Showing 42001 words to 45000 words out of 86533 words

Chapter 15 - JININMU DAYA HAUSA NOVEL

bai saurari wani abu da zata ce ba ya kashe wayarsa gaba 'daya ma duk da ya san Rufaida ba zata kira saba hasali ma yadda ya fahimta ita ba mai damuwa bace da son su ri'ka waya sosai dan sai yace tun da suka fara waya sau 'daya ta kira sa shima Ra'is ne ya dameta ta kira shi su gaisa, yana ajiye wayar sai a sannan hawaye masu zafi suka zubo masa, domin ya san zai yi wuya ya 'kara samun mace kamar Rufaida nutsatstsiya mai sanin ya kamata mai kawaici, tabbas iyayensu basu zamo masu kyautuwa a karon farko a gare shi ba, hawayen nasa ne suka ci gaba da zubowa, daga bisani ya mi'ke ya shiga ban'daki ya 'dauro alwala ya fara nafilfilo da kai kukansa ga mahaliccinmu da neman tuba izuwa ga Allah. Yana idarwa kuma ya fara azkar kafin ya 'dauki alqur'an ya ci gaba da karantawa a hankali yaji damuwarsa tana raguwa, Sai dai kuma garin kano ta masa zafi ba zai iya kwana a cikinta ba a yau , Mukhtar driver ya kira bayan ya shirya kayansa ya zo ya 'dauka yasa a boot, dakin Momy Hannatu kai tsaye Ra'uf ya nufa ya 'kwan'kwasa mata, Ta basa izinin shiga da take a falonta ta zuba ta gumi da alama ita ma tana cikin damuwa, a kujerar dake kusa da Momy ya zauna ya dubi Momy ya na cewa
"Momy dan Allah kada damuwar rabuwa ta da Rufaida ta dame ki Allah ne ya ha'damu dama, yanzu kuma Allah bai sa dama zamu yi rayuwa mai tsawo da ita ba, Amma Momy Kano ta yi min zafi haka ma Nigeria na yanke shawarar zan bi Ammi jibi mu koma Delhi tare".

"Haka ne Ra'uf Allah ya yi maka albarka, Amma ba na son ka tafi domin shi kansa Dady ba zai so haka ba bare kuma ni"

"Amin Momy, sai dai tafiyar tawa itace zata sa na manta da komai in dai Allah ya so na manta 'din dan Allah Momy ki barni na tafi".

Ba dan ta so ba ta amince da tafiyar tasa

Har mota ta raka sa ita da Husna da take magiyar kar ya tafi kallon Husna ya yi yace "banda abin Husna ai kema Dady zai kawoki Delhi idan jarabawarku ta fito".

Motar su ce ta bar gidan

Inda Momy ke hawayen rabuwa da Ra'uf 'dan 'yar uwa a gare ta ba tare da ya cika burinsa ba na auren Rufaida, Da take ganin ina ita 'din da namiji ce kuma tana da iko akan aurawa Ra'uf Rufaida da sai ta yi 'ko'karin aura masa Rufaida.

"Mukhtar ka yi kwana ina so naje Danbatta yi wa Yakumbo sallama". Ra'uf ya ce haka da sai yanzu ya tuna al'kawarin da ya yi wa Yakumbo cewa zai je mata sallama idan zai koma.

SADIYA KHALIL🖊️😊*JININMU 'DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
Wