Showing 57001 words to 60000 words out of 85260 words

Chapter 20 - _NIDA_BARRISTER_SADEEQ_Complete

04 Apr 2025

7432

da haiba yake furta meyasa kin kasa ki manta da Abinda yafaru Abaya yasmeen?kinma duba sak'on dake cikin ladar d'azun?duk yana maganar ne idanuwansa nakan kyakykyawar fuskarta"girgiza kanta tayi batare data kallesaba ta janye hannayenta da yake k'ok'arin sark'ewa da nasa....meyasa?" bana buk'ata ne"rabin ranka,kuma muradin ranka itace yaka mata ka bamawa bani ba y'ar k'auye"wacce kake ikrarin har Abada bazaka tab'a sonaba!....kafin ta rufe baki suhan ta turo k'ofar da k'arfi bbu ko sallama ta danno kanta cikin d'akin......✍️

wannan book d'in na kudine ! idan kina buk'atar siya serious regular grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK

Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
2/26/24, 14:09 - Ummu: ❤‍? *NIDA BARRISTER SADEEQ*❤‍?

*49&50*




*Littafin kud'i ne!*
....... tsintar kansa sadeeq Lamid'o yayi dajin fad'uwar gaba sbd ransa yabashi yasmeen ce ta turo k'ofar "yayinda suhan sarai tasan itace sbd dama kan idon yasmeen ta shigo d'akin cikin izgili"kwantar da kanta tayi Abayansa"yaja tsaki yana tureta daga jikinsa ya juya ya kalli k'ofar"saidai tuni yasmeen tabar wajen ta nufi kitchen cikin tsananin zafin kishi da b'acin rai "dukda tasan suhan tafi laifi"Amma meyasa be kore taba har yabari ta rungumesa?"gaba d'aya ta rasa meke mata dad'i?"saidai tayi k'ok'arin danne damuwarta tana Aikinta "tana jin wani mik'i daya taso mata a mak'ogwaro" duk idan ta tuna yadda ta tura k'ofar ta gansu tsaye suhan ta rungumesa sai taji wani irin rad'ad'i Azuciyarta"tayi dana sanin shiga d'akin bbu Adadi"dama sbd taji shiru bata fitoba taji barata iya jurewa ba shine ta shiga taga meye yasaka suhan zama d'akin? bayan ba kwananta bane"saidai tasha Alwashin bashi suhan ta d'auka Akwai ranar biya ,ba kuma yanzun ba daga shi har ita daya bama dama zasu gane kuransu..... sadeeq kuwa daya fahimci yasmeen ta gansu Amma batace komai ba tayi tafiyarta sai yaga be mata Adalciba"yaji kuma ta burgesa ta shiga ransa sosai"ya tabbar da suhan ce sai Anyi tashin hankali da ita...nifa gaskiya Ina buk'atar ka sweet heart! ta fad'a cikin jan hankali badan kuma hakane Aranta ba saidan sbd ta k'untatama yasmeen ta fad'i hakan "tsaki sadeeq yaja ya juyo suka had'a Ido"da hannu yanuna mata k'ofa yana fad'in bana buk'atar ganinki Anan "na lura dole ki koma islamiya sbd kisan Abinda musulunci yayi hani Ayi da wanda yayi hani Adena"koda yasmeen ta Amince na kwanta dake ranar kwananta bazan Amince ba sbd haka get out"korata kakeyi?"Eh sbd hankalinki ya kwanta husumar dakika so ki tayar tokin tayar"karki d'aukeni bansan meye nakeyiba"kokin manta rule of law na karanta ne?"ni baki Isa kimun wani kina yar banzaba "shi kansa hak'urin badan Allah kikazo bayar dashiba"me kake nufi?"ban saniba"daga yau idan zaki shigo d'akina nasanar miki saida izinina koda kece da girki"yana fad'in hakan yanufi gefen bed ya d'auki jallabiyar jikinsa yazura"suhan kuwa baki sab'ule ta fita tana mamakin ta yaya sadeeq ya ganota da sauri haka??"shima fitowa yayi yana k'arema parlourn kallo ko Ina k'al very need "saidai be ganta a parlourn ba"sai k'amshin girkinta da yaji"hakan ya tabbar masa da cewa tana kitchen,hakan yasa ya nufi kitchen d'in Anutse "tana tsaye gaban gas