Showing 27001 words to 30000 words out of 85260 words
tagama sallar take son ta koma part d'insu saidai tana tunanin sadeeq yadawo"ita kuma bata son had'uwa dashi"tana dai zaune gefen kujera kan carpet"Anty salma nata fira da moon bata saka musu baki"zarah kuma tana kitchen zata Aza dinner"mama kuma na kallo a sunnah TV.....oyoyo uncle! cewar baby Amrah y'ar wajen salma tana kallon sadeeq "dake k'ok'arin shigowa cikin parlourn"gaban yasmeen yafad'i dataji k'amshin turarensa "ta d'ago kanta da sauri suka had'a Ido dashi"da sauri ta sunkuyyar da kanta k'asa "sbd tun wayewar yau sai yanzun ta yadda suka had'a Ido"Anty kuna nan kenan?"Eh sadeeq ya Aiki?"Alhamdulillah "Ina suhan Amarya?"Ashe next month za'a saka muku rana?"Ai gara Asaka Allah yasa Alkhairi"tunda take maganar uban gayyar beyi mgn sai satar kallon yasmeen dake zaune gefe yayi"bega wata Alamar damuwa saman kyakykyawar fuskarta ba game da kalaman Anty salma"yana k'ok'arin zama salma tace yauwa muje ciki ina son mgn dakai"bece komai ba yanufi d'akin baccin mama ita kuma ta tashi ta bishi"mama kuwa tasha Alwashin zata takema salma burki tadena cin fuskar yasmeen "wacce yasmeen Azuciyarta tana mamakin duka watansu 4 da Aure shine za'a saka musu rana da wata"sbd ya nunama duniya baya k'aunarta?"sosai taji tausayin kanta"mama dai nata kallonta"ita kanta bataso sadeeq ya kinkimo k'ara Aure yanzun ba"saidai tunda yanaso kuma da lafiyarsa da wadatarsa sai yayi"musammun tunda bason yasmeen d'in yakeyiba....k ! zaman meye kikeyi Anan ki tashi ki koma mana"taji muryansa yana daga tsaye"ka barta sai zuwa Anjima mana"idanfa tayi bak'i mama?"yasmeen batace komai ba ta mik'e tsaye batare data kalli kowaba tace sai Anjimanku "tana fita yabita da sauri"kasa cewa komai mama tayi"zarah ta girgiza kanta tace"wlh mama yaya bayama Anty yasmeen Adalci ko kad'an bewar Allah"tana k'ok'arin kyautata masa yayita mata wulak'anci"yanzun mama ba sai kice yabarta Anan ba"wlh inda nice ita bazan iyaba....bama fatan Allah yasa Abba yamiki Auren dole"cewar Anty salma data fito daga cikin d'akin"mama ta bita da wani irin mugun kallon datasha jinin jikinta murya Akausashe tace"wannan itace mgn ta dake ta k'arshe game da matar sadeeq"ki fita harkanta bbu ruwanki da ita"me y'ar mutane ta miki kika tsaneta har haka?"wlh kika bari Alh yaji maganar nan sai kin gane kuranki"kwata kwata yarinyar nan batasan da zancen nan ba shine kikayi maganar da gayya Agabanta sbd taji ko?nifa mam...rufemin baki mutuniyar banza"shi kuma zaizo yasameni "me kuma sadeeq yayi?"ban saniba"idan kinsan tada zaune tsaye zai dinga kawoki gidan nan kiyi zamanki gidanki"ita rayuwa baka sanin menene Alkhairi gareka"ka kyautata ka nemi zab'in Allah "indai suhan ce yaje ya Aura "idan har naga Akwai cutarwa zanyiwa Alh mgn yasakashi ya sallameta saiya zauna da wacce yakeso wata tsiyace"sosai mama keta fad'a "salma ta kasa cewa komai..... yasmeen na fitowa taji motsinsa Abayanta"sai bata juyo ba"shi kuma sai k'are mata kallo yakeyi daga bayanta har suka iso bakin k'ofar parlourn"tasaka key ta bud'e" so takeyi tayi kuka ko taji sauk'in Abinda takeji a