Showing 6001 words to 9000 words out of 85260 words

Chapter 3 - _NIDA_BARRISTER_SADEEQ_Complete

04 Apr 2025

7409

mama! bazaki nuna masa illar hakan ba?"okay so kakeyi nayi takara da hukuncin Allah,ko kuwa so kakeyi nace kabujirewa maganar Alh??"karka manta matar mutum kabarinsa "tun jiya nake sanarwa Allah idan babu Alkhairi a wannan Auren Allah yarabasa"idan kuma Akwai Alkhairi Allah yasaka muku son junanku kaida ita....yatsina fuska yayi yana girgiza kansa "mama ta zauna gefen bed d'in cikin rarrashi tace kayi hak'uri babanah ka kasance meyin biyayya kamar yadda itama yarinyar tayi"karka manta namiji mijin mace 4 ne idan kana ra'ayi saika k'ara Auren ka agaba"Amma bana baka goyon bayan ka bujurema umarnin mahaifinka"sannan bance kanunama kowa baka son Auren nan ba , musammun hafsa da salma "shiru yayi yak'i mgn dan beso ana wani cewa yak'ara Aure"sbd tsarin mace guda yake dashi"kusan mintina 3 beyi mgn ba yamik'e tsaye yabar d'akin "mama ta girgiza kanta itadai fatanta Allah yasa sadeeq karya cutar da y'ar mutane ,sarai tasan halinsa idan baya son Abu...yana fitowa yasami moon itada Amira suna guje guje....wata rikitacciyar tsawar da y'an hanjin cikinsu suka kad'a yasakar musu"Atake suka nutsu"yaja doguwar tsuka yafita yana bar musu daddad'an k'amshin turarensa"directly part d'insa yanufa zuciyarsa na wani irin had'ewa "yana tunanin dole yaje yaga mohd suyi mgn Asami mafitar dazai gujema wannan kaddararran Auren" Amma gsky bazai iyaba...... jallabiyar jikinsa yacire ya d'aura farin towel iya k'ugunsa"nabi manyan k'wanjinsa da kallo Masha Allah"ba k'aramin karfaffan mutum bane"gaba d'aya bashida walwala Ahaka yashiga bath room d'in,yafi mintina 30 yana wankan yana tunani had'e da jan tsaki"wani irin mugun tsanar yasmeen da haushintane dank'are Aransa, dukda kasancewar besan taba "komai nasa Atsare kan lokaci yake gudanar dashi Amma yau gashi daga wanka zuwa shiryawa yabata kusan Awa guda sbd haushin wata kucaka.....dukda a bad mood yake Amma milk suit d'in dake jikinsa ba k'aramin kyau da karb'an sa sukayiba"ya hade rai sosai fuskarsa babu walwala"yafito yana rik'e da wayoyinsa da keys d'in motarsa"lokacin k'arfe 8:34 am"bayan kuma k'a'idarsace 8:00am a office take masa"ko daya fito tacan k'ofar baya yabi ya iso parking lot ,sbd beson ya had'u da mama tamasa zancen yatsaya yayi break fast.... Asukwane driver ya iso yana kwasar gaisuwa ya Amshi key d'in motar ya bud'e masa back sit ya shiga"batare daya ce kanzil ba"hakan yasaka driver d'in jan bakinsa ya tsuke be furta komai ba"yana ganin kiran mutane a babbar wayarsa da k'aramar Amma duk ya musu banza yana jan tsaki"da k'yar yace police station zamuje! to yallab'ai"suna gab da isowa wasu motoci suka iso Aguje zasu bangajesu"driver d'in yayi saurin kaucewa....maza ka gangara kayi