cooker tana rik'e da frifan tana juya pepper chicken"yayi tsaye bakin k'ofar kitchen d'in ya rungume hannayensa a k'irji yana Aikin kallonta tun daga saman dogon farin wuyanta dake sumul har zuwa diga digan k'afafuwanta"yasak'i d'an guntun murmushi Aransa yace"my princess coka cola shape ne da ita"kasancewar ta bada baya shiyasa be kalli fuskartaba balle yagane taji haushin Abinda yafaru ko kuwa??.... k'amshin mayataccen turarensa da yasmeen taji ya tonasa"da sauri ta juyo ta kalli k'ofar suka had'a Ido"d'auke kanta tayi da sauri"yak'araso yana fad'in my princess sannu da Aiki"irin wannan zazzafan girki k'amshi yacika ko Ina"yak'are maganar yana matsowa zai rungumeta....karka tab'ani dan girman Allah da monzonsa! Akanme yasmeen?"Akan banaso"idan kuwa kata b'ani zanyiwa kaina illah"ta fad'a tana cigaba da Aikinta"tamkar yace"to kiyima kanki illar mana"saidai yakasa furta komai jikinsa na basa sbd ta gansu da suhan ne"idan kuwa hakane tafara kishinsa kenan?"kiyi hak'uri yasmeen dan Allah! wlh ni banida laifi"kawai ta shigo zan....dama nace maka wani abu ne?"pls mlm dan Allah ka k'yaleni kaje abunka"bece komai ba yajuya yafita ransa Ab'ace sbd Abinda take masa yafara isarsa Aganinsa "kodan sbd yadamu da ita take masa hakane wai?"zai fita harkansu daga ita har suhan d'in sai wata tsiya"Atake yahau dokin zuciya yatun zura....ko break fast be yiba yana shiryawa yabar gidan"da dama yau wasu daga cikin mutanan dayake mu'amala dasu sun fahimci yana cikin bad mood"yasmeen kuwa ko Ajikinta da fushinsa "tama d'auka suhan zatazo suyi fitinah har shiryama zuwan nata tayi Amma tajita tsit bata zoba"hakan yasa tana idar da sallar Azahar ta wuce part d'in su mama, gashi gobe monday.....sai yamma tadawo gidan "tana turo k'ofar gabanta yafad'i sbd hango sadeeq datayi zaune a parlourn ya mik'e k'afa"yana sanye da k'ananun kaya t shirt da wondo 3 quarter "bata yadda ta kallesaba ta nufi bakin k'ofar d'akin baccinta....daga Ina kike?"taji Amon jarumar muryansa Abayanta"batare data juyo ba tace"sashen su mama mana"da izinin wa kikaje?"Amma dai kasan Ai Ina zuwa ko?"ban saniba"wai mekika maidani ne yasmeen?"wlh ki shiga hankalinki dani zan had'aki da baba"shikenan zanfi buk'atar hakan"tana gama mgn ta bud'e k'ofar ta shiga ta maida key ta rufe"shi kuwa girgiza kansa yayi yadai fad'ane Amma bazai iya had'ata da baban taba.....Adaren ranar d'akinsa ya kwana sbd yasmeen ta rufe masa k'ofa"tun daga lokacin yafita harkansu daga ita har suhan d'in sbd ya fahimci gwale gwale kawai suke masa Agidan"ga suhan data kafe zata fara zuwa Aiki A wannan satin yace" ta bari sai sati na sama Amma tak'i ji ta fara zuwa"ya kuma zuba mata Ido yabarta da zunubinta"idan ta fita daga nan tana y'an biye biyen gidan k'awaye da gidansu da wajejen shak'atawa "musty suna waya bbu yadda beyi da itaba kan suyi mahad'a ta bashi had'in kai ita kuma tak'i yadda sbd tsoron kar sadeeq yagane.... yasmeen kuwa daga shi har suhan d'in babu ruwanta dasu"garama da safe idan sun had'u tana gaishesa ya Amsa da k'yar"Amma ko itace keda girki bata zuwa d'akinsa balle ta gyara sbd rufewa yakeyi"saidai kullum break fast da lunch nata yake ci koda ba itace keda girki ba"tunda suhan ta fahimci kamar sun tsani juna sai tadawo shigema sadeeq musammun idan ta lura da yasmeen na'a wajen "shi kuma ya dinga dizgata"bayan yafita