Showing 39001 words to 42000 words out of 85260 words

Chapter 14 - _NIDA_BARRISTER_SADEEQ_Complete

04 Apr 2025

7420

mayatattun idanuwansa yana kallo" sbd tsabar furgitan datayi tama manta da bbu kaya Ajikinta "shi kansa saida yaji fad'uwar gaba dayaga jinin yakuma kasa fassara meye dalilin zuwan jinin?? yasmeen kuwa data lura da yadda yake binta da wani irin kallo irin na k'urullah "saita fashe da kuka ta yayi bed sheet ta rufe jikinta tana fad'in hankalinka ya kwanta ka salwantar da cikin kamar yadda kakeda buri Abaya"na tsaneka! bana sonka!! ka b'accemun da gani an....shiru tayi tana rintse ido sbd ganin ya d'aga hannu zai mareta"jin shiru yasaka ta bud'e idon"taga yayi k'asa da hannun yana huci" bbu Alamar tsoro Atare da ita tace"idan kanayiwa Allah ka mareni ko nima ka rabani da raina mana"in sha Allah na gama zama dakai daga yau"shiru yayi yana kallon d'an bakinta"tunda yake da ita yasani bata tab'a d'aga masa murya ko masa masifa irin hakaba sai yau"kuma bata tab'a furta masa kalmar k'iyayya ba sai yau"haka nan ya tsintsi kansa da zargin be kyauta mata ba"gefen zuciyarsa kuma yana jin zafin yadda take furta masa kallamar k'i....mik'ewa tsaye yayi ya suturta jikinsa fuska Ad'aure yace"idan kin gama gayan maganar ki tashi kiyi wanka nazo na kaiki Asibiti"yana fad'in hakan yafita be jira cewar taba"yana fita ta cigaba da kukan tausayin kanta"tunda take da sadeeq bata tab'a jin zafinsa da haushinsa irin yau ba"da k'yar ta samu ta mik'e tsaye tana tafiya wawware sbd gaban nata zafi da rad'ad'i yake mata"Ahankali ta iso wajen towel nata daya fusge ta d'auka ta d'aura"cikin k'arfin hali ta cire bed sheet d'in ta canza wani"lokacin tafara jin jinin yafara bi mata gefen cinyoyi"da hanzari ta nufi bath room "tana wankan tana kuka"tana fitowa tasaka pads da kaya sbd bata zaton zata iya sallar da jini haka na fitar mata batasan kona miye ba"wankanma tayi shine sbd ta tsarkake jikinta"tana k'ok'arin saka hijab da nufin tabar masa gidansa farooq yaturo k'ofar da kula Ahannunsa ya shigo"Abin mamaki yana shigowa ciwon marar yarikice yasmeen ta duk'e k'asa dafe da wajen"da sauri farooq ya juya yafita da kular"beyi cikakken mintina 5 ba mama da sadeeq suka shigo d'akin Atare "shiya gama sallah ya fito da nufin yaga idan ta shirya su tafi Asibintin sai ga mama ta shigo bata kulashiba ta nufi d'akin "shima yabita suka shigo Atare"lokacin yasmeen na kwance ta fita daga hayyacinta"mama ta bishi da wani irin mugun kallo irin na tuhuma tace"meke damunta?"gabansa ya fad'i yama rasa meye zaice mata?"d'akkota muje Asibiti"shine Abinda ta fad'a ta fita daga cikin d'akin "lokacin yasmeen harta sume"gaba d'aya sai yaji wani iri yana fatan Allah yasa kar cikin yafita"sbd yasan idan yasmeen ta fad'i yadda Akayi za'a iya fassara da gangan yaje mata sbd cikin ya zube"yana wannan tunanin ya duk'a ya d'auketa ya fito"ko k'ofar be rufeba yanufi parking lot"ya sami mama harta shiga mota"bayan yasaka yasmeen a back sit ya shiga gdn gaba ya zauna"babu me mgn cikinsu har suka iso Asibintin, ya d'auketa suka nufi emergency room da ita shida mama"bayan ya Ajiyeta yafito yayi tsaye"idan ka