Showing 33001 words to 36000 words out of 85260 words

Chapter 12 - _NIDA_BARRISTER_SADEEQ_Complete

04 Apr 2025

7423

kawo haka?"sai mgn yakeyi cikin b'acin rai "mohd dayakeyi danshi Abokinsa nefa.... k'arar rufe k'ofar dayayi yadawo da ita tunaninta"sai d'aure fuska yakeyi yana jan tsaki "itadai burunta yacika mata hannunta"Amma beda niya "yaya sadeeq dan Allah Amai nakeji... mitsssssuww! kima maidashi idan yataso"kika koma b'atamun jiki da kazantar Amanki saikin lashe kayanki"yak'are maganar yana d'aukar wayarsa da suhan ke kira"cikin taushin muryansa me dad'in sauti yace"sweet heart kina raina sai gashi kin kira"to ai naga bakada niyar kirana shiyasa nace bara ni nakiraka naji lafiyarka mijina"ya wani lumshe Ido yana fad'in lafiya qlau nake zamu fitane Anjima zan kiraki"kaida waye zaku fita d'in?...."yasmeen dake sauraronsu tayi wuf tace shida k'anwar gyatumarki ne"bige mata baki yayi yana yanke wayar"ita kuma ta turo baki tana fad'in Allah saina rama"uhmm to shikenan idan zaki iya"gulmar banza Akanme zaki shiga sabgar rabin raina?"nama d'auka rankace ita gaba d'aya "?yana k'ok'arin mgn suhan ta kirashi"be d'auka ba sbd yasan k'orafi zata masa sbd taji muryar yasmeen"dan Allah mlm kacikani"ta fad'a suna isowa parking lot "driver yataso yana gaishesu "yasmeen ta gaidashi "yana murmushi ya Amsa ya bud'e musu back sit"sadeeq Lamid'o yamasa Alamar yaje basu buk'atarsa "mazaunin driver ya shiga ya zauna fuskarsa a gimtse"ganin hakan yasa itama ta shigo"yaja tsaki yana fad'in daga yau nakoma ganin kin gaisheshi wlh saikin raina kanki"ya k'are maganar fuska Ahad'e yana jan motar"itadai shiru tayi"Abin mamaki me makon su fara tafiya Asibintin sai kawai yatsaya daidai bakin wani babban shago"da suke siyarda wayoyi da layi" da mamaki yasmeen ta kallesa yasakar mata wata uwar harara"ta d'auke kanta "kina jiran nace ki fito muje ne?"batace komai ba ta fito da k'yar sbd tana jin jiki daurewa kawai takeyi "jerawa sukayi suka nufi cikin shagon"masu shagon suna ganinsa suka masa barka da zuwa "yanata shan k'amshi suka gaisa"jeki can daga bayan can ki duba akwai manya"yafad'a yana kallonta"toni yaya sadeeq muje ka rakani mana....ranki yadad'e bara nazo muje saiki duba ko?"cewar wani da tunda suka shigo yake kallonta"sadeeq Lamid'o ya gimtse fuska ya bishi da wani shegen kallon daya sakashi jin fad'uwar gaba "ita kuwa yasmeen bata tanka suba ta wuce tana tunanin wane irin murd'add'en haline sadeeq kedashi?"ita tama rasa wace zata d'auka "saidai data tuna wayarsa iphone 14 ce kawai saita d'auketa"sbd ta k'uresa yace ta d'auki iri d'aya dashi"saidai batasan wayar nada tsadar gaske ba....kije can layin ki zab'i cover da baby nokia"taji muryar sadeeq Lamid'o Abayanta ya matso yamata zobe da hannayensa yana Amsar kwalin wayar yana dubawa"ta marairaice murya nidai yaya sadeeq daga baya ka siyamun cover d'in wlh jiri nakeji ni"ta k'are maganar cikin y'ar shagwab'a "ya dinga kallonta kawai yaga zata silale ta fad'i"yayi saurin rungumeta ta baya "ta d'auke numfashi sbd k'amshin turarensa da bataso"ke matsalata dake bakida dauriya "Eh naji nidai kacikani muje"cikata d'in yayi ta matsa ta d'auki