yasmeen tayita dariya tana yada mata mgn idan zata wuce....haka suka d'auki lokaci kusan sati ukku suna irin wannan zaman"sadeeq yayi rama ya Ajiye uwar k'asumba data cike masa fuska yak'i gyarawa"kullum fuska Ad'aure cikin b'akin rai yake"tun abun baya damun yasmeen har yafara damunta ta fara tunanin bata kyautaba" karma taje ta sami zunubi "saidai ko yaya tayi niyar tun kararsa kwarjininsa ke hanawa koda mgn ta masa"mohd yana lura dashi Amma yazuba masa Ido tunda yak'i sanar masa damuwarsa"gashi saura bikinsu da sarah befi saura wata biyu ba"ransa yabashi sbd matansa ne yasaka kansa damuwa"wanda duk sha'awa ce tasaka yayi rama"kullum da sha'awar yasmeen yake kwana yake tashi"dan yanzun suhan gaba d'aya bayajin wata sha'awarta"idan itace keda girki tazo jikinsa tana iyayi zai tureta yaja tsaki"sbd daya tuna Allah ya Isan data masa sai yaji zafi Azuciyarsa..... Ayau friday da yamma yasmeen na zaune a parlourn wanda yau itace da sadeeq har girki ta gama bayan ta dawo skul"tasha gayunta cikin k'ananun kaya "hannayenta sunsha jan lalle "tayi wani irin haske da shek'i had'e da y'ar k'iba"gaba d'aya cikin satin batajin dad'in jikinta"saidai ta d'aure ne kawai"tana zaune tana shan agwalima farooq da Amir yaron Anty salma suka shigo cikin parlourn "tayi murmushi suka zauna suka gaida ita"sai taga sun wuce sashen suhan"kamar tace"kar suje sai kuma ta k'yalesu"basufi mintina 10 ba suka sakko Aguje tana kallonsu tace"farooq lafiya?"basuyi mgn ba suka fita da gudu"saiga suhan itama ta sakko Azafafe tana fad'in dan kutumar ubanku kuna Ina?"ta k'are maganar tana y'an waige waige"yasmeen ta tab'e baki bata tankataba"data fahimci su farooq basu parlourn saita fita bbu ko mayafi"kai tsaye sashensu mama ta nufa"tunda tazo gidan bata tab'a zuwaba sai yau"zarah na zaune a babban parlourn gidan itada yaran suna sanar mata fashema suhan jug sukayi"ita kuma Aranta tace Allah ya k'ara "Afili kuma tana musu fad'an karsu koma zuwa sashenta"Ahaka suhan ta fad'o parlourn babu ko sallama"tana fad'in kai dan kutumar ubanku kun Isa kumin b'anna ku gudo?"kunsan ko nawa jug d'ina yake ne?"ta k'are maganar tana fisgo farooq tafara marinsa da masa k'ulli"ya saki ihu"kanzil zarah batace ba sbd taji dad'in hakan kodan kowa nasu yagane mugun halin suhan"cika farooq tayi yana ihu"kafin ta nufi wajen Amir dake k'ok'arin guduwa ta damk'osa tafara jibga"ihun su yasaka mama ta fito daga cikin kitchen tana fad'in wai zarah me kikema yaran nan ne?"shiru tayi sbd ganin suhan duk''e tana jibgar Amir tana zaginsa bbu mutunci"zarah ta kalli mama tana fad'in banice na dake suba"sunje sun fashe mata jug kamar yadda sukace shine ta biyosu ta daka"da wani irin mugun mamaki da Al'ajabi mama ke kallon suhan"wacce sarai ta lura da ita bata kuma fasa dukan Amir da zagin saba"cikin b'acin rai mama tace"K marar kunyar banza cikasa kije kibama mutane waje"ta cikasa tana tab'e baki tace"nasan dama laifina zaki gani bayan ga masu laifi nan"ko gaban sadeeq suka min saina dake su...ke banza !y'ar iska kin Isa ki gayama mahaifiyata mgn Ina zaune?"cewar zarah tana mik'ewa tsaye "kinga ki barta duniya ce"kuma lafiya qlau zata zauna bbu Abinda sadeeq zai mata sbd faruwar hakan "suhan ta tab'e baki ta juya ta fita"zarah ta shige bed room ta fara k'ok'arin kiran sadeeq Lamid'o.....
Afannin sadeeq Lamid'o kuwa har shari'a suka shiga yau bayan sallar Azahar me matuk'ar mahinmanci "Amma Abin mamaki yakasa nutsuwa yayi tambayoyi ko kare wanda ya shigar mawa yadda yaka mata"hakan yasaka Alk'alin cewa An d'aga shari'ar sai bayan kwana 2 Azauna"sbd shi kansa ya fahimci sadeeq nada damuwa"kuma idan yace Ahaka za'a fafata da wuya Ayi nassara"gashi kuma b'aro b'aro wanda yake k'arewa shine da gaskiya"kasancewar mohd na wajen yafahimci damuwar sadeeq ta wuce ak'yalesa sai kawai yabiyosa suka shigo motarsa"driver zai shigo mohd yadakatar dashi kan yabasu waje suyi mgn "shidai sadeeq na zaune yana kallonsa beyi mgn ba"kimanin shud'ewar mintina 3 mohd yayi gyaran murya yana fad'in wace irin matsalace ke damunka har tana k'ok'arin katangeka wajen Aiki??"najima da fahimtar kanada damuwa Amma zurfin ciki da zuciya yasaka kak'i fad'amun ko?"yayi shiru kamar bazai tankaba"sai kuma Ahankali yace"yasmeen ce! ita kad'aice damuwata Abokinah "wlh nayi nadama pls ka taimakamun nashawo kan yasmeen"wlh mohd yanzun yasmeen batada mak'iyin daya fini"daga ita har suhan wahalar da zuciyata kawai sukeyi"nayi fushin har nagaji Amma sunk'i su dena.....ni nama d'auka suhan zakace?"sbd nasan dai yasmeen ba wata tsiya bace A wajenka"miye Amfanin kadamu dan tana k'ink'a?"yafad'a yana danne dariyarsa"dama tuni yafahimci yafara son yasmeen,ga suhan na bashi ciwon kai had'e da caza masa k'wak'walwa....wannan dalilin yasaka nak'i sanar maka da damuwata"bana son dawo da Abinda ya wuce baya mohd"kuskure na riga nayi"na kuma gane kuskurena"ina son matata yanzun har bansan Adadiba"suhan kuma na fahimci sha'awarta nakeyi da kuma burgeni datakeyi shiyasa na d'auka sonta nakeyi"bak'ak'en halayenta sun saka nayi saurin gane hakan"k'ilan data kyautatamun da bazan gane komai ba" Amma data nuna halayenta nagane"sannan na fahimci Abinda kake Ankarar dani kenan"kayi hak'uri mohd nasan kana hak'uri dani da halayena"duk idan natuna kwanaki sbd suhan naso na raba Alak'ar mu wlh nine kawai nasan yadda nakeji Azuciyata"kayi hak'uri ka yafemun"Ajiyar zuciya mohd ya sauke yace"bbu komai ni tuni komai ya wuce"saidai Lamid'o saka damuwa Aranka da fushi dasu konace fushi da yasmeen bashine mafitah ba"rarrashinta da bata kulawa da nuna mata soyayya shine zakayi"ba mamaki itama tana sonka"sbd nasan bbu macen da zata k'ika Abokinah"suhan kuma kaine kajama kanka sai kayi hak'uri kacigaba da zama da ita haka Allah yatsara maka "shiru kawai sadeeq yayi sbd beson yasanarwa mohd harda jahilcin rishin karatun Addini ke damunta"Aganinsa bbu dad'i wannan sirrin su ne"ko yasmeen suhan d'ince takaisa bango har yagaya mata mgn gabanta ta fahimci wacece ita.....yanzun muje muyi sallar la'asar kaje Ayi maka gyaran fuska muje gidan tare zanyiwa yasmeen d'in nasiha"da sauri yace to Abokinah godiya nake"shidai mohd kallonsa kawai yakeyi yana d'an murmushi sbd yabashi tausayi"dubi yadda duk ya zabge sbd mata sun sakoshi gaba ,ga kuma soyayya dake damunsa"dama tuni ya fahimci ba son suhan yakeyiba kawai sha'awarta yakeyi"gashi Aure wata guda da y'an kwanaki yamata irin wannan tsana....sai bayan sunyi sallah sannan yara kashi Aka masa Aski da gyaran fuska"sai tsokanarsa yakeyi wai yau Ango ne"sbd yasanar masa yauma yasmeen d'ince keda girki"shidai sadeeq jinsa kawai yakeyi k'ilanma koda ta gansu mohd d'in kawai zata kuka shi bandashi"yana wannan tunanin