zuciyarta"tasha Alwashin har part d'in iyayen nasa tagama zuwa"tana bud'ewa suka shigo tare kamar zai bangajeta"ta kauce bata kulashiba"ta nufi d'akinta "mayafin ta cire da d'an kwalin tana ninkewa yaturo k'ofar ya shigo"saida gabanta yafad'i....yayi tsaye yana danna waya cikin husky voice yace"daga yau na hanaki zuwa ko Ina sai kin sanarmun banda skul"dato ta Amsa bata yadda ta kallesaba"fatanta yafita kawai "be fitanba sai bayanta ya matso ya Amshi mayafin ya aza saman mirror ya rik'e hannunta guda"ta d'aure fuska tanaso ta k'wace "beyi mgn ba yajata yanufi saman bed da ita"me kuma zaka mun dan Allah?"Abinda mukayi jiya"saiki ji dad'in cewa baki yafemun ba ko?yafad'a yana k'ok'arin zuge mata zif d'in riga"jikinta na rawa tace"wlh zafi wajen keyimun dan Allah karkamun kayi hak'uri"ban sanar miki ba Atsarina ba'a bani hak'uri?"tayi shiru hawaye na zubo mata"beji wani tausayin taba biyan buk'atarsa shine ransa"gaba d'aya yahaye samanta yanaso yayi kissing nata"sai tak'i yarda ta kauda kanta ta rufe bakinta gam"ta k'ank'ame dukiyar fulaninta"hakan yasaka yaci gaba da tafiyar da ita irin jiya"yanayi tana kuka da kiran sunan babanta yazo yataimaketa"sosai sadeeq yajima Akanta har aka fara kiran sallar magrib sannan ya k'yaleta"bayan ya suturta jikinsa yafice daga cikin d'akin bebi takan taba"gaba d'aya gabanta zafi da rad'ad'i yake mata"daurewa kawai tayi ta tashi tashiga bath room "tajima ciki tana kwance cikin ruwan d'umi tana kuka"saida ta fahimci lokaci yafaraja sannan ta fito tayi sallah daga zaune"tana gama magrib tayi isha'i "ko Abinci bata nema ba ta kwanta sbd jikin nata babu dad'i"ga zuciyarta dake mata rad'ad'i "wani irin mugun tsoron sadeeq ne Aranta "sai tunani takeyi Anya za'a samu miji marar tausayin matarsa irinsa"tajima tana tunani daga k'arshe bacci yasaceta"washe gari bata makaraba ta tashi tayi raka'atanil fijri sannan tayi sallar Asuba "tana idarwa tafara Azkhar da karatun Alkur'ani me girma"Atake taji zuciyarta ta mata wasai"sai wajen bakwai da rabi ta koma bacci"bata farkaba sai wajen goma saura"wanka ta shiga ta gasa jikinta ta fito"bayan mintina 15 ta gama shirinta cikin doguwar riga gownt "saidai tana dosowa cikin parlourn taji fad'uwar gaba sbd k'amshin turaren sadeeq Lamid'o dataji"daurewa tayi batako kalli gefen dayake ba sbd yunwa takeji sosai" K! banza ta masa tanama k'ok'arin tayi wucewarta....*yasmeennnnnnnnn!* yakirata cikin k'asaitacciyar muryarsa "ta juyo da sauri sbd mamakin jin sunanta daga bakinsa"wanda tunda take dashi be tab'a kiran sunan taba sai yau dataji ya kira"wanda har cikin kanta taji sunan,yana sanye da t shirt da wondo 3 quarter rigarsu irinta lauyoyi da hular na Ajiye saman center table"zuwan zakiyi ko kuwa kallonah zaki tsaya kina yi ne?"batace komai Ahankali take nufo inda yake sbd har yanzun jikin nata babu dad'i"nesa dashi ta duk'a fuskarta bbu walwala tace gani"banza yamata kusan mintina 5"cikin k'osawa tace"dan Allah nidai gani" banida mutuncin da zaki gaisheni?.....✍️
wannan book d'in na kudine ! idan kina buk'atar siya serious regular grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