cover da k'yar tana dafe bango"wajen biyan kud'in tasamesa"saidai dataji yana fad'in su zare kud'in ta ATM card nasa tayi mugun mamaki"gashi Anata kallonsu bbu damar ta musa masa"ganin zata fad'i yasaka ta matso ta kwantar da kanta gefen kafad'arsa "saida yaji wani iri"cikin murya me kama da rad'a tace"yaya sadeeq dan Allah muje karna fad'i"shiru yayi beyi mgn ba"sai bayan sun zare kud'in ya sak'alo hannunsa gefen bayanta daga saman k'ugunta ya rungumota suka bar wajen"da kansa ya bud'e mata k'ofar ta shiga sannan ya zagayo ya shigo ya aza mata ledar kwalin wayar saman cinyarta"batare data kallesaba tace"yaya sadeeq kayi hak'uri wlh wayar nan tafi k'arfina"niban zata haka tsadarta takeba"wacece ni dazan rik'e irinta?"dan Allah ka rik'e gobe ka mayar musu su baka wata daidai dani "dama naga irinta gareka shine na d'auka sbd na tsokaneka.....tunda ga Abokin wasanki ko?"dolema ne na gyara miki zama kwanannan"batun waya bazan canzaba gulmar data saka kika zab'eta saiki d'auka "idan layin ya hau zamuje A bud'e miki acc "karkije kimun sharrin bana baki kud'i "koki rok'i mohd yabaki"kin mgn tayi"saidai shi kuma mamakinta yakeyi"meyasa zatace iphone 14 tafi k'arfin rik'eta?"ga wasu nan da yawa dasuke son nuna su wasu ne"Atake suhan ta fad'o masa Arai "ko jiya tasanar masa irin man datake shafawa dubu sittin yake befi idan ta siya yamata wata gudaba yak'are" da yayi lissafi set d'in sabili,turare mai datake shafawa duk wata dubu d'ari biyu da hamshin suke"ita idan son samun tanema tayi Amfani da wad'anda suka fisu tsada....ita waccan wayar idan ka Amsa kayi me da ita?"dan Allah kabarmun layin "bazan bari ba"yarda ita zanyi idan kin tashi sai kiyi tunk'aho da wani Abun bada wanda wani yasiya miki ba"ohk yaya mohd ne d'inne wani? ban saniba"jan bakinta tayi ta tsuke tana mamakin meyasa yake yin hakan?"sai tsaki yake ja yana driving d'in"ita dai yasmeen bata tankashiba har suka iso *Lamid'o international hospital* tana ganin sunan Asibintin ta tabbar Asibintin mama ce"bayan ya gama parking suka fito tare"Adak'ile yace "zamuje office nata ta dubaki saura ki musa mun"batayi mgn ba "yayi gaba cikin takunsa na izzah"ta girgiza kanta tana biye dashi"suna k'ok'arin shiga k'ofar da zata sada mutum da reception wani saurayi na kawowa zai wuce"sun kusan bangazar juna da sadeeq yaron ya kauce batare dayasan su biyu bane yana tahowa suka bangaji juna da yasmeen "ta saki k'ara tana dafe gefen k'ofar"subahanallahi! sannu kinji?"ban lura bane wlh"duk yayi maganar yana tsura mata Ido yama d'auka budurwace kuma ba tare suke da sadeeq ba"saidai yasmeen bata tankashiba"sadeeq Lamid'o kuwa had'e rai yayi yafasa shiga yayi baya yana binsu da kallo batare da yaron ya lura ba"baby bazaki iya shiga ciki bane.....wata wawar damk'a sadeeq yamasa ta baya "yana juyowa suka had'a Ido "wani wawan mari ya d'aukesa dashi yana fad'in jakin inane kai kake tanka matar Aure??"da matuk'ar mamaki yasmeen ke kallonsa sbd bataga Abinda yakai yayi dukaba.....kayi hak'uri bansani bane" ah ah kasani bara kawai na d'umamaka sai kafi sani da kyau"yasmeen najin hakan da sauri ta matsa tayi hugging d'in sadeeq ta baya ta