ya tsaya yasiya musu kilishi da tsire,ko wacce leda biyu aka mata"mohd na tsokanarsa yace"mata biyu kenan! dole mutum yayi Adalci koya shiga wuta"shidai sadeeq be tanka saba yana dai tunani"wai yasmeen har yanzun bata koma samun wani cikin ba?"idan nace Eh ko ah ah na maka k'arya Abokinah Amma idan nasamu ta sakko daga fushin datakeyi dani k'ilan nagane"wai itama d'in fushi takeyi dakai?"Eh mana"ya labarta masa musabbabin Abun "murmushi kawai mohd yayi sbd yagano itama dai yasmeen tana sonsa tunda tana kishinsa"suna a hanya zasu shigo get kiran zarah ya shigo cikin wayarsa"haka nan yaji k'irjinsa ya buga"fatansa Allah yasa ba suhan da yasmeen sukayi fad'a ba"mohd dake driving d'in yana lura da yanayinsa" cikin dakiya yad'aga yana fad'in meke faruwa ne?"zarah ta shiga kora masa bayani"bece komai ba harta idar ya yanke wayar yana furzan da zazzafan huci daga bakinsa "lokaci guda idanuwansa suka koma rik'ewa sukayi jajir"hakama red lips nasa ,ga jijiyoyin dake saman kansa sun tashi rad'o rad'o"b'acin ransa da suhan shine" ta tsaya tana fad'a mahaifiyarsa na fad'a"Amma dukan yara be damesa ba,dole ta gane shayi ruwane "shi kansa mohd ya tsorata da yanayinsa"kasancewar yaji komai Ahankali yace"kayi hak'uri bata kyautaba dataje har sashensu mama ta daki yara sbd rashin tarbiya"ka nutsu ka mata hukuncin daya dace karkayi Abu cikin fushi sadeeq"nasan mama batasan zarah ta kiraka ba ko?"kansa kawai ya gyad'a masa"suna shigowa cikin get d'in gidan tun kafin mohd ya gama parking sadeeq yabud'e k'ofar ya fito Azafafe"Adaidai lokacin wayarsa tayi ringing"yana dubawa yaga mama ce"hakan yasa ya d'auka cikin ladabi"kana Ina sadeeq?"gani nan bakin get"kazo nan Ina son mgn dakai bance kafara zuwa part d'in kuba"hasalima bansan zarah ta sanar makaba saida naji yanzun tana waya da salma"dato ya Amsa yakashe wayar "be cewa mohd komaiba ya wuce"shi kuma mohd ya d'akko ledojin yafito yanufi sashensu yasmeen"yana isowa yayi knocking"waye ne?"Abokin me gidan kuma mijin sarah in Allah yaso"yasmeen tayi d'an murmushi da sauri ta koma d'aki ta sako hijab tazo ta bud'e k'ofar tana fad'in gaskiya ka koma yaya mohd"inani Ina komawa yasmeen"kina neman ki haukatarmun da Aboki fisabilillahi "wannan zuwan naki nema gaba d'aya"gashi yace na wuto dashi , yad'an shiga sashens su mama"yak'are maganar yana Aza ledojin saman center table ya zauna"yasmeen ta zauna suka gaisa"kafin taje ta kamasa drinks da snacks"zataje kamasa Abinci yace"ki bari Abokinah yadawo zamuci tare"dato ta Amsa gabanta nata fad'uwa tazo ta zauna"saida yazuba lemo yasha kafin Anutse yace"yanada kyau yafiya da mance Abinda yafaru marar dad'i Arayuwa yasmeen "nasan tabbas Lamid'o Abaya yamiki rashin daidai saidai yayi nadama yanzun"kuma yana sonki yasmeen meyasa baza kiyi Amfani da damarkiba?"kijashi Ajiki ki zama tauraruwa a wajensa"gaba d'aya ya canza beda walwala sai yawan tunani duk sbd ke da irin Abinda suhan keyi na rashin daidai"shin so kikeyi saiya koma hararo wata yasmeen?"da sauri ta girgiza kanta hawaye na zubo mata "karkiyi kuka kiyi hak'uri dan Allah"ki manta da komai ki faranta ma sadeeq dan Allah "yamun complaine d'in kina nuna bakya sonsa pls yasmeen kibarsa Ahaka kinjiko?"kanta kawai ta gyada masa tana tunanin dama yana sonta shine yak'i sanar mata yake dogon fushi da ita??.... Ab'angaren sadeeq.....✍️