2/26/24, 14:08 - Ummu: *Littafin kud'i ne!*
.......da mamaki yasmeen ke sauraron kalamansa har yayi shiru "saidai ta kasa cemasa komai"cikin zafin rai yace"idan baza ki iya yin mgn ba tashi ki bani waje"da sauri tayi k'ok'arin tashin "sosai ta bashi mamaki....K dawo ki zauna"wai yaya sadeeq me kake nufi dani ne?"karka manta kaine da kanka kace nadena gaisheka ko yimaka mgn saika mun shine kuma kake tuhumata?"ta k'are maganar kamar zatayi kuka fuska bbu walwala"shi kuwa saida ya gadama dan kansa kafin cikin Isa yace"Eh nine nace na kuma janye hakan sbd na gwadaki nayi hakan"sai Abu na gaba gyaran part d'ina yadawo kanki dole ki cigaba"daga k'arshe kije kiyi list d'in Abinda babu a paper ki kamun"kika sake kika b'ata mun time rankine zai b'aci"batace komai ba ta mik'e tsaye zata nufi kitchen....Ina nace kije ne?"yunwafa nakeji ni"ta fad'a tana b'ata fuska "zoki Amsa badan halinkiba"batare data juyoba tace"bana buk'atar komeye naka"daga haka ta shige cikin kitchen d'in tana jin tsoron karya biyota"da sauri tajawo k'ofar zata rufe shi kuma Adaidai lokacin yadoso cikin kitchen d'in"da k'arfi yasaka hannu ya rik'e k'ofar "tana turowa iya k'arfinta shima yana turowa"shi dariyama tabashi sbd yana iya hangota har cije baki takeyi tana turo k'ofar "saida ya bari ta gaji sannan da k'arfi yaturo"tayi saurin matsawa gefe tana sauke numfashi batare data yadda ta kallesaba....naga Alama har yanzun ban gama fidda rainin dake tsakaninmu ba"yak'are maganar yana tunkarota"ta duk'e k'asa ta saka kanta a tsakkiyar cinyoyinta ta kama kukan da bbu hawaye"beyi wata wataba ya sungumeta yafito da ita daga cikin kitchen d'in"bana so ,nika saukeni ,wai mlm meye haka?"dan Allah ka k'yale ni....Ank'i Akyaleki d'in" takura miki yanzun na fara keda samun saukinah sai my suhan Amaryar ki ta shigo"yafad'a murya can k'asa yana kallonta da tsantsar rainin wayo"yasmeen tayi murmushin da beauty point d'inta ya lutsa tana fad'in banida burin daya wuce na rabuwa dakai"bana kuma fatan har ita suhan d'in tazo ta sameni "Abu na k'arshe dan Allah ka k'yaleni "Abinda kamun jiya da shekaran jiya ban yafe maka ba"tunda nazo gidan nan kake cutar dani meyasa baka tuna hakk'i....matse mata lips dayayi yasaka tayi shiru "dukda a bad'ini kalamanta sun tsaya a zuciyarsa Amma Azahiri saiya nuna ko Ajikinsa saima d'aure fuska yayi ya direta saman kujera cikin tsawa yace"d'auki ledar nan ki duba Abinda ke ciki kici ta Arzik'i ko kici ta tsiya"zab'i yarage naki"tayi shiru"yana daga tsayen ya dako mata tsawa yana fad'in baraki d'auka bane?"tana kuka jikinta har rawa yakeyi ta d'auka sbd irin tsawar daya dako mata ta tsorata "yaja tsaki ya zauna kan kujerah yana d'aukar remote ya kunnah TV"kafin ya kalleta"yaga kuka takeyi take away d'in chips dana kaji a hannunta"ko kukan jini zakiyi sai kin cinye"ki tashi kije ki had'a tea kidawo kici"idan kuma kika bari nasameki a kitchen d'in sai ranki yab'aci "batayi mgn ba ta tashi ta nufi kitchen d'in"batafi mintina 10 ba tadawo rik'e da cup ta zauna tana tunanin wani yatura yasiyo masa"wata zuciyar tace idan fa yazuba miki wani abun sbd yacutar dake fa?"wannan