parking! yafad'a murya adake yana huci"tun kafin yagama parking motocin suka zagayesu"sadeeq Lamid'o yasaki tattausan murmushin daya nuna Ainahin baiwar kyawun halittar sa"driver d'in na k'ok'arin fitowa Lamid'o yayi saurin dakatar dashi wajen cewa yi zamanka"daga haka yabud'e k'ofar da k'arfi ya fito.....hahahahahahahaha!! yaji suna kecewa da wata mahaukaciyar dariya"kusan su goma k'atti majiya k'arfi"duk suna tsaye da manyan makamai Ahannunsu "yayinda Bilal lamis ke zaune saman mota yana busa sigari"yana bin sadeeq da mugun kallo "yana kuma mamakin da bega tsoro a k'wayar idanuwansa ba....sadeeq kuwa tsaye yayi yana binsu da kallon k'asan Ido yana shafa lallausan b'akin sajensa d'aya zagaye kyakykyawar doguwar fuskarsa.....me kukejira da bazaku afka masa ba ne?"inaso kasani zan wulak'antaka Agaban bainar nasi kuma gab da police station bbu Abinda zai faru"cewar Bilal cikin kurari da d'aga murya "kusan mutum biyar suka nufi sadeeq da makamai a hannunsu"hankalin driver d'insa dake zaune yana kallon komai ta glass yatashi"yana ganin kamar sadeeq bazai iya dasuba"saidai tun kafin su iso yayi tsalle guda yashaki k'ato guda yabuga masa kansa ya Amshe wuk'ar hannunsa yana karashi gefensa wad'anda suka kamasa suka suka yankesa a k'ahon zuci ya sulale cikin jini"cikin mintina 5 sadeeq yabazar dasu duk yamusu rauni"sai gashi sauran biyar d'in suka fara ja da baya"shi kuwa fuskarsa d'auke da k'ayataccen murmushi yanufi wajen Bilal"cikin tafiyarsa irinta kas'aitatun mazan da suka Amsa sunansu maza"dallah banzaye ku hau kansa mana"cewar Bilal gabansa na fad'uwa yadiro daga saman motar"mutum biyu suka nufi sadeeq Atare yabazar dasu k'asa ya iso gaban Bilal"Ido cikin Ido ya kallesa yasaki malalacin murmushi sannan ya had'e rai ya fisgosa yafara bashi zafafan puncher's kota Ina"yayinda mutane sunfi 30 zagaye dasu suna kallonsu"cikin zafin rai sadeeq ke furta zan wulak'antaka naje dakai na rufe naga shegen daya Isa yafito dakai"shashasha lusarin namiji"yafad'a yana fisge rigar dake jikin Bilal yayi saura daga shi sai dogon wondo da farar vest"yayinda sauran kantin ukku suka gudu"Bilal kuwa fuska ta kumbura,hanci da baki duk sun fashe"jibgarsa kawai sadeeq keyi babu tausayi Aransa yana jansa k'asa kowa nagani"wasu suka fara binsu wasu kuma basu bisuba"tafiyar mintina 10 yayi da Bilal yana dukansa har suka iso police station d'in"yana huci ya halbasa da k'afarsa me takalmi sawu ciki "da kansa yakaisa cell ya rufe yana nufar office d'in mohd yaja kujerah ya zauna yana furzan da zazzafan huci daga bakinsa"yayi bala'in had'e rai sbd wasu mata biyu daya gani suna mgn sai kallonsa sukeyi"dama haka yakeyi idan yaga mata"tamkar mohd yayi dariya yadai dake ya sallamesu "dama tun farkon fara fad'an su da yaran Bilal Aka kira mohd Aka sanar masa"bejeba be kuma tura