Showing 18001 words to 21000 words out of 85260 words
sbd ranta yabata kallonta yakeyi"hannunta ta saka ta goge hawayenta tana tashi zaune sai kallon k'ofar fita takeyi"wani irin b'acin rai da tsanarsa ne Aranta"tana tunanin yamata mugunta kashi na farko ta hak'ura"yamata na biyu ma ta hak'ura "saidai bazata hak'ura akashi na ukku ba.....K! banza ta masa ko motsi batayi ba"baki jine?" naji kace K "ni kuma ba sunana K ba"da K naga damar kiranki kuma dole ki Amsa"batace komai ba ta mik'e tsaye sbd bataga Amfanin zama tare da mak'iyintaba"dawo ki zauna"kayi hak'uri kaina ke ciwo kuma lokacin sallah yakusanyi"tana fad'in hakan da gudu ta nufi k'ofar ta bud'e ta fita batare data rufeba sbd ganin yabiyota...kinsan Allah koki tsaya konayi k'asa k'asa dake"yafad'a yana daga bayanta.....saidai yayi turus sbd hango mohd da sarah da zarah zaune a cikin parlourn suna fira"yasmeen kuwa murmushi ta k'ak'aro tana murnan ganinsu"mohd kuwa tunda yaga ta sakko Aguje kuma Lamid'o yabiyota ya fahimci wata muguntar zai mata"cikin second 5 yak'are mata kallo ya fahimci taci kuka sbd kumburin da idanuwanta sukayi"ga y'ar rama datayi"yaya mohd Ina wuni?"ta fad'a tana russinawa ya Amsa cikin tausayinta"ta kalli sarah tana fad'in k'awata koki kamasa ruwa?"na bari ki fito ne shiyasa"yasmeen batace komai ba tana murmushi ta wuce kitchen"mohd na bin sadeeq da kallon tuhuma bece komai ba"shi kuma yatab'e baki yana Ida sakkowa k'asan "sarah fuska bbu yabo bbu fallasa ta gaidashi ya Amsa da k'yar yana fad'in Abokinah saukar yaushe?"yanzun bamu jimaba"ya bak'uwa?"yi yayi kamar beji shiba "Adaidai nan yasmeen ta dawo parlourn rik'e da tray data zubo musu drinks da dubulan da cincin da nakiya"sannunki Amarya "d'an murmushi tayi ta zauna tana kallon zqrah tace"Ina farooq?"tafiya yayi nima bara naje"dato ta Amsa "gaba d'aya ta kasa sakewa sbd ganin yana wajen"shi kuwa tunda ya zauna beyi mgn ba ya daure fuska yana danne danne Awaya "mohd kuwa yanata ciye ciyensa yana jan yasmeen da sarah da fira"agundure sadeeq ya mik'e tsaye yana fad'in mlm katashi muje masallaci in kuma nabarka kayi surutun to"yafad'a yana nufar k'ofa"mohd be tanka shiba ya mik'e tsaye yabiyo bayansa"suna fitowa yace"Lamid'o kenan! koban tambayi yasmeen ba yanayinta kawai ya nuna kana wahalar da ita"ka sani kome zaka mata muddin bata yafe maka ba sai Allah ya tambayeka"ada nace bazan koma yimaka zancen taba" saidai naga Abin naka yayi yawa"shin baka tunanin ta sanarwa mahaifinta kosu Abba?"ko kuma zarah dake lura da komai tasanarma mama"duk bama wannan ba,idan Akayima k'anwarka haka zakaji dad'i?"Ina baka shawara da kaji tsoron Allah" to wlh bari kaji!kaga dai sarah nakeso kuma nake muradin Aure?"idan yanzun daddy ya Auramun mace kamar yasmeen wlh bazan damuba"miye laifinta dan Allah??"k'in mgn sadeeq yayi har suka iso bakin get"mohd yatab'e baki Aransa yace"Akwai ranar nadama me Amfani ko marar Amfani....har suka shiga masjeed sukayi sallah suka fito mohd be koma masa zancen yasmeen ba saima zancen bilal lamis da sukeyi har suka iso side d'in "tun kafin su shigo k'amshin girki ke dukan hancinsu"sadeeq yatab'e baki ransa na bashi sarah ce ke girkin yasan yasmeen ba wani iya girki tayiba"ko sarah d'in ma yafi k'arfin yaci girkinta"yana wannan tunanin mohd yace"nifa basai na komaba bara na kirata ta fito mu wuce"okay kawai sadeeq yafad'a yana d'an murmushi me tattare da ma'anoni masu yawa yace"meya hana Asaka muku rana da ita?"babu "saidai soon za'a sanya"dukda nasan lokacin bikina kai kazama daddy"d'aure fuska Lamid'o yayi yana fad'in dakata pls"tsarin yara 3 nake dasu kuma suhan ce zata haifamun I n sha Allah "sbd haka kabari saina Aureta sannan kace nakusan zama daddyn"okay lokaci zai nuna hakan"daga haka mohd yafara k'ok'arin kiran sarah da suke kitchen suna Aiki tana bama yasmeen shawaran ta zage damtse wajen k'irsa da kisisinah da d'aukar gayu ta k'wato y'ancinta"kuma ta dena nuna masa tsoro"itadai yasmeen jinta kawai takeyi"ita kawai tasan yatakeji ko ganinsa Ida tayi"idan kuwa ta had'a Ido dashi daburcewa takeyi....tana kallon yadda sarah keta zuba ma mohd shagwab'a data d'aga wayar"sai taji sunyi ba'in burgeta"bayan ta idar ta kashe wayar tana fad'in zamu wuce"insha Allah sai mun had'u a skul"to shikenan nagode muje na taka miki tunda kin rantse bazaki tsaya kici girkin ba"ta k'are maganar suna fita daga cikin kitchen d'in.....bayan tadawo ta Ida girkinta"dama sarah ta koya mata yadda Ake Amfani da gas cooker wajen kunnawa da kashewa "sai bayan sallar la'asar ta gama girkin"batayi gigin fitarma da sadeeq Lamid'o ba"saidai ta fidda wanda zata kai cikin gidan"tana gama goge kitchen d'in taje tayi wanka da sallar la'asar ta shirya cikin riga da siket na lace white & golden ta yafa k'aramin veil golden ta zauna a parlourn tana cin Abinci....ko mintina 5 batayiba sadeeq ya sakko k'asan yasha gayunsa cikin k'ananun kayan da sukayi masifar yimasa kyau"yanata zabga k'amshi na musammun, fuskarsa Ad'aure ya wuce"kallon second 5 yasmeen ta masa tana fad'in Masha Allah"Ahankali tace "dan Allah zanje cikin gida"kamar bazai tankaba har yakai bakin k'ofa yace"rayuwarki ce kiyi yadda kikaso banida damuwa"yana fad'in hakan yasaka kai yafita"ta girgiza kanta kawai"bayan ta gama cin Abincin ta zuba komai a basket ta d'akko mayafin dayayi shige da kayan ta yafa Ajikinta "sosai tayi kyau da haske"saidai fuskarta bbu walwala "key d'in dake jikin k'ofar tasaka ta rufe k'ofar shiga side d'in kafin ta nufi side d'in su mama....✍️
wannan book d'in na kudine ! idan kina buk'atar siya serious regular grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
2/26/24, 14:08 - Ummu: *Littafin kud'i ne!*