kuma shida Allah "ta fad'a Afili cikin sub'utar baki"yakafeta da idanuwansa masu matuk'ar kwarjini fuska Ad'aura yace"zagina kikeyi cikin ranki ko?"wlh ah ah yaya sadeeq ni bana zagin kowa"banza yamata yaci gaba da kallonsa ita kuma tana break fast d'in...bayan mintina 10 Ahankali tace na gama"banza yamata"yaya sadeeq nagama"ya d'auki kusan second 5 kafin ya kalleta yana tab'e baki yace"gulmar banza dama kinaso kike nuna bakyaso"mintina 5 na baki kije ki kamun list d'in fita zanyi"Allah yasa ki batamun lokaci ki gani"zancen baki yafeba daga yau bazaki koma fad'in hakan ba...batace komai ba ta kwashe take aways d'in ta mayar a kitchen sannan ta koma d'aki "cikin mintina 5 d'in ta dawo parlourn rik'e da paper d'in"yana tsaye yasaka kayan shiga shari'ar sai waya yakeyi ya juya baya"ta bishi da kallo daga kansa zuwa k'afafuwansa"ta kauda kanta tana Ajiye paper d'in saman center table"juyawa tayi tana k'ok'arin wucewa yak'ara mata k'afarsa me takalmi sawu ciki"ta saki k'ara tana fad'awa saman kujerah"ya kashe wayar yana kallonta fuskarsa babu Alamar rahama"ke wai yaushe kika rainani har haka?"kinfi k'arfin kice gashi ne?"yafad'a Atsawace yana nufo gefenta"ta matsa da sauri tana sakkowa k'asa tace"kayi hak'uri dan gashi"inda zaka bi ta tawa dak....shout up! da sauri tayi shiru"yaja wasu dogayen tsaki yana d'aukar paper d'in "hand writing nata ya kallah ,yaso yaga makusa kodan ya dank'ara mata mgn Amma saiya basar yaja tsaki yana fad'in Allah yasa nadawo baki gyara part d'in nawa ba"daga haka yajuya cikin gadara yafita"ta sauke Ajiyar zuciya tana fad'in masifaffe"ta tashi ta d'an kwanta kan 3seeter tana tunanin meyasa sadeeq ke kusantarta bayan baya sonta?"sannan taji ana cewa idan namiji nasamun biyan buk'ata da mace baya wulak'antata"ita meyasa har yanzun be dena yimata wulak'anci da mugunta ba??.....motsin turo k'ofar da zarah tayi yasaka ta dawo tunaninta"k'ok'arin saita kanta tayi ta daure ta tashi zaune ta dod'ana sbd zaman bata jin dad'in sa tafiso ta kwanta yafi yimata sauk'i"tana d'an murmushi tace"b'atan kai kikayi zarah?"ah ah wlh Anty yasmeen "kan idona yaya yashiga mota"shiyasa nace bara na lek'o mu gaisa kafin 12 tayi na wuce skul"dukda nayi kasadar zuwa kar inzo baki nan sbd nasan kina zuwa skul kema"hakane kin kyauta yasu mama?"lafiya qlau tana Asibiti"mutumin ki kuma yana skul"wai wacece ke miki lallen nan?sunanta jamila idan kinaso in tazo saita miki"daga haka suka d'an tab'a fira kafin ta wuce sashensa"zarah kuma tafara gyara main parlour dukda ba wani dirty yayiba....dukda yasmeen bata jin dad'in jikinta haka ta daure ta gyara masa d'akin sosai"har kayansa na ciki dabaice ta wankeba dukta wanke data gani a toilet d'in da handcheeps d'insa"Agajiye ta sakko down stairs d'in"ta samu kaya jibgi guda na cefane da sadeeq yaturo wani yaronsa yakawo"zarah na ganinta tace"Anty Ashiga dasu ciki yaya ya Aiko Akawo?"Eh zarah sannunki da Aiki "dato ta Amsa ta tashi,ita kuma ta kwanta tana hutawa....da yamma yasmeen na zaune a parlourn tana kallon wani indian firm "Tasha gayunta cikin k'ananun kaya tanata zuba k'amshi"gaba d'aya hankalinta baya