kallesa a zahiri zaka zata beda wata damuwa"Amma a bad'ini yana cikin tashin hankali musammun idan yatuna Abba"fatansa Allah yabata lafiya "yana nan tsaye Anata kiraye kirayen sallar isha'i"hakan yasa yatafi masjeed "ya d'an jima sannan yadawo Amma bega Alamar mama sun fito shida gudar dr d'in dasuke kan yasmeen ba"yafi mintina 30 tsaye sannan mama ta fito"yadda sadeeq lamid'o yaga fuskar mahaifiyar tasa gabansa saida yafad'i matuk'a"dakewa kawai yayi da k'yar ya iya furta mama ya jikin nata?"ka biyoni office"shine Abinda ta fad'a ta wuce"cikin wani yanayi sadeeq yabi bayan ta zuwa cikin office d'in "tunda ya shigo ya zauna ya kasa mgn"mama kuma na danne danne a laptop "can batare data dubesaba tace"binciken mu ya nuna mana ka haike mata da yawa shiyasa Aka samu wannan matsalar"bansan da gayya kayi hakanba ko kuwa cikin rashin sani kayi"munyi iya bakin k'ok'arin mu ganin cikin be fitaba Amma abun yaci tura"sbd haka da mukayi nassarar farkawanta mun bata magani ya ida fita"saidai na kasa gane yanayin yasmeen "tunda ta farka kuka takeyi tana neman waya ta kira mahaifinta"babu irin tambayar daban mataba meya faru? saidai tace babu komai Amma tana kuka"hakan ya tabbamun da cewa ba k'aramar wahalar da y'ar mutane da gana mata Azaba kakeba "gashi har hak'urinta ya k'are tanaso tayi mgn da babanta ,may be zata sanar masa yazo yatafi da ita"kaga hankalinka saiya kwanta ko?"musammun sbd ga Aure data tattaga zaka k'ara "ina jiye maka yadda zaku kwashe da Alh muddin nasanar masa meke faruwa.....pls mama ki tsaya ki fahimceni kuma ki tambayeta kiji...rufemin baki mutumin banza! Allah yabaka mace me hakuri da ilimi ga tarbiya Amma ka kasa ka gane"sbd haka na baka nanda sati biyu zuwa ukku data warke ka bata takardan saki Allah ya had'ata da wanda yafika tunda ka nuna mu bamu isa dakai ba"Alh kuma kaida ita zakuyi masa bayanin komai"idan kuma ya tambayeni bazan b'oye masa gaskiya ba.... Amma mama waye be kuskure?"ni wlh ban mata komai da nufin na zubar mata da ciki ba"kumafa laifintane bata son yadda dani sai....sai kuma yayi shiru sbd jin nauyin Abinda zai furta"ita kanta mama tayi zaton kodai yasmeen d'in bata yadda dashi ta k'arfi yake kusantarta??"saidai ita kanta tasan burgace takeyi na sadeeq yasaketa "bazata so sadeeq yarabu da yasmeen ba, sbd tana kyautata zaton zata bama yaransu tarbiya me kyau sbd ilimin datake dashi"saidai ta Ayyana Aranta muddin yasmeen ta nuna bata son cigaba da zama da sadeeq bazata tursasataba"koda shi yana muradin cigaba da zama da ita.....dan Allah mama kiyi hak'uri itama zan rarrasheta Ai"Amma Abinda kike zargi na ba haka bane....damuwar kace wannan"ruwa baya tsami banza"yasmeen ta jima tana hakuri dakai"sbd haka na riga na gama mgn"sauran hukunci Alh zai yanke maka"idan kaga dama kaje wajen zarah ka Amso Abinci da ruwan zafi kasamemu room 10 ka kawo"dato ya Amsa ya mik'e tsaye gaba d'aya beda walwala ya fita"driver ne ke jansa yayi shiru yana tunani"gaba d'aya yarasa meyasa da mama tayi zancen yasaki yasmeen yaji fad'uwar gaba da k'in son hakan?? "bayan yanada burin hakan Aransa"wata zuciyar tace" tausayine ta baka sbd Abinda yafaru"da