.......mama dasu zarah da Anty na zaune a main parlour sai wasu bak'i da suka zo yi musu Allah yasa Alkhairi na hidimar da Akayi"Ahaka yasmeen ta shigo cikin parlourn da sallama kanta na'a sunkuye"duk suka kalleta da murmushi suna Amsawa,zarah ta mik'e tsaye da nufin taje ta Amshi basket d'in dake hannunta"farooq yayi wuf yaje Aguje ya rungume yasmeen yana dariya"bayan ta bama zarah basket d'in ta iso kan carpet ta zauna ta gaishesu"mama nata satar kallonta ta Amsa"hakama Anty "su moon da Amira ma suka gaida ita"sai godiya mama ke mata"ita dai kanta na'a k'asa tayi shiru tana tunanin inama ace yadda iyayensa suke da kirki shima haka yake....Anty yasmeen tashi muje ciki"cewar zarah"babu musu yasmeen ta mik'e tsaye tabita d'akin mama suka zauna suna d'an tab'a fira"mama ta shigo cikin d'akin ta zauna"hakan yasa zarah ta fita.....kiyi hak'uri dan Allah yasmeen da rashin hankalin dasu hafsat suka miki jiya...lahh babu komai mama ya wuce"madallah Allah yayi muku Albarka Ina fatan babu dai wata matsala ko?"in kuma Akwai dan Allah kisanarmun"tana d'an murmushi tace"babu komai wlh "to Alhamdulillah Abbanku yacemun Angama komai zuwa monday driver zai fara kaiki skul"Allah yabada sa'a "ki kula da kanki da mutuncinki dan Allah"tana mamaki ta Amsa da in sha Allah "wato inda bata zoba sadeeq bazai sanar mata monday zata fara zuwa skul ba kenan?"Anya mutumin nan zai canza kuwa?"ta fad'a Aranta"to yasmeen yaya batun me Aiki yarinya ko dattijuwa kikeso a d'aukar miki??"da sauri tace"ah ah mama Aikin ma beda yawa zan dingayi da kaina kawai"wanda tayi hakanne sbd tasan sadeeq bazai bari tayi me Aiki ba....duk yadda maman taso suyi fira yasmeen ta kasa sakin jikinta"lura da tana jin kunyarta yasaka tabaro d'akin"zarah tadawo suka kama fira"sai gab da sallar magrib yasmeen ta dawo sashen"tana idar da sallar magrib tayi zamanta tana chats ta rufe k'ofar d'akinta da key sbd karma sadeeq ya shigo yamata muguntar daya saba.......washe gari tunda ta idar da sallar Asuba taje ta gyara sashensa cikin taka tsantsan sbd kar tayi kuskure"sai Akayi sa'a baya nan"bayan ta gama tadawo tana gyara main parlour "Ahaka sadeeq d'in ya shigo da farar jallabiya Ajikinsa da Alama daga masallaci yake"kallo be ishetaba sbd tasha Alwashin ta gama gaidashi tunda baya Amsawa"wucewa yayi ya haye upstairs d'in"komai ya gansa very need"babu wanda zai kushe gyaran datayi sbd gyaran yayi"Amma dayake son k'untata mata yakeyi musammun da yaga tak'i tankashi saiya sakko k'asan yasamu bata cikin parlourn "saidai ko Ina nata k'amshin turarukan wuta da air frishners , kitchen ya lek'a yaga bata ciki"ransa yabashi tana d'aya daga cikin d'akunan baccinta"hakan yasa ya nufi guda daga ciki"babu sallama balle knocking yatura k'ofar ya shigo"yasmeen na tsaye gaban mirror d'aure da guntun farin towel da iya karsa rabin cinya"tana rik'e da cum tana taje gashin kanta daya sakko har gadon bayanta "tasaka wayarta hands free tana waya da baba sai shagwab'a takeyi tana kuma taje gashin....sam bataji motsin shigowarsa ba, tanata hidimar gabanta kamar ita kad'aice cikin d'akin "can baba yace"yaya sadeeq d'in da fatan kuna zaune lafiya dashi ko??"lafiya qlau yake baba"to Alhamdulillah kiyita dai masa biyayya dan Allah yasmeen "banda gaddama kina jina?"to baba in sha Allah....tunda ya shigo yafara yin Arba da bayanta yaji fad'uwar gaba" da sauri ya kawar da kansa