wajen tv d'in yana wajen tunanin babanta da garinsu"fatanta Allah yasa wacce ya Aura satin daya wuce tanada halin kirki kuma tana kulawa dashi....tana wannan tunanin sadeeq Lamid'o yaturo k'ofar yashigo"yana rik'e da riga da hular a hannunsa"hannunsa guda na cikin Aljihun wondon jeans d'in dake jikinsa"idanuwansa sunyi jajir "fuskarsa babu Annuri"ko sallama beyiba yashigo"ita yasmeen ma bata lura da yanayin nasaba"da sauri tace"yaya sadeeq sannu da zuwa"banza yamata"ta d'ago kanta ta kallesa saidai ya riga yanufi hanyar upstairs"hakan yasa bataga fuskarsaba"maida hankalinta wajen TV d'in tayi"befi mintina 5 da hawa saman ba farooq yashigo da yunifoam Ajikinsa na islamiya ya gaida yasmeen kafin yace"Abba yace yaya yazo yanzun"d'an jim tayi sai kuma tace"jekace yana zuwa to"daga haka ta mik'e tsaye ta haura saman....sadeeq Lamid'o na tsaye gaban mirror dagashi sai d'an k'aramin boxer Ajikinsa da Alama wanka zaiyi"wayace kare a kunnansa cikin zafin rai da tsananin fusata yace"in har ka cika namiji ka fito zahiri gaba da gaba kayi Arba da mutuwarka"Ina Mai tabbatar maka da cewa nine ajalinka!! idan kafi k'arfin hukuma ni baki fi k'arfina ba"yadda ka gudu a gidan yari haka zaka koma cikin k'ask'anc....be Ida mgn ba aka yanke wayar yayi jifa da ita kan tile Adaidai lokacin yasmeen data gaji dayi masa knocking ta turo k'ofar cikin d'ari d'ari....Ido hud'u sukayi dashi yana tsaye yana huci fuskarsa babu Annuri "da sauri ta d'auke kanta gabanta na fad'uwar sbd bata tab'a ganinsa a haka ba"sau d'aya ne ta tab'a ganinsa d'aure da towel"ko kusantarta zaiyi cikin duhun ne kuma rufe Ido takeyi"miye kika shigo kimun Adak'i?"ya fad'a da k'arfi yana zaro Ido "dama Abba ne ya Aiko kazo"ke zaki d'ago ki kalleni ko saina saki kuka yanzun nan"bata kallesa d'in ba ta bud'e k'ofar ta fita da sauri tana tunanin wani yab'ata masa rai shine zai huce kanta"ko cikin parlourn bata yadda ta zauna ba ta koma d'akinta ta rufe kanta"shi kuwa kwafa yaja yazura jallabiya Ajikinsa yasakko k'asan "dama ransa yabashi guduwa d'aki zatayi"fita yayi bebi takan taba"directly side d'in su mama ya wuce"Abba na zaune a parlourn yana jiransa"da sallama ya shigo"kallo d'aya Abba ya masa ya fahimci yana cikin yanayin b'acin rai da damuwa"k'asa kan carpet ya zauna"yanada kyau idan kana fushi ka iya controlling d'in kanka"sannan nunama Abokin gaba kana fushi Akansa kuskure ne"nasami labarin Bilal ya gudu daga gidan yari"inhar bakuyi da gaske ba shima Alh lamis zai iya guduwa kenan?"sannan Abu na gaba sadeeq ka dage da Addu'a"Ina tsoron wani abu yasameka sbd mutanan nan bbu Allah Aransu",ka yawaita Addua da kulawa da kanka"Ajiyar zuciya sadeeq ya sauke Ahankali yace"karka damu Abba basu isa suyi komai ba saida izinin Allah "koda sunyi nassara Akaina nasan haka Allah yatsara mun"saidai Inaji Ajikina nine Ajalin bilal lamis.... yafad'a cikin wani yanayi yana huci"karka manta ka wuce iyakarka ta barrister"mohd ne kawai keda ikon yyi kisa bisa sharad'in wanda zai kashe d'in me laifi ne ,kuma zai cutar da mutane ko shi ya cutar dashi shine zai iya kashesa Atake sbd bama mutane kariya ko kansa"idan akawuce wannan dalilin yayi kisa tofa yanada laifi kuma za'a hukuntasa"iya Abinda zakayi kaida mohd ku fara samun damar kamashi kafin Akoma shiga kotu"badan sadeeq ya gamsuba ya Amsa dato"Abba na kallonsa yace"Ina fatan ba haka kake jema yasmeen Agidan ba cikin irin wannan yanayin ba?"ah ah Abba"to madallah zaka iya tafiya"daga haka sukayi sallama sadeeq yanufo part d'insu"kamar yafara nufar d'akin yasmeen Amma sbd yana son yayi wanka saiya wuce saman may be daga baya yayi lokacinta"saidai Abin mamaki yana shiga k'ayataccen bed room d'insa yasmeen na fitowa daga cikin toilet d'in sa"tana ganinsa tayi saurin cewa yaya sadeeq kazo kayi wankan na had'a maka ruwan wankan ,ga kaya can na fiddo maka"na fahimci kanada damuwa"yanayin Aikinku dama ya gaji irin haka"saidai ba'a nunawa mutane Ana fushi dasu"nuna musu ana fushi dasu game da wani abu da suka Aikata shike sakawa duk lokacin da suka so k'untatama mutum su Aikata hakan....da wani irin mamaki sadeeq ke sauraronta"be tab'a zaton tanada hankali da iya tsara zance haka ba"saidai yama rasa meye zaice mata "ita kuma ta d'auka wulak'ancin daya saba yimata zaiyi saita rab'a gefensa da nufin ta fita"dama k'arfin hali ne yasaka tayi kasadar shiga sabgarsa"saidai ko taku biyu batayiba sadeeq Lamid'o ya rik'e hannunta guda"ta juyo yayi saurin fisgota ta fad'o jikinsa ya rungumeta "toni yaya sadeeq ka cikani mana kaje kayi wankanka dan Allah"ta k'are maganar tana turashi"dama kinada hankali?"ah ah mahaukaciya ce ni"ta fad'a cikin gatse"okay dama mahaukaciya na Aura bansaniba?"ya k'are maganar yana janta zai nufi saman bed d'in da ita"tasaki kuka tana turjewa"wai miye haka ?"zaki nutsu ko saina b'ata miki rai ne"dan Allah ka k'yaleni kaje kayi wankanka mana"bazan yiba"yafad'a yana janta da k'arfi"ta kama kuka harda hawaye sbd taga take takensa zai iya cewa hakkinsa zai k'arba"saman bed d'in yajata suka zauna"ya d'auki wayarsa dake ringing sbd ganin mohd ne"yasmeen na ganin hankalinsa na wajen wayar ta kama yimasa chakulkuli"besan lokacin daya kama dariyaba yasaki wayar"ita kuma tayi saurin sauka daga saman bed d'in tana dariya ta zura Aguje yabar d'akin"sadeeq yaja kwafa yana fad'in wlh zaki sani tunda kin maidani Abokin wasanki"mohd dake sauraron komai ya kashe wayar yana murmushi domin ya fahimci yasmeen tafara Amfani da kissarta ta y'a mace wajen fara canza sadeeq Lamid'o"gaba d'aya jikinsa ya mutu murus bebi takan wayarba ya tashi yana kallon kayan da yasmeen ta fiddo masa harda towel "yaje ya d'auki towel d'in ya d'aura sannan ya shiga bath room d'in"da kayansa na ciki data wanke masa yafara cin karo"kauda kansa yayi yshige cikin bath tub"gaba d'aya sai yaji ya nemi b'acin ran daya shigo dashi yarasa"yafi mintina 20 Aciki sannan yafito"yana fitowa yaji babbar wayarsa na ringing "kuma ringing d'in daya sakama suhan ne"wanda yayi hakanne sbd koda yana wani Aiki ko yana cikin mutane" idan ta kirashi zai gane itace basai ya d'auka ba...... d'an murmushi yayi ya matsa gefen bed d'in ya d'auka"me makon tamasa sallama sai kukan shagwab'a data fara saki"menene? keda bakya gajiya da k'orafi "ba labari najiba