mak'alk'alesa tana fad'in yaya sadeeq ka k'yalesa muje wlh na kusan fad'uwa"ta k'are maganar tana kwantar da kanta saman bayansa"wanda hakan yabama nashanunta damar gugar bayan nasa"babu shiri yacika yaron yakasa furta komai"dama lallab'awa yakeyi gashi tana neman tayar masa da hankali.....cikin kasalalliyar murya yace"yasmeen cikani muje"batace komai ba ta janye jikinta ya kalleta suka had'a Ido"ta turo baki tana fad'in shine saika dinga fad'a da mutane ko?"beyi mgn ba sai hannunta daya kama suka wuce ciki"tunda suka shigo aketa kallonsu"sbd wasu sun san shine d'an wacce keda Asibitin"duk wanda ya kallesu zai musu d'aukar masoya ne"sbd yadda sukayi matuk'ar dacewa da juna"kai tsaye wani had'ad'd'en office sadeeq yanufa da yasmeen"sai tafara k'ok'arin k'wace hannunta sbd kunyar mama ta gansu yana rik'e da ita"shi kuwa juyowa yayi ak'ule ya kalleta yaja tsaki"yajata da k'arfi suka shigo ciki da sallama"mama na zaune tana duba wata yarinya mamanta na rik'e da ita"Amsa sallamarsu tayi"ta kallesu tana fad'in daga Ina haka yasmeen?"saida ta gaisheta kafin tace"nan muka zo bani jin dad'i ne"okay babanah kaje reception ka yankar mata kati"dato ya Amsa yafita yabar yasmeen nan"mama tace ta zauna kan d'an gadon da ake duba patient"sai satar kallon yasmeen d'in take"tama gama fahimtar juna biyu ne da ita" bayan ta sallami matar tace"zoki zauna yasmeen yanzun kin mana tawaye ko?"shiru tayi tana d'an murmushi"bayan ta zauna mama tafara yimata BF sannan ta duba laptop taga sunanta yafito"Ahankali tace"meke damunki?"kanta na'a k'asa tayi mata bayani"roba ta bata tace taje toilet tayi fitsari"saida gaban yasmeen ya fad'i fatanta Allah yasa ba juna biyune da itaba"Ahankali ta tashi ta nufi toilet d'in "bata jimaba ta dawo tasami sadeeq zaune yanata cin magani"kafeta da Ido yayi yana kallon Abinda ke hannunta"mama ta Amsa sannan ta zauna ta d'ibi jininta "bayan ta gama ta fita ta barsu ciki"kamar yana jira ta fita fuska a gimtse yace"Allah yasa ba juna biyune bane sbd ban shirya haihuwa yanzun ba"uhmmm bana fushi da hukuncin Allah"saidai bana so na haihu dakai.....cikin fushi sadeeq ya mik'e tsaye ya iso gabanta yana nunata da yatsa yace "nine yaka mata na fad'i haka"bana buk'atar ke ki haifamun yara "wannan sai suhan"sbd haka idanma shine zubar dashi zanyi"dubeki dan Allah"Ai da kunya Ace kece zaki zama uwar yarana"ke d'in yaushe Aka haifeki har kika girma ? fatana Allah yasa ba shi bane"idan kuwa shine kima shirya saina zubar dashi"suhan ce nake da muradin ta zama uwar y'ay'ana bake stupid ba"yafad'a yana jan tsaki yana banko mata harara"duk tana jinsa batace masa komai ba sbd tasan datayi mgn kuka ne zaici k'arfin ta"suna a haka mama ta turo k'ofar fuskarta cike da fara'a tana fad'in Alhamdulillah babanah"yasmeen na d'auke da ciki sati hud'u"Allah ya inganta yabada lafiya"daga shi har yasmeen d'in bbu wanda yayi mgn "sai mama ta d'auka kunya sukeji"magunguna ta rubuta mata "sannan ta tura ta laptop a pharmacy room"sadeeq yaje ya Amso "ta tabbatar masa ya dinga kulawa da yasmeen da gudun bacin ranta"shidai dato ya Amsa "sukayi sallama suka fita"ran mama fas tanata sauri ta gama Abinda takeyi ta koma gidan.....suna fitowa......✍️

wannan book d'in na kudine ! idan kina buk'atar siya serious regular grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK

Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
2/26/24, 14:09 - Ummu: *Littafin kud'i ne!*
........suna fitowa daga cikin office d'in yasmeen tayi gaba da sauri batare data jirashiba"sbd ba k'aramin haushi yabata ba game da irin bak'ak'en maganganun daya yayyab'a mata" ba k'aramin sukar zuciyarta sukayi ba"ta dai daure ne ta tursasa kanta ta b'oye yanayinta"tana k'ok'arin wucewa taji Ance yasmeen! tana waigowa taga wata kiristan y'ar Ajinsu"d'an murmushi tasaki ta tsaya tana fad'in Affiyo ya kike? Matsowa gefenta tayi tace"banida lafiya wlh"yau kinje skul ne?"ah ah "nima banida lafiyar banjeba"Amma gobe in naji da sauk'i zanje"ta k'are maganar lokacin da sadeeq ke wucewa gefensu"yana mamakin jin yadda yasmeen ke zuba turanci"sbd duk maganar da sukayi da turanci ne"shifa ya d'auka bata wani iya turanciba"yana isowa gefen motar ya bud'e yashiga yatashi motar, sbd ganin bata biyo saba kuma batakai matsayin dazai jirataba"yana tada motar yasmeen na fitowa daga ciki"d'auke kanta tayi data hangosa yafita daga cikin get d'in Asibintin"sai kawai itama ta fito ta nufi bakin titi"da nufin ta hau Adaidai ta koma gida"har cikin ranta batason cikin, musammun uban cikin daya nuna be sonta beson cikin"saidai ta fawwalawa Allah komai"ta kuma d'auka hakan na daga cikin jarabawarta" tana nan a tsaye wata had'ad'd'iyar mota bak'a tayi parking gabanta"bayan An zuge glass d'in motar saurayin d'azun yazuro kansa yana murmushi yace"shigo na saukeki inda zakije"kauda kanta tayi tak'i mgn"dan Allah ki fad'amun da gaske wannan guy d'in mijinki ne?? k'in mgn tayi gabanta na fad'uwa tafara k'ok'arin matsawa shi kuma yaci gaba da binta"sai Akayi sa'a ta hango me nafef"saita tsayar da me nafef d'in"tana k'ok'arin shiga taji wani mahaukacin horn Abayansu"ta juya taga motar sadeeq ce"Ashe saida yasha Newtown sannan ya hangota saiya tsaya"kauda kanta tayi tana d'aure fuska ta sanarwa me nafef d'in inda zai kaita ta shigo....kai ! karka d'auketa ka jira nace...taji Amon kakkausar muryar sadeeq Lamid'o yana fad'a Abayansu"kayi hak'uri dan Allah"shine Abinda ta fad'a tana fitowa daga ciki"sukayi Ido hud'u dashi yana jifarta da wani irin mugun kallon daya saka taji mugun shakkarsa da kwarjininsa"uban me kika tsaya yi gaban waccen motar??"shine Abinda yafad'a cikin tsawa yana zare mata Ido"tak'i mgn "yajuya cikin fushi ya nufi wajen motar sbd har lokacin tana fake"tun kafin ya iso guy d'in yafito yana kallonsa bbu Alamar tsoro Atare dashi yace"raina ya bani ba matar Aure bace k'anwarka ce ko kuma soyayya kukeyi da ita"inaso kabata dama ta zab....isowar dayayi gabansa Afusace yana huci yasaka saurayin yin shiru yaja da baya yana fad'in karka sake ka koma tab'ani"ka mareni na barka sbd ita....wane irin jaki ne kai?"matar tawa kakeso kace kana so sbd kana jahili??"yafad'a yana cin kwalarsa"yayinda mutane ke kallonsu"gaban yasmeen bacin fad'uwa bbu Abinda yakeyi ita tsoron tankashima takeyi sbd irin kallon dataga yana jifarta dashi"saidai ganin