gefe"lokacin da yaji tanata shagwab'a da tambayar da baba yamata tabashi Amsa yayi mamakin meyasa bata sanar masa da irin muguntar dayake mata ba?saidai har lokacin zuciyarsa nasanar masa ba gashinta bane attached ne"ganin zata juyo yasaka da sauri yafita batare daya rufe k'ofar ba"yasmeen kuwa tana gama wayar ta daure gashin kanta"saidai tana juyowa taga k'ofar Abud'e "da mamaki ta kalli k'ofar sbd tasan itadai data shigo ta rufe k'ofar"bata kuma zaton sadeeq dayakeji da girman kai zai iya shigowa cikin d'akin "sai kawai ta basar sbd batason zurfafa bincike Aranta"rufe k'ofar da key taje tayi sannan ta shige wanka"bayan ta fito ta shirya cikin bak'ar jallabiya me Adon stones ta yane kanta da mayafin"sai tayi kamar bak'ar balarabiya....lolx"d'akin ta d'an gyara sannan ta fito da nufin ta shiga kitchen ta sami sadeeq kwance saman kujera 3 seeter da jallabiyar d'azun Ajikinsa"ya lumshe kyawawan idanuwansa yyi matashin kai da hannayensa"kallon second 3 ta masa ta d'auke kanta zata wuce kitchen Farooq yaturo k'ofar yashigo da wani exercise book Ahannunsa"ihu yasaki yaje yayi hugging nata tasaki murmushi tana fad'in islamiya zakaje?"s d ganinsa da yonifoam Ajiki"Eh Ina kwana Anty yasmeen?"lafiya qlau "dama Assignment zaki mun guda biyu ne kuma yah sayyadi yace"idan ba'a mana ba zai dokeni pls kimun"to shikenan Amma bazaka makara ba?"sai k'arfe 8 muke shiga ajifa "kuma mama yanzun da zata tafi wajen Aiki tace k'arfe bakwai da rabi yanzun"batace komai ba ta zauna kan carpet tana duba book d'in "Anty yasmeen yah sayyadi yace"misali guda biyar zamu rubuta na nunisakinah da tanwini"kuma kinga harrufan nan yace" duk idan muka rubuta muja musu layi"to shikenan bara na rubuta maka a wata paper saika kwafa ko?"yauwa Anty yasmeen daga yanzun zan dinga kawo duk wani Assignment kinamun ko koyamun hadda na hadisi"idan na cewa Anty zarah ta mun batayi"murmushi tayi batace komai tana yagar paper tafara rubuta masa"tana gamawa tace"maza ka kwafa Anan saika tafi karka makara"tana fad'in hakan ta tashi tsaye ta wuce kitchen"duk zatonta sadeeq bacci yakeyi"Ashe idonsa biyu tun bayan yabar d'akinta yaje yayi exercise shine yadawo nan ya kwanta ya huta kafin yaje yayi wanka"duk Abinda yafaru tsakaninta da farooq yanaji"kasancewar week end ne ba office zai fitaba shiyasa yayi kwance yak'i tashi har farooq yagama kwafa yamik'e tsaye yafita da gudu batare daya lura da sadeeq na kwance a parlourn ba"shi kuwa k'amshin girkintane yafara kai masa ziyara"yaja tsaki ya tashi zaune yana duba time 7:48 p
am"Ahaka yasmeen ta fito daga cikin kitchen d'in tana rik'e da plate da cup d'in tea"saidai tana ganinsa da sauri tayi baya batare data yadda ta kalli cikin Idanuwan saba"shi kuwa doguwar tsuka yaja"sbd ganin ta koma cikin kitchen d'in"Aikin banza kawai"shine Abinda yafad'a yatashi ya wuce saman"yasmeen kuwa a kitchen d'in ta zauna tayi break fast d'in "bayan ta gama ta wanke Abinda ta b'ata tayi tafiyarta d'akinta tayi kwanciyarta bacci me dad'i yayi Awon gaba da ita......
kimanin kwanan yasmeen biyar kenan Agidan"tana iya bakin k'ok'arin ta wajen gyara sashensu da tarban duk wanda zaizo ka musu ziyara cikin mutunci"yayinda zarah da farooq sun zama y'an gidanta ta shak'u dasu Acikin kwana biyar kacal"gefen sadeeq Lamid'o kuwa babu ruwanta dashi"kullum da safe zata gyara masa part d'insa "idan yashigo waje tana agurin kallo be ishetaba zata tashi tabar masa wajen"yana jin zafin Abin Aransa yasha Alwashin zaiyi maganinta"sbd Aganinsa rainine yasaka take masa hakan"jiya da yau ta fara zuwa skul dukda ba course d'aya suke da sarah ba Amma idan basuda lactures tana zuwa"kuma face mask duk tasaka"iya zuwan datayi sau biyu taga Abubuwan k'aruwa ga rayuwarta fiye da tunanin me tunani"sbd mutanan data gani kala kala"masu tarbiya da mararsa tarbiya "masu mutunci da mararsa mutunci"babban Abinda yafi burgeta ga wasu y'an matan shine iya d'aukar dressing"da yadda zakaji mace ta wuce k'amshi ya zauna Ajikinta"sai yanzun ta fahimci irin shawarwarin sarah da lami da suke bata"badai sbd sadeeq yaganta hakaba yake ganin bata kai mace ba"in sha Allah zata nuna masa d'an hakkin daka raina shike tsone maka ido.....da yamma taci kwalliyar da tunda take bata tab'a yin irintaba"riga da wondone maroon calour na kanti Ajikinta da maroon d'in veil"sai jambaki maroon data shafa"ba k'aramin kyau yasmeen tayiba kamarma ba itaba"sai k'amshin turaruka masu dad'i jikinta keyi"ita kanta yau jinta takeyi kamar ba itaba"sbd yanzun duk kayan cikin lefenta tafara Amfani dasu,irinsu soap,body cream ,body sprays da sauransu da k'ananun kaya" suna zaune itada farooq tana koya masa haddan wani hadisi"sadeeq ya shigo cikin parlourn"sallamarsa kawai dayayi ciki ciki ta Amsa daga haka ta nuna kamar Allah be ajiyeshi Awajen ba"dukda bata yadda ta kalli fuskar saba saidai ta kalli bayansa daya wuce"saima mik'ewa tsaye tayi tana fad'in farooq tashi muje daga ciki....K! banza ta masa kamarma badashi dake ba"saima k'ok'arin kama hannun farooq datayi da nufin subar parlourn.....kai farooq! wuce kaje cikin gida" dan Allah yaya hadda Anty yasmeen zata koyamun....kallonsa kawai yayi da mayatattun idanuwansa da sauri yazare hannunsa dg cikin na yasmeen yanufi k'ofa"sosai yasmeen taji haushi"saita juyo da nufin ta gallah masa harara"Atake idanuwanta suka shige cikin nata"da farko shi yama d'auka ba ita bace sbd canzawar dayaga ta masa"Amma dayake d'an duniyane saiya had'e rai yana zare mata Ido yace"nike kiranki kinaji kikamun banza??"ta janye idanuwanta tana b'ata fuska tace"kaifa kace nayi rayuwata kuma nadena tankaka"kinamun tunine ko kuwa gayan mgn kikeyi?"nidai dan Allah ka kira zarah kace farooq d'in yadawo"mitsssssuww! Ina miki mgn kinamun wata mgn ko?"ba cewa nayi kizo ba"batace komai ba ta iso gefensa ta zauna kan kujerah nesa dashi tana fad'in gani "da mamaki Aransa yace"yaushe yarinyar nan ta waye ne?"saiya kalleta murya Akausashe yace"sakko k'asa kimun tausa nagaji"wayyo Allah yaya sadeeq ni ban iyaba"kuma banaso hannuna yatab'a ji....kallon daya Aiko mata dashi yana jan tsaki yasaka tak'i k'arasawa"saiya mik'e tsaye zai nufota"k'ara ta saki tana fad'in wlh zanyi karta taso pls"yaja tsaki yana fad'in matsoraciyar banza"yak'are maganar yana zare takalminsa sawu ciki ya kwanta kan 3seeter a gefen dama yana fad'in Allah yasa bakida kaushi ga hannu"k'afafuwana zaki