kowaba"sbd yasan waye Abokinsa ko sun kai su 50 zai iya dasu cikin ikon Allah....tun bayan fitar matan yake kallonsa yana nazarinsa"Atake ya fahimci yanada damuwa"dama kuma yasha Alwashin bazai neme saba saidai shi ya nemesa tunda be masa laifin komai ba"Ayan zun ya tabbatar da Lamid'o yanada damuwa"sbd yasan indai sbd Bilal ne yana rufesa office d'in commissioner zashi bazai neme saba"kuma sbd Bilal bazai saka damuwa Aransa ba..... Abokinah barka da Asuba! cewar mohd sbd yasan zafin kan Lamid'o da wuya yatankasa"d'ago kansa yayi yazuba jajayen idanuwansa saman fuskar mohd murya asark'e yace"inada damuwa Abokinah me tsananin girman gaske" pls kabani mafitar yadda zanyi"saidai kasake kamun dariya wlh saidai ran kowa yab'aci"d'an murmushi mohd yayi yana sauke Ajiyar zuciya sbd jin kalaman Lamid'o na k'arshe "hakan yatabbar masa da cewa" matsalar ba wata babba bace ba"tunda gashi yana zancen wai karya masa dariya"okay tell me......cikin wani yanayi sadeeq yamasa bayanin komai"ya d'ora da cewa" inda ba k'aramar yarinya bace zan iya hak'ura bayan y'an watanni nasan yadda nayi na rabu da ita"Amma bazan iyaba, ga suhan kasan halinta Akaina babu Abinda bazata iya ba"banaso ta tashi hankalinta"pls tayaya kake ganin zamu bullowa Abin?"kodai zuwa zamuyi mu biyata kud'i tacema mahaifinta bataso yasaka nasaketa??.....da wani irin shock mohd ya kallesa yana girgiza kansa yace" wannan shine babban kuskuran da zakayi musammun idan Abba yagane"meyasa kai bazaka bujureba sai ita kakeso ka yaudara da kud'i?"tabbas mutanan yanzun sunayin komai sbd kud'i"saidai ba duka Aka taru aka zama d'aya ba"nidai idan zakaji tawa ka hak'ura ka Amshi Auren nan da daraja insha Allah zakayi farin ciki dashi Ina jin hakan Ajikina"sannan bazan b'oye makaba Lamid'o wlh naji dad'in Auren.....wani banzan kallo sadeeq yajefa dashi"yasaki d'an murmushi yana fad'in dama nasan yanzun bazaka ganeba"wacce zuciyarka take kanta itama ba sonta kakeba burgeka kawai takeyi"inaso kasani !ba'a sanin maci tuwo sai miya ta k'are"kuma d'an hakkin daka raina shine ke tsone maka ido"sbd wata suhan karka yadda ka bujurewa iyayenka"inda zakaji shawarata daka hak'ura da ita Ango ,sbd sam bata dace da kamili kamarka ba"wai yama sunan Amaryar tamu ne?? yak'are maganar yana b'oye dariyarsa sbd yasan yakai Abokin nasa mak'ura,yakuma d'auresa da kalamansa.....doguwar tsuka yaja ya mik'e tsaye yana fad'in wlh sbd kana mun irin hakan zamu iya rabuwa dakai har Abada"Aikin banza kawai"yafad'a yana doka table d'in gabansa ya mik'e tsaye yafita afusace"mohd ya girgiza kansa yana jin tausayin yarinyar data zama mata ga sadeeq "da hanzari ya d'auki landline phone yakira yasanar Arufe cell d'in da Bilal ke ciki, sbd kar sadeeq yaje ya huce haushinsa kansa"yasan halinsa da bak'ar zuciya kar yaje yayi kisan kai....