wannan book d'in na kudine ! idan kina buk'atar siya serious regular grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK

Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
2/26/24, 14:09 - Ummu: ❤‍? *NIDA BARRISTER SADEEQ*❤‍?

*51&52*




*Littafin kud'i ne!*
...... Ab'angaren sadeeq Lamid'o, tunda ya shigo parlourn da sallama can ciki mama ta kallesa da yana yinsa" ta fahimci yaji zafin Abinda suhan tazo ta Aikata"zama kawai yayi kan kujerah beyi mgn ba "ta kallesa tace"kana jina?"uhmm"bance kamata fad'an Abinda tayiba"ba kuma wannan ne karon farko datayi rashin daidai ba"saidai bana daga cikin masu kai k'orafi ko k'ara"tayi iya rashin kunyarta lokacinta ne"Abinda kawai zaka sanar mata karta koma zuwa sashen nan"ta tsaya iya nan ta k'arasa d'iban Albarkanta"nasan kasan irin rashin mutuncin datayima su salma kwanaki, Amma bance maka komai ba"saidai nasan baka san Abinda yayarta tayiba ranar da aka kawota gidan"sbd haka ka zama tsayayye Agidan ka"dama irin haka na gudar maka gashi tun kafin tafiya tayi nisa kaga ba daidai ba"shiyasa mutum ya Auro y'ar gidan mutunci da tarbiya keda Amfani "yasmeen ko had'a Ido dani yarinyar nan bata iyawa"mgn cikin ladabi ta tausasa harshe haka takemun"ga kunya da kawaici da nuna ita ba kowa bace"tunda kaje ka d'akko mana wacce idonta yabud'e har haka taya zata maka biyayya da ladabi??wlh Ina koma gargad'arka da babbar murya ka k'ara rik'e yasmeen da mutunci"Inka bari ta sub'uce maka daga hannunka da wuya kasamu kamarta"kuma bazan tab'a tsayama takoma maka karo na biyu ba"idan kaga daga farko na Amsheta ka had'a baki da Alh ta koma to idan ka koma yimata wani Abu bbu ruwana....daga k'arshe karna koma jin labarin taje har d'aki sunyi rigima da yasmeen harda makami sbd rashin hankali"in kuwa tayi mata lahani wlh harkai sai Abin ya shafa"tana fad'in hakan taja tsaki tabar parlourn batare data jira yabata hak'urin dayakeso yabata ba"shi kansa yasan yayi babban kuskuran Auren suhan"sai yanzun ya yarda da zancen mohd daya ce sam be dace da itaba"tayi sanadin b'acin ransa dana mahaifiyarsa Ahaka har zai iya cigaba da zama da ita??...ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login