jamun kimun tausa sbd nagaji"saidai kika sake kika kallemun jiki saikin sani"batayi mgn ba gabanta na fad'uwa tana jin tsoron tab'a shi"jin shirun yayi yawa bata faraba yasaka ya juyo ya kalleta tana duk'e gabansa"yaya sadeeq dan Allah kayi hak'uri kasani wani Aikin banda wannan"hmm! tunda na b'ata lokacinah na miki mgn confirm kiyi yadda nakeso"kinma Isa na lallab'a kine"matan wajema sunamun biyayya idan nabasu umarni balle ke matar Aurenah oya ki fara ko ranki yab'aci"bayan ma wannan dalilin kinada aji ko matsayin tab'amun jiki ne"batace komai saidai kalamansa ba k'aramin zafi suka mata ba"ta daure ta matso tana bin k'afafuwan nasa da kallo sbd ganinsu jajir kamar na jinjiri wanda baya taka k'asa"daga sama k'afafuwan duk gargasan gashi "d'an murmushi tayi sbd itama ta shirya muguntar da zata masa"Aza hannuwanta tayi saman k'afafuwan "tayi d'an sama dasu ta zauna ta Azasu saman cinyoyinta tafara jamasa yatsun k'afar"wani iri sadeeq yaji ya rintse idanuwansa babu shiri"beyi tunanin tafin hannunta zaiyi laushi har haka ba"be gama wannan tunanin ba yaji tana ja masa b'akin gashin dake saman fatarsa da k'arfi"Aransa yayi murmushi yana fad'in nafiki mugunta yarinya"bud'e idanuwansa yayi da nufin yamata mgn aka turo k'ofar"yasmeen ta kalli k'ofar"wasu gogaggun y'an mata ne guda biyu"gudar datafi isgili itace Agaba tana bin parlourn da wani irin k'ask'antaccen kallo irin na raini"sai kuma suka had'a Ido"Atare gabansu ya fad'i "tana bin yasmeen da wani irin kallo take fad'in sweet heart mena ke gani haka?"gaban sadeeq yafad'i sbd jin muryar suhan"kafin yajuyo ya kallesu ta iso gabansu afusace cikin zafin kishi da bacin rai tana fad'in me k'afafuwanka keyi saman cinyar wannan banzar y'ar gidan matsiyatan?? da wani irin mamaki yasmeen ta d'ago kanta tana kallonta zuciyarta na sanar mata wannan itace suhan d'in jinta yafi ganinta"kallon second 5 yasmeen ta mata"tana sanye da doguwar riga ta kanti wacce ta bayyana shape d'in k'irjinta "ta yane kanta da siririn mayafi ana iya ganin gashin kanta"tanata taunar chiweengum da wayarta iphone 14 a hannunta sai takalminta masu masifar tsini a k'afarta"jikinta na fitar da wani irin shegen k'amshi"duk yasmeen ta mata wannan kallon ne cikin second 5"yayinda feedyn data zugota sukazo ta toge daga nesa"sadeeq kuwa tunda yake da suhan bata tab'a kaisa bango irin yauba"miye ribarta na zuwa nan? idan Abba ko mama suka san tazo har wani abu marar kyau yafaru miye zai ce sbd yakare kansa??"bance ki kulataba ki cigaba da Abinda nasaki"shine Abinda yafad'i murya bbu Alamar wasa "yasmeen batayi mgn ba ta cigaba da Abinda takeyi"sadeeq ni zaka nunama wannan y'ar iskan tafini mutunci awajenka?"meye take baka dani na kasa baka?ke dan kutumar ubanki tashi daga nan kona miki shegen dukan dana sabar taki.....wa'iyazubillahi! a'ubillahi mina shaid'anun rajim!" y'ar gidan k'aruna zagi da rashin iya mgn naki iyayen suka koyar dake ne?"zan iya jure komai Amma banda cin zarafin iyayena"bandamu da sanin ko wacece ke Awajensaba !saidai inaso kisani ita rashin tarbiya babban dafice duk inda mutum yaje saiya nuna....ke banza kin Isa ki nunamun yadda zanyi ne? sadeeq cikin tsananin bacin rai ya mik'e tsaye da wani irin mugun sauri ya wuce upstairs....kinga zomu wuce sakkowar wannan me bak'in halin ba Alkhairi bane"cewar feedyn tana nufar k'ofa"suhan