sadeeq ya shak'esa Azuciye yasaka ta nufesa tana jan hannunsa"wasu maza biyu suka iso suka k'wacesa"saidai sadeeq yace"sai yaga uban waye ubansa?"rirrik'esa Akeyi Amma ya fisge ya hana yaron shiga mota.....yaya sadeeq idan kana yiwa Allah kazo muje ko naje na sanarwa mama Abinda ke faruwa "nan mazan dake wajen suka dinga bashi hak'uri"yaja tsaki yana fad'in zamu had'u dakai next time dole ka kwana bayan kanta shashasha kawai"yak'are maganar yana fisgar hannunta da k'arfi yanufi gaban motarsa ya turata ciki"ya zagayo Azafafe ya shigo"cikin tsawa yace"fad'amun da ubanwa da ubanwa kike mgn dashi a skul d'in ko kuma yake miki mgn?"tana kuka tace"ni wlh babu wanda nake ma mgn"yaja tsaki ya fisgi motar da k'arfi yana jan tsaki yace"wlh daya yau na koma fita dake wani waje kika tsaya shirmen banza saina tattakaki Awajen"shiru tayi tak'i tankashi"wayarsa tayi ringing yama zata suhan ce sai yaga mohd ne"d'auka yayi beyi mgn ba "Abokinah gani nan gidanku baku nan"kajirani muna hanya"daga haka ya yanke wayar ak'ule yace"wlh ko kimun shiru kokiji saukar mari "idan kuma gurin shi d'an iskan zaki koma saina saukeki ki koma wajensa"nanma tsit tayi"har suka iso gidan masifa kawai Lamid'o yakeyi"yana gama parking ya mik'a mata ledojin maganin dana wayar"ni bana so ! bai zama dole na rayu da wayaba"kuma yanzun zan bama yaya mohd wayarsa tunda dama shine yabani nace masa ka hana ni rik'ewa"d'ago kansa yayi yana tsareta da rinannun idanuwansa da sukayi jajir"Allah yabaki sa'a kije ki masa mgn da kin gane Ainahin true colour d'ina "zaki Amsa ko saina koma saki wani sabon kukan"hannunta na kirma ta Amsa "yana fad'in hakan ya bud'e k'ofar da k'arfi ya fito yamayar da k'arfi ya rufe"ita kuwa bata koma kallonsaba tayi gaba"saidai kasancewar tak'in nasu ba d'aya ba "tana tafiya yazo ya wuceta....daga nesa mohd dake zaune da kakinsa Ajikinsa ya hangosu"yadda yaga fuskokinsu saida gabansa yafad'i "ya girgiza kansa Aransa yace"Lamid'o Allah yakamaka sauk'i "yana isowa ya zauna gefensa ya furzan da zazzafan huci daga bakinsa yana fad'in kafin ka kirani da zanma kiraka ka turomun police su kama mun wani k'aramin d'an iskan yaro"subahanallahi! meya had'aka dashi?"waccan marar mutuncin mana ta tsaya yana mata mgn"d'an murmushi yasaki domin yadda yayi maganar da k'wayar idonsa daya kallah ya fahimci zahiri yafara kishin yasmeen"saidai bece komai ba sbd ganin yasmeen d'in ta iso"kallo d'aya yamata yasan kuka tayi"yaya mohd Ina wuni?"lafiya qlau yasmeen ya gidan?"Alhamdulillah"daga haka tasaka key d'in ta tabud'e k'ofar ta shiga ciki"wai meke faruwa ne? naga kaida ita kowane yana cikin fushi"tab'e baki sadeeq yayi yana fad'in wlh yarinyar nan 2 days d'in nan tafara rainani"shiyasa nace maka Auren yarinya k'arama sam beyiba"inda babbace ita taya zata nemi kamun raini?"karka damu Ango Aiga suhan nan ta kusan zuwa normal zaku zauna ta bika da yadda kakeso"ya yatsina fuska yak'iyin mgn"nazone dama kan shari'ar da zaku shiga ne gobe"banaso ka kare yarinyar nan Lamid'o"Alh idi ba k'aramin mugum mutum bane"tabbas nasan sai kayi nassara a shari'ar sbd baka zama lauyen marar gaskiya" wlh wlh!! yayi kisa da fyad'e