan na kiraka saika jira yak'araso"dato kawai sadeeq ya Amsa yana kallon wayarsa da suhan keta faman kira ya girgiza kansa kawai be d'auka ba"yarasa meyasa suhan keyin Abinda zata tayar masa da hankali tabarshi cikin wani yanayi bayan ita ba mallakinsa bace"ko jiya shagwab'ar data dinga masa yasaka da ciwon mara ya kwana da k'yar yad'an daidaita kansa.....sallamar mohd ce ta katse masa tunani"Atare shida Abba suka Amsa "mohd ya duk'a ya gaida Abba kafin ya zauna gefen Lamid'o"sadeeq yabashi hannu sukayi musabuha"Abba yayi murmushi yana fad'in Alhamdulillah yaranah ko kufa"Allah yak'ara had'e kanku Adena yawan fushi da juna "dama shi haka zaman tare yagada"insha Allah Abba zamu kiyaye"cewar sadeeq shidai mohd na zaune bece komai ba"Abba ya mik'e tsaye yabasu waje"sadeeq ya kallesa yace"kayi hak'uri Abokinah.....babu komai Allah ya kyauta"da k'arfe nawa za'a je d'aukar yasmeen d'in goben??"saida sadeeq ya d'auki kusan second 5 kafin yace"yau za'a tafi da yamma gobe Ataho dasu"okay sai muje da idi driver ko?" Aida kabarsa sbd yanayin Aiki"babu damuwa indai game da hidimarka ce"yafad'a yana mik'ewa tsaye,shima sadeeq ya mik'e tsaye suka fita"mohd nata kallonsa sbd ba k'aramin kyau yayiba"saima yanzun yaga irin dacewar da sukayi da yasmeen "dan harta kalar fatarsu chacoolate iri d'aya ce"saidai yasha Alwashin bazai koma gigin yimasa zancen yasmeen ko suhan ba inba shine yamasa ba.......
washe gari misalin karfe 3:11 pm y'an kawo Amarya suka iso katafaren gidan Alh Ahmed Abubakar lamid'o.... y'an maraban Amarya na babban parlourn gidan zaune "dukda mama tayiwa salma da hafsat jan ido akan kar suyi Abinda za'a fita dasu Abakin duniya"suna dai zaune suna jiran isowar Amaryar suga yaya take?....tunda suka taso hanya gaban yasmeen ke fad'uwa "wacce tasha gayunta cikin sabuwar gownt ta lace da Alkyabba tanata zuba k'amshin humrah da kulakcah"tunda suka shigo gidan zuwa fitowarsu Amota addu'o I ne takeyi a ranta kamar yadda mahaifinta yabata shawara"taci kukan rabuwa da babanta shima bayan fitowar su har hawaye yayi"matan hakimin garinsu su ukku sune rik'e da yasmeen da shiga ta mutunci Ajikinsu"sai lami da ummanta dake bayansu da uwani matar kawu bala"sai mata 3 dake fannin dangin mamanta"duk wanda ya kallesu bazai musu kallon rainiba"wanda tunda suka shigo ana bud'a kowa su yake kallo"babbar k'awar mama ta tashi ta musu sannu da zuwa ta rik'e hannun yasmeen ta zaunar da ita Atsakkiyar parlourn "Anty dame Aikinta suka kamusu Abinci cikin take aways da drinks aka Ajiye musu"sai yatsina Anty keyi mama na lura da ita"bayan wasu y'an mintina akayi Addua "salma tayi saurin cewa Abud'e mana fuskar Amaryar mu yayun miji mu rigasa gani"me kikeci na baka na zuba? Anan zamu bar muku ita"cewar k'aramar matar hakimi "mama na murmushi tace hakane"bayan Angama raha suka mik'a Amanar yasmeen dayin godiya da Addu'ar samun zaman lafiya"sannan suka d'auketa suka wuce shashenta da ita....bata karan y'an kawo Amarya ba har ita kanta Amaryar tayi mamakin had'uwar gidan da tsarinsa"da irin wa'annan gidajen saidai ta gani a TV"bata tab'a shiga cikinsu"gashi yau bama shigaba rayuwa zatayi Aciki" saidai bata ji wani dad'i ba ko ganin Amfaninsu tunda wanda aka kawota tayi zamansa be k'aunarta....lami kuwa tsabar murna pictures ta dingayi da wayar yasmeen tace ta tura mata ta what's app "sai wajen k'arfe biyar kowa ya watse"Aka bar yasmeen da sarah wacce bata jima da zuwa ba"sai jan