******
kimanin kwana 3 kenan da faruwar hakan"mlm yasami lafiya sosai"sun bashi magunguna"Abba yasaka driver yakawosa har gida da Abin Arzik'a"yasmeen kuwa dukta tashi hankalinta sbd gudun kar wanda aka Aura mata baya sonta"lami kuwa da mahaifiyarta murna suka dinga taya yasmeen "sbd sunsan mahaifinta bazai mata zab'en tumun dare ba"dandanan umman lami tafara bama yasmeen kulawa da shawarwarin yadda Ake zaman Aure"ita dai ji kawai takeyi"wani irin mugun tsoron Auren da wanda ta Aura d'in takeji"tana gani babanta yazo yayima iyayen lami godiya yabada kud'i afara yimata gyaran jiki sbd dangin mamanta ba'a nan sukeba"gashi baba yasanar mata ranar friday sadeeq zaizo"gaba d'aya batada walwala wani iri takeji Azuciyarta...
Ab'angaren uban gayyar kuwa gaba ya d'auka da mohd baya kiransa baya zuwa wajensa"yayinda har yanzun Bilal na'a rufe"mutanan cikin gidan su kuwa kowa yaji labarin Auren,wasu sunyi murna wasu akasin hakan"suhan kuwa jiya suka shirya da mutumin nata yagaji da fushin dayakeyi da ita.....tun wayewar garin yau zuciyar sadeeq a cunkushe take sbd yau zai tafi charanchi wajen yasmeen "gashi yana fushi da mohd"besan waye zai masa rakkiya ba"kuma Abba yasanar masa yaje yayi Abinda yaka mata"muddin beje ba ransa zai b'aci"tun wajen k'arfe 10 yagama shirinsa cikin milk d'in shadda sabuwa"wacce akayima Aiki da dark brown d'in zare"komai yasaka brown"yanayin yadda wankan ya Amshesa zaka d'auka yau aka d'aura Auren"har wani haske da shek'i fuskarsa keyi"su moon na zaune a main parlour ya shigo"suka bishi da kallo suna gaishesa yamusu banza ya nufi d'akin Ammi....wlh An cuci yaya kamarsa kyakykyawan gaske me Aji da kud'i da mata ke rubi binsa za'a had'ashi da y'ar k'auye"cewar moon"wayace miki y'ar k'auye ce? charanchi ai LG ce"kuma yarinyar tayi karatu"kuma Ahaka yana son kayarsa"cewar zarah"wai dama shike sonta?"Eh mana"to Anty suhan fa?"oho musu....murya can ciki yayi sallama ya shigo cikin d'akin"mama na tsaye gaban mirror tana shiri zata tafi Asibiti"ta juyo taga yadda ya wani had'e rai tayi d'an murmushi tana fad'in kai babanah haka zakajema y'ar tawa kana wannan d'aure fuskan?"kaida yakamata kaje da fara'a"to nidai kace Ina gaisheta ,sannan ka kula ku gaisa cikin mutunci kana jina?"da k'yar yace uhmm"sbd yafahimci har yanzun mama bata fahimci yadda yatsani Auren bane"kuma itama yarinyar saita gane kuranta.... ringing d'in wayarsa ya katse masa tunani "yana dubawa yaga mohd ne"yaja k'aramin tsaki yana yanke kiran"mama ta kallesa taga shida waya ne"beyi mgn ba yafita"Allah yasa yarinyar nan me wayoce da hikima ta haka kawai zata canza mana kai sadeeq....yana fitowa bakin get ya lura da motar mohd"hakan yasaka yakoma had'e rai"mohd dake can baya tsaye yana waya da sarah yana sanar mata labarin Auren ya kallesa yayi murmushi yana yanke wayar "saidai kawai sadeeq dake k'ok'arin shiga mota yaji muryar mohd yana fad'in Abokinah idan bazaka nemeniba ni gashi nazo nemanka"komai yayi zafi maganinsa Allah yin dogon fushi ko gaba banaka bane"sadeeq beyi mgn ba yashiga cikin motar ya zauna "shima mohd saiya zagayo ya shigo ya zauna gefensa yana fad'in yanzun tafiyar ce shine kafi k'arfin kasanar mun?"wai meka d'auki kankane Lamid'o?"look mlm ! idan zakaje muje idan baraka kajeba kawai kabarni"ita kuma wlh saita sani"kamarya saita sani?"wlh kaji tsoron Allah karka cutar da y'ar mutane"banza sadeeq yamasa"driver yashigo yajasu....motar ta d'auki shiru sbd ba fira suke ba"saidai mohd ne ke waya da sarah"sai sadeeq daya mak'ala earpiece a kunnansa sbd beson jin surutun mohd"koda yagama wayar saiya fara tsokanarsa wai karyaje ya kama y'ar mutane yabari sai Ankawota"tamkar sadeeq yarufesa da duka haka yaji"saiya masa banza kawai" ...tafiyar Awa biyu sukayi suka iso charanchi" saidai ganin masallacin juma'a a hanya yasaka suka tsaya sukayi sallar juma'a.....tun bayan mlm yasanarwa yasmeen zuwan yau sadeeq zaizo"ta fara gyara soron,bayan ta share ta goge sumintin ta