suhan ta shigo zaka manta da ita"da wannan tunanin suka iso gidan yakira zarah ta waya yace"ta fito yana bakin get ta kamasa Abincin "bayan ta kawo yasanar mata taje ta zauna sashensu kafin ya dawo sbd k'ofar ma Abud'e take"lokacin daya iso Asibintin mama na masallaci sbd tayi sallar isha'i data wuce batayi ba"sadeeq na rik'e da basket d'in bema bari driver ya biyosaba ya d'auki kayan da kansa"Anutse yatura k'ofar d'akin ya shigo"yasmeen na zaune ta jingina Ajikin bango"wata sister na zare mata drip"idanuwanta sunyi jajir sun kumbura"tana ganinsa taji fad'uwar gaba da b'acin rai da damuwa"dukda mama bata yimata bayanin data yima sadeeq ba"Amma yasmeen ta Alak'anta zubewar cikinta akwai saka hannunsa"tunda ta ganshi ta had'e rai"yana lura da ita "da yake d'an renin wayo ne saiya zauna gefenta yana fad'in my princess ya jikin naki?"banza ta masa dukda ga sister d'in tsaye tana kallonsu"wai fushi kikayi sbd na jima ban dawo bane?"ya k'are maganar lokacin da sister d'in ke fita"yasmeen ta matsa daga kusa dashi ido cikin ido ta kallesa tana fad'in ban tab'a jin tsanar waniba kamar yadda nakejin taka Ayanzun"sbd dalili biyu na farko kai mak'iyina ne kasha sanarmun baka sona, na biyu ka cutar dani"bana son ganinka kaje kawai dan Allah"ciki ne ko?"tunda ka zubarmun dashi shikenan kaje kaida Allah ban yafe maka ba"kuma in sha nida komawa gidanka har Abada na gama zama da kai"ta k'are maganar kuka nacin k'arfinta"kasa mgn yayi yana dai kallonta "kalmar na gama zama dakai da banyafe maka ba kaida Allah sun masa tsaye A k'ahon zuciya"saiya mik'e tsaye fuska bbu walwala ya fita"yana fitowa mama na isowa zata shiga"harara ta sakar masa ya matsa ta wuce"yasmeen najin sallamarta tayi shiru"ta kalleta taga hawaye take sharewa"gefen bed d'in ta zauna ta zuba mata Abincin daban da farfesun kaji"sannan ta had'a mata tea"Ahankali tace"kiyi hak'uri yasmeen dan Allah kinjiko?"dama haka Allah ya tsara"fatanmu Allah yabaki lafiya "kici Abinci ki k'oshi kisha magani ga pads can saiki shirya jikin naki"yayanki kuma bansan laifin daya miki ba, na tambayeki kink'i fad'amun "dukda dai bansan laifin nasaba naci masa mutunci a office sbd agyara Agaba"kuma in sha Allah can part namu zaki koma saiya gyara laifin daya miki sannan zan bashi ke"ita rayuwa hak'uri Akeyi kinji yasmeen"in sha Allah wata ran sadeeq sai yadda kikayi dashi"banaso ki sanarwa da mahaifinki komai sai Alkhairi"ita k'addara bbu wanda ya wuceta dama Allah yasa sai cikin yafita"fatana Allah yabaki lafiya kinjiko?"sosai kalaman mama suka sanyaya zuciyar yasmeen"har saida maman ta fahimci taji dad'in kalamanta "dama ita matsalarta ace ta koma gidansa"gara tavbarsa tayi nisa dashi ta haka zai gane idan tanada rana wajensa ko batada ita"saidai ita ason samunta gara kawai ta rabu dashi"Amma komai Allah ya k'addaro mata me kyau ne"tana wannan tunanin taci ta k'oshi"sannan ta shiga bayi ,bayan ta fito ta zauna mama ta dinga janta da fira sai gashi ta sake"sai wajen goma suka kwanta"mama k'asa kan darduma ta shimfid'a bargo ita kuma yasmeen saman bed..... sadeeq kuwa yanayin b'acin ran da yake ciki sbd kalaman yasmeen yasaka yakasa