yasmeen da fira takeyi Amma ta lura batada walwala "saita Alak'anta hakan da fargaban da kowace Amarya ce keyi ke damunta....Acan cikin gida kuwa salma da hafsat suka sato jiki batare da mama ta luraba suka nufi sashen su yasmeen dukda d'azun sunje sunga jeren Amarya"suna na nan a bed room sarah na waya da mohd ,tana sanar masa itadai da magrib tayi yazo ya maida ita gida babu kowa"yasanar mata suna tare da Lamid'o yanzun haka da sunyi magrib Atare zasu shigo gidan sai ya d'auketa su wuce gida"bayan ta yanke wayar ta kalli yasmeen zatayi mgn taji ana cewa.....salamu Alaikum Ina Amaryar ne , yasmeen ko waye take???cewar Anty salma A gadarance suna shigowa cikin had'ad'd'an bed room d'in yasmeen......✍️
bazan komaiba guys sai mun had'e a paid grps kamar yadda aka saba zakuga me NIDA BRR SADEEQ ke tafe dashi kundai san alkalamin mom fareesa baya rubuta shirme🥰🥰
Maza hanzarta biyan naki tanan sbd adama dake a tafiyar👇
wannan book d'in na kudine
regular grp 300
vip grp 1000
special group 2k wato 3pages in a day
zaku biya kud'in ku ta wannan acc number👉2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
kituro shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne
banason transfer d'in kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kira?
y'an nijar ku tuntub'i wannan number 👉 +227 88 01 90 50
normal grp 500f
vip grp 1000f
special grp 2000f
dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biya ba
2/26/24, 14:08 - Ummu: *Littafin kud'i ne!*
........gaban yasmeen yayi wani irin fad'uwa ta d'ago kanta da sauri tana Aza dara daren golden eyes d'inta saman fuskarsu" kasancewar ta cire Alkyabbar dake jikinta"Ido hud'u ta farayi da Anty salma wacce ke a gaba tana binta da kallo kamar TV....Ayanayin kyawun halitta tayi 100% ! saidai babbar matsalarta y'ar talakawace kuma y'ar k'auye wacce bata waye ba"duk salman ta Ayyana haka Aranta "yayinda sarah ta Amsa sallamar su ta kauda kanta batare datace komai ba,sbd Alamar rashin mutunci data gani Atare dasu"Ina wuninku??cewar yasmeen tana kauda kanta "suka yatsina fuska hafsat tace"na d'auka baki iya gaisuwar bane sai kallon mutane?"to bari kiji da kyau! keba sa'ar Auren sadeeq bace"suhan itace daidai dashi da kuma tsarinsa"kuma nan bada jumawa ba zata shigo gidan nan sbd da ita yadace"munsan komai ba sonki sadeeq keyiba "kwad'ayin cin gado da dukiya yakawoki"sai kiyi k'ok'ari ki haihu sbd ki samu....hafsat ta karb'e zancen da cewa"uhmm Ahaka kike tunanin sadeeq zai rab'eta?......haba Anty salma meye kukeyi haka?"wlh saina gayama mama"sukaji muryar zarah Abayansu "kafin suyi mgn ta juya da sauri tabar wajen"dama mama data lura da basu nan tace mata,tazo ta duba nan taga ko suna nan"kuma koda tazo tsaye tayi bakin k'ofar bata shigo ba"tsaki sukaja sukabi bayanta da sauri"yasmeen kanta na'a k'asa tana furta kalmar innalillahi wa inna ilaihir raju'un Azuciyarta "hawaye masu zafi na wanke mata fuska, tana tambayar kanta meye laifinsu itada iyayenta da sauran mutane da sbd suna talakawa kuma y'an k'auye??.....dan Allah kiyi hakuri karki zubar da hawayenki Abanza sbd su"in sha Allah sai kin taka babban matsayi Azuciyar sadeeq "suhan kuma da suke miki zancenta Ayadda yaya mohd yasanar mun da mugayen halayenta wlh sai sun gane kuransu ya Aurota"ki tashi kiyi Alwallah muyi sallar magrib"nasan zarah saita sanarwa mama komai"saidai gaskiya zarah dama ita batada matsala"tun a skul nasan halayenta"sudai wa'annan