k'aramin Aiki ne"yanada had'arin gaske mutumin"kuma matsafi ne"Ina me baka shawara ka hak'ura ka janye kace su nemi wani"bawai Ina nuna maka kaji tsoronsa bane"ah ah kwanciyar hankalinka data family naka nake so"kaga Alh lamis yana gidan yari bana zaton idan yafito zai barka"sbd kayi sanadin zuwansa gidan yari ya jima , sannan kayi sanadin kai d'ansa bilal mak'argama"sannan ga kuma Alh idi"bana jin taka ta family naka nakeji kaduba....dama dalilin zuwan naka kenan?"yafad'a cikin izzah yana mik'ewa tsaye"Ido cikin Ido yace"in sha Allah gobe 2pm zamu shiga kotu"idan munyi nassara daga baya yamun yankan rago dama haka Allah yaso"kana bani kunya DPO dakai kana tsoron wani tsohon banza"wlh ba tsoro bane gaskiya ce Lamid'o"Amma tunda bakaso shikenan"yanzun kaje ka rarrashi babynka naga kamar fushi takeyi"yafad'a cikin tsokana"uhmm tayi ta gama nafi k'arfin hakan"k'ilan sbd tanada juna biyu take fushin ko"in bacin wani dalili wlh da saina zubar dashi"tunda har tana gayan mgn bata son haihuwa dani....dariya kawai mohd keyi yana kallonsa saida yayi me isarsa yace"Ashe kingin yasmeen suhan zata Aura?"yanzun ba saurayi bane kai second hand ne"duk Ina ka Ajiye girman har ka surnana ma y'ar mutane ciki Lamid'o??wani wawan duka ya kaimasa ya goce yana dariya ya mik'e tsaye yana fad'in baka sonta Amma kana son hutawa da ita ko?"kaga pls jeka dallah"dole kace haka tunda na fad'i gaskiya ko?"saidai kaji tsoron Allah karka zubar mata da ciki"sannan kasani me yaron ciki ba'a son yawaita saduwa da ita sai cikin yayi k'wari"yana k'arami zai iya samun matsala"Allah ya inga mana "nasan lokacin da kwatan ran naka zata shigo yasmeen tayi nauyi"banza sadeeq yamasa ya tashi ya wuce ciki "directly d'akin yasmeen ya wuce.... fuska Ahad'e yaturo k'ofar ya shigo"tana zaune saman bed d'aure da farin towel"da Alama daga wanka ta fito"tana ganinsa tayi saurin rarumar bed sheet ta rufe jikinta"kallo d'aya yamata ya d'auke kansa yana tab'e baki sbd wani irin haushinta yakeji sbd Abinda yafaru a d'azun.... Adak'ile yace Ina wayar take?"ka bari dan Allah na fidda duk Abinda ke ciki me mahinmanci saina kamaka harda sim card d'in dan Allah "yayi shiru yana kallon wayar sabuwa data saka chargy"kinsha maganin?"ah ah"ya kalleta ta sunkuyyar dakai "Ahankali tace"dama sai naci wani abu zan sha"mintina 20 na baki kije ki wanke kayan dakika b'ata da Amai"dato kawai ta Amsa sbd Azauna lafiya" ta lura fitinah kawai yake nema da ita"be koma mgn ba yajuya yafita....yana fitowa zarah na shigowa parlourn rik'e da kula a hannunta....koma had'e rai yayi batare daya Amsa gaisuwar taba yace"wato gulma takawoki ko?"wlh ah ah yaya"mama ta kirani tace na zubo Alalan wake danayi sbd Ina Azumi nakawowa Anty yasmeen"ya yatsina fuska ya Amshi kular"ita kuma ta fita da sauri"Ajiye kular saman center table yayi yakoma nufar d'akin "babu sallama ya turo k'ofar ya shigo yayi tsaye"yasmeen na tsaye gaban ward rope zata d'auki kaya"ta d'aure fuska tana fad'in wai yaya sadeeq wannan y'ar zaryar ta mecece kakemun ?"bansaniba"in kin gadama kije kiyi Abinda nasaki kafin ki Amshi sak'on da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login