zuwa wajen suhan yanata ganin kiranta yamata banza....daya kwanta bacci sai yayi mafarkin gashi nan yarabu da yasmeen tanata murna harda rawa takeyi"washe gari daya tashi sosai ya dinga jin fad'uwar gaba kuma mafarkin ya tsaya masa Arai"sai wajen k'arfe 7:48 am ya nufi Asibintin yasha zazzafan wanka na suit ash colour"yana rik'e da Abin break fast nasu....yasmeen na zaune saman bed d'in da sabon wankanta"kanta bbu d'an kwali kuma A tsefe yake"tanata game da wayar mama dake hannunta"ita kuma maman na tsaye tana cire mata drip"Ahankali ya turo k'ofar ya shigo da sallama"mama ta Amsa,ya duk'a har k'asa ya gaisheta yanata kallon yasmeen saita masa kamar y'ar 10yrs"ina kwana?"ta fad'a cikin sanyayyar muryarta "ta fad'a da k'yar sbd ganin idon mahaifiyarsa"lafiya qlau ya jikin?"Alhamdulillah"daga haka duk sukayi shiru"can ya kalli yasmeen fuska bbu walwala yace "ina d'an kwalinki?"batayi mgn ba yana gefenta ta d'auka ta yafa"duk mama na lura dashi"kaje wajen d'ibar jini zasu d'ibi leda guda ak'ara mata , Ai bakayi kari ba ko?"uhmm! shikenan kaje"yasmeen ta saci kallonsa sbd ta d'auka zaiyi gaddama"saidai tana kallon nasa akayi sa'a shima ya kalleta"harara suka sakarma juna"yaja kwafa yafita"be jima da fitaba Abba da Abban mohd da mohd d'in suka zo duba yasmeen "bayan tafiyarsu mama taje ta Amso jinin Aka d'aura mata"sadeeq kuwa be biyoba ya wuce Abinsa"bema san su Abban sun zoba....yasmeen kam dad'i dataji dabai dawo ba.....wasa wasa saida yasmeen tayi kwana 2 a Asibitin y'an dubiya nata zuwa harda y'an skul nasu"sosai ta samu lafiya"Anty tazo dasu zarah Amma Anty salma da hafsat ko lek'e"saima cewa sukayi itace ta zubar da cikin sbd tayi kwalliya ta burge sadeeq "yayinda yasmeen batasan sunayiba"sadeeq lamid'o da sukeyi sbd shi baya gabanta"kullum idan yazo iya karta dashi gaisuwa shima sbd ganin idon mama"bayan hakan ko kallo be ishetaba"duk idan yazo zaita k'ok'arin mgn ta had'asu da ita" zata nuna kamarma babu ita a d'akin"hakama zaita k'ok'arin ganin sun had'a ido shima zata k'i yadda"Azatonsa wasa mama keyi sbd ganin Abba be masa maganar yasmeen ba"saida Aka sallameta yaga zarah tazo ta kwashe duk wasu kayan sawarta da books nata na makaranta sannan ya yadda mama nason rabasu"saidai bece komai ba "Abba kuma dayace miye Amfanin zuwanta nan ta zauna?"da yake mama likitace saita tsarashi ta hanyar nuna masa kulawa sosai za'a bata,kuma Ana buk'atar ta huta karta barta ta koma wajen sadeeq ta d'auki wani cikin"Abari sai bayan Amaryar sa ta tare saita koma.... Afannin suhan kuwa taji labarin zubewar cikin yasmeen Abakinsu Anty salma, taji dad'in hakan sosai"kuma ta Ayyanah Aranta koda cikin be zubeba ita da kanta zata zubar mata dashi tunda Ance gida guda zasu zauna"kamarta Aita wuce zama da kishiya gaba d'aya ballema Ace kuma gida guda zasu zauna"saidai ta tanaji uk'ubar da zatayiwa yasmeen ta yadda da kanta zatabar mata sadeeq...ganin sadeeq ya k'ara kwana 3 be zoba yaka maka cards d'in da sukayi mgn zai kawo"hakan yasaka ta k'ullacesa ,sbd Aganinta sbd yasmeen bata lafiya yak'i zuwa" tana jiran yazo ta masa gal"ni kuwa nace indai lamid'o ne kisaka niya....