kunnah turaren wuta ta shimfid'a darduma sabuwa ta mlm"ruwan roba da lemo ta tanada sai snacks da sukaje wani shago bakin titi suka siyo itada lami"sannan suka soya musu kaza"basuyima gigin dafa musu Abinci ba sbd ran yasmeen yabata su y'an gayune bazasuci Abincin suba"saidai sun dama musu fura dataji kayan Hadi"lami nata tsokanarta wai idan mijin mummunane yaya zatayi?"itadai saidai tayi murmushi kawai"cikin fargaba tayi wanka ta shirya cikin k'uru adakarta"sabuwar Atamfar sallarta datake matuk'ar jida ita light green da ratsin black"batayi make up ba "saidai tayi masifar kyau "lami na zaune tanata kallonta"tana yaba kwawunta Aranta"yasmeen ta d'akko hijab gogaggiya ta fesa mata turare ta Ajiye "kina nufin hijab zaki saka?"Eh mana "dakin b'ata kwalliyarki wlh"sannan ki shafa lips stick hjy sbd nasan idan kikayi make up tamkar ba indiya kike komawa"nifa lami ki k'yaleni bazanyiba"bana buk'atar yasoni sbd kyawuna dan kyau yana gushewa"ta hanyoyi guda ukku na (1) tsufa" na (2) rashin lafiya)na (3)talauci.....wannan gaskiya ne"bara nide nayi sallah tunda ke kinyi"dato ta Amsa"Adaidai lokacin da yasmeen taji horn d'in mota"gabanta yadinga wani irin mugun fad'uwa"mlm da dawowarsa kenan daga sallar juma'a "yana sanye da kayan mutunci ya fita k'ofar gidan..... sadeeq da mohd na tsaye gefen motar"mohd nata Aikin rarrashinsa kan yayi Abinda yadace kar yayi Abinda zai zubda mutuncin iyayensa "kasancewar dama yasan fuskar mlm dukda yajima began saba Amma yana hangosa yaganesa"Assalamu Alaikum! wslm baba sannu da fitowa"cewar mohd"sadeeq yak'ak'aro murmushi suka duk'a suka gaishesa"ya Amsa fuska Asake yana fad'in ku shiga ciki "yak'are maganar yana yin gaba"gaba d'aya suka bi gidan da kallon tausayi "suna shigowa k'amshin turaren wutan yadaki hancinsu"sadeeq yatab'e baki yana zare takalminsa suka zauna "Masha Allah! kasamu irin wacce kakeso wato me tsabta"banza sadeeq yamasa yacigaba da danna waya "baba yafito yasanar musu tana zuwa kafin yafita"sadeeq yaja tsaki yana kallon muhd yace"duba time kagani "wani aji ne da ita dazata shanyamu"koda cikakkiyar mace ce ita ta Isa tajamun aji balle ita k'aramar yarinya?"d'aure fuska mohd yayi bece komai ba sbd hango wata yarinya dayayi rik'e da tray"Ahankali lami ta musu sallama mohd ya Amsa ta Ajiye tray d'in tana murmushi ta gaidasu"kallo bata ishi sadeeq ba jikinsa yaba shi ba itace bace yasmeen"sannunku da zuwa ya hanya?"Alhamdulillah"Masha Allah ga k'awar tawa nan tafe"Ina Angon namu ne?"tafad'a tana satar kallon mohd ta d'auka ko shine sbd lura datayi yafi sakin fuska"da hannu mohd ya zunguri sadeeq"yana fad'in gashi nan ni Abokinsa ne kamar yadda kike k'awar Amaryar tamu"kallonsa kawai lami keyi cikin mamaki had'e da rud'ewa " dukda taji haushin sharetan dayayi saita kauda kai ta mik'e tsaye ta wuce ciki tana tunanin gaskiya wannan me girman kan yafi k'arfin yasmeen.....ka kyauta kenan Lamid'o?"wace irin zuciya ce dakai?"shikenan kaga zatace bakada kirki ko?idan ta shiga zata fara sanar mata halinka na k'yaliya.....saime dan wata banza tace banida kirki ne? shikenan kayi duk yadda kakeso wata rana sai labari.....da sauri lami ta shiga d'akin tana fad'in yasmeen kingan shi kuwa?"kinada matsala lami?"Ina ruwana da muninsa?"ta k'are maganar fuska bbu walwala tana gyara hijab d'inta"bafa haka nake nufiba "ke nifa tunda nake ban tab'a ganin mutum d'an gayu Ido da Ido me tsananin kyau kamarsa ba"ga wani irin mugun k'amshi sunayi shida Abokin nasa"har yanzun ban dena jin k'amshin suba"kuma shima Abokin nasa wlh ya had'u"dan Allah ya Isa haka muje mana"Ina ?"can wajensu ko?"ah ah wlh kije kedai wajen mijinki"k'ilan ya rungumeki"tsaki yasmeen taja tana saka plate shoes nata ta fito tsakar gidan"wani iri takeji Ajikinta"tana jin kamar karta fita"tsoro,fargaba , fad'uwar gaba duk sun mamaye mata zuciya"da k'yar ta daure jikinta na kirma ta nufi soron d'auke da sallama cikin y'ar siririyar muryarta me tsananin dad'in sauti......โœ๏ธ