sune keda mugun hali"kasa cewa komai yasmeen tayi jikinta Asanyaye ta tashi ta nufi bath room ta d'auro Alwallah"duk idan ta tuna da sadeeq sai taji fad'uwar gaba "daurewa kawai tayi sukayi salla"bayan sun gama sarah taci gaba da bata y'an shawarwari Ahaka kiran mohd ya shigo cikin wayarta"hakan yasa ta kalli yasmeen tace bara na wuce"yaushe zaki dawo dan Allah?"ta fad'a tana kallonta da fargaba saman fuskarta "Eh to da kamar wuya nadawo yasmeen sbd halin mijin naki"nifa ko gaisuwata baya Amsawa"saidai yaya mohd yace"mun bayan sati guda zaki fara zuwa skul "kuma a skul namu za'a kaiki kinga Any time muna tare indai course d'aya zamu karanta....shigowar wani kiran na mohd yasaka tasaki murmushi ta d'auki wayar tana lankwashe murya ta fita"yasmeen tayi ta gumi ta Lula tunanin irin zaman da zasu da wannan meji da girman kan "ga yunwa da k'ishirwa ga damuwa"saidai Aganinta duk masu sauk'i ne da Ace ta had'u da sadeeq Lamid'o"sarah bata jima da fitaba zarah ta shigo cikin d'akin da sallama tana rik'e da wata kula da leda fara irinta shopping Ahannunta"yasmeen ta kalleta ta Amsa sallamar ta"tana d'an murmushi tace" Anty yasmeen gashi inji mama tace kici" kuma dan Allah kiyi hakuri Akan Abinda su Anty salma suka miki"lahhh ! kice mata babu komai nagode"dato ta Amsa tana Ajiye sak'on ta fita"yasmeen ta sauke numfashi tana bud'e Abincin"friend rice ce with chicken"sosai taci ta k'oshi tasha ruwa batare data tab'a lemon ba"bayan ta idar ta tashi ta kabbara sallar isha'i"ta jima tana Addu'a sannan ta d'auki kular Abincin ta fito daga cikin d'akin"da nufin ta mayar a kitchen...... k'irjinta ne yayi wani irin mugun bugawa sbd yalwataccen k'amshin turaren mutumin nata da hancinta yashak'o mata"ta lumshe Ido tana sauke Ajiyar zuciya"in bacin tayi k'ok'arin rik'e kular gam da tuni ta sub'uce daga hannunta"sbd tsoron dataji"sunan Allah kawai take Ambata Aranta, tana d'an daidaita nutsuwarta ta kalli cikin parlourn"sadeeq Lamid'o na zaune kan d'aya daga cikin kujerun da sukayi matuk'ar k'awata parlourn"sanye yake da wani milk d'in yadi me taushin gaske da shara shara har ana iya hango fara k'ar d'in vest d'in dake jikinsa"kansa babu hula yayi wani irin sanyayyan kyau"saidai ya had'e gabas da yamma ya daure fuska"laptop na gabansa Ajiye saman center table yana Aiki da ita"yatura red lip nasa na k'asa yana tsotsa"tunda yaji motsin turo k'ofar da yasmeen tayi ransa yabashi itace ta fito"saiya yak'ara had'e rai beko kalli gefen datake ba"parlourn ya tsaru ya kuma k'awatu matuk'a"A upstairs nan shashensa yake"yasmeen kuma parlourn da 2 bed rooms sai kitchen da dining area sune nata"kallon second 10 ta masa ta d'auke kanta tana tunanin inane kitchen??k'ofar dake gab data fita Anan ranta yabata shine kitchen"hakan yasa ta wuce can da sauri...masha Allah! ta fad'a Aranta tana k'arema kitchen d'in kallo da Abinda ke cikinsa"duk wani Abu na buk'ata Akwai Aciki"wata k'ofa ta bud'e taga store ne shak'e da kayan Abinci "kular ta Ajiye ta bud'e fridge Abin mamaki shima Akwai ruwa da lemo Aciki kala kala"ikon Allah! Ta fad'a tana Ajiye drinks d'in data shigo dasu ta rufe fridge d'in ta jingina Ajikin cabinet"tsoronta guda shine kar tazo wucewa yamata mgn"sannan tana gudun ta gaishesa ya disgata....ganin babu mafitah yasaka ta fito daga cikin kitchen d'in tana tuna ita ga yadda daren farkonta suke zuwa mata"wancan yazo a rikice wannan yazo Abaibaice.... sadeeq Lamid'o kuwa yayi