da yamma bayan dawowar su yasmeen daga Asibiti yaci wanka me matuk'ar d'aukar hankalin duk wanda ya Aza Ido Akansa"yanata zuba k'amshi yashige motarsa yanufi gidansu suhan....tana zaune kan fararen kujeru daga tsakkiyar lambun gidansu "riga da wondone jikinta"wondon jeans ne yaka mata sosai da t shirt d'in "sannan Ana hango shatin k'irjinta daga gaba "kanta yasha kitson Attached "ta yafa siririn mayafi me shara shara"saidai tayi wani irin mugun kyau ,ta k'ara haske da shek'i"ga wani shegen k'amshi da takeyi tsabar gyaran da akeyi mata na jiki"musty saurayinta na b'oye na gefenta fuskarsa bbu walwala yanata kallonta kamar maye, ita kuma tana kallonsa tana yatsina fuska tace"wai miye Abin damuwa Anan musty?"dukdan sbd zanyi Auren kake haka? hmm dole kice haka mana"to bari kiji gaskiya ban Amince bayan kin Auri brr sadeeq lamid'o ki rabu dani ba"bayan ya bud'e k'ofar nima saiki barni na shiga"tana k'ok'arin mgn taji daddad'an k'amshin turaren sadeeq lamid'o.....✍️

wannan book d'in na kudine ! idan kina buk'atar siya serious regular grp 300
vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK

ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
2/26/24, 14:09 - Ummu: *Littafin kud'i ne!*
......gaban suhan ya buga da k'arfi! da sauri ta juyo bayanta ta hango sadeeq Lamid'o na doso inda suke zaune cikin tafiyarsa irinta kas'aitattun zaratan jaruman mazaje" fuskarsa Ad'aure yana bin musty da wani irin shegen kallo "yana hango Alamar rashin gaskiya Atare dashi, k'asan zuciyarsa yana tuna Ina yatab'a sanin shi?....Ajiyar zuciya suhan ta sauke ta kalli musty murya can k'asa tace"gama sadeeq d'in nan kaje zamuyi waya pls"sbd shi zaki koreni?"mitsssssuww! zancen kakeso"ta fad'a tana d'an k'ak'aro murmushi sbd isowar sadeeq wajen"sallama ya musu"taja masa kujerah tana fad'in baby zauna mana"beyi mgn ba ya zauna"kyakykyawar fuskar nan Ad'aure "musty yabashi hannu da nufin suyi musabuha"be bashiba saidai yad'aga masa hannun cikin izzah da rainin wayo "musty beyi mgn ba sbd kobe san halin sadeeq Lamid'o ba yaji mutane na fad'a"sallama yayima suhan ya wuce.....kusan second 5 da wucewarsa fuska Ad'aure yace "waye shi?"haba baby babu gaisuwa ko wani abu sai tambaya?"banza yamata"tad'an kallesa Ahankali tace "causing d'ina nane"ta fad'a tana d'aukar cards d'in daya Aza saman table d'in gabansu"yayinda shi kuma yake danna waya"fuska Ad'aure ta d'ago ta kallesa tana fad'in ka soke yaregaja and arevian night Akanme?"Eh sbd bana ra'ayi dinner kawai zan iya zuwa"haba sadeeq wai yakakeyin Abu kamar baka wayeba?"banza yamata"ta tab'e baki tana fad'in kaida mukayi dakai tun last 3 days zakazo shine sbd wata banza na kwance Agadon Asibiti shine kak'i zuwa saida Aka sallameta.... Ajiye wayar yayi yana binta da wani irin mugun kallon daya bata tsoro"ita matar tawa ce banza?"waye kike turawa yana bibiyata dani da Ahalinah??"yafad'a da wani irin tone yana tsareta da firgitattun idanuwansa "yo zancen duniya"idan kana cewa wani matarka wlh har mamaki