wannan book d'in na kudine

regular grp 300
vip grp 1000
special group 2k wato 3pages in a day

zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐Ÿ‘‰2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
kituro shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

300 kawai ake turo kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne

banason transfer d'in kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโ?

y'an nijar ku tuntub'i wannan number ๐Ÿ‘‰ +227 88 01 90 50
normal grp 500f
vip grp 1000f
special grp 2000f

dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biya ba
2/26/24, 14:08 - Ummu: ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

โคโ€๐Ÿ”? NIDA BARRISTER SADEEQ โคโ€๐Ÿ”?

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story &written by
mommyn fareesa

free page 7&8

........tun daga nesa Yasmeen ta hango mohd daya gyara zamansa yana kwasar dad'i yana lumshe Ido"yayinda uban gayyar ke zaune yana kallonsa yana yatsina fuska"can yaja gajeran tsaki ak'ule yana fad'in wai mlm meye haka?sai kace wani bak'on cin wannan Abin?"karma yarinya tasameka kana irin haka tace zata rainani na tattakata wlh...kaga idan zakaci muci kawai ,idan baraka ciba kabarni naci na kuma kaima driver sauran....shiru sadeeq Lamid'o yayi sbd jin sautin siririyar muryar yasmeen data musu sallama "be Amsa sallamar tataba"saidai rai daya koma had'ewa yana jin zuciyarsa na wani irin bugawa"yana kuma mamakin meyasa yaji hakan??.....saima ya d'auke kansa cikin basarwa...wa'alaikissalam ran Amaryar mu yadad'e"irin wannan jan Aji haka ?"duk Abokinah ya k'osa ya ganki"yak'are maganar yana murmushi had'e da satar kallon sadeeq yaga ya murtuke fuska kamar zai had'iyi zuciya"itadai yasmeen d'an tak'aitaccen murmushi ta saki tana d'an zama gefen tabarmar zuciyarta na wani irin harbawa da sauri da sauri"yayinda hancinta ke shak'o mata ni'imtaccen k'amshin turarukan su..masha Allah! masha Allah!! shine Abinda mohd yafad'a Azuciyarsa sbd ganin baiwar nutsuwa,kyau , tarbiya da sanyin hali Atattare da yasmeen "yatabbar da cewa tafi suhan komai"Abinda kawai suhan tafita dashi shine" wayewa da ilimin boko me zurfi...sannunku da zuwa"ta fad'a da k'yar cikin fargaba"sbd gaba d'aya wanda ta fahimci shine mijin nata taji yacika wajen" yauwa Amarya ya gida?"Alhamdulillah" Ina yininku?"lafiya qlau mohd ya Amsa da fara'a saman fuskarsa"yana d'aukar kwanon furan ya sha ya Ajiye"yasmeen kanta na'a k'asa "uban gayyar kuwa danna waya kawai yakeyi kamar besan da zamanta a soron ba"sbd ko gaisuwar data musu mohd ne kawai ya Amsa "yasha Alwashin muddin bazata gaishesaba su kwana Anan bazai tanka taba.... yasmeen! baby nah sarah tana gaidaki"Ina Amsawa sosai"to Alhamdulillah "sunana mohd b salis" nine babban Amini kuma d'an uwa ga mijinki sadeeq "Ina fatan kinyi murna da zuwan mu"sannan zakiyi Alfahari da Abokinah daya kasance Amatsayin miji Agareki"d'an murmushi kawai tayi tama kasa d'ago kanta balle tayi masa mgn"ya d'an girgiza kansa, sbd ya lura tanada kunya sosai" masha Allah! bara naje daga waje na kaima driver

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login