kake bani"bafa sonta kakeba cusam.... enouph! ya katseta cikin tsawa"kinga suhan karki nemi kimun zancen banza ko kamun raini"sanin kankine ko namiji d'an uwana be isa yad'aga mun muryaba balle ke mace da zaki zauna a k'ark'ashina"duk ranar da kika koma zancen wani daya shafi Ahalinah bada Alkhairi ba wlh zan baki mugun mamaki"yasmeen d'in dakike zagi baki gabanta tama manta dake "ban tab'a jin tayi zancen kiba"sbd haka ki rik'e girmanki da mutuncin kanki"koda kinje bana son fitinah ,duk wacce ta tado mana fitinah wlh zanyi maganinta....ta tabbata dai ta fara yimaka Asiri ko?"yaja tsaki"tasaka k'aramin kukan da idan tayi yake shiga wani yanayi"gaba d'aya Anaso Ashiga tsakanina dakai baby"duk ka canzamun kana nunamun tsana....suhan ya Isa haka"kindai san Abinda nakeso da wanda bana so"dakin kiyaye zaki sameni yadda kikeso"kima dena zancen wani Asiri"shikenan Ai "Amma zaka bani million biyu nayi gyaran jiki,lalle ,kitso,da biyan kud'in d'inki"sai kuma kud'in da zamu buk'ata na hidimar komai nida friends d'ina "zaka basu million 3 kaga million biyar kenan pls baby! saurarenta kawai yakeyi da matuk'ar mamaki"sai yanzun ya lura itafa duk Abinda zatayi fafa da nuna ita watace shine burinta"ya kalleta murya bbu Alamar wasa yace"bazan bayar da million 5 ba"ba kuma sbd banida suba"meyasa bakya sara kina duban bakin gatari suhan."million biyu zan baki ki basu guda ke ki d'auki guda"nasan sun isheku komai"daga haka bazan k'araba"wai dama irin wannan Abin zakamun sadeeq?"wlh dana san zaka bani irin wannan matsalar dana fasa Auren naka....ko yanzun k'ofa Abud'e take zaki iya cewa kin fasa kiga zan fasa rayuwa ne sbd bbu ke?"bari kiji ! wlh wlh!! muddin kinaso muyi Aure girma da Arzik'i cikin so da k'auna dole kimun biyayya"meke damunki wai suhan?"wlh bana jin komai nace zan fasa bbu Abinda zai faru"yafad'a da k'arfi yana dukan table d'in gabansu"sosai ta tsorota da yanayinsa"yabi kayan jikinta da kallo ya doka tsaki "shi duk irin shigar datakeyi be tab'a jin zafin taba irin yau"ak'ule ya kalleta yace"sbd rashin yaka mata shine zaki tsaya gaban wani d'an iska Ahaka"koni be kamata na ganki Ahakaba balle wani.... "gaskiya sadeeq bakai bane"Akanme zakazo kata sani Agaba kanata mun fad'a irin haka?"saita kama kuka"yayi shiru yak'iyin mgn "daga k'arshe tayi shiru ta d'auki card d'in ta mik'e tsaye da nufin ta tafi"Ina zakije?"ka k'yaleni bbu ruwana dakai"ta k'are maganar tana sumb'ura baki"murmushi yasub'uce masa ya kawar da kansa yace zauna muyi mgn "batace komai ba ta zauna"Ahankali yace "laifinki ne suhan nasha fad'a miki ki dena Abinda bana so"yanxun zan turo miki million biyu d'in "batun fita barkatai na hanaki "fatana Ashafa fatiha kawai ko?"ta gyad'a masa kanta"beyi mgn ba yamik'e tsaye ya d'auki wayarsa yana fad'in sai Anjima "daga haka yyi gaba be jira cewar taba"suhan taja tsaki tana sauke numfashi "ita Abu biyu ne yafi bata haushi dashi, na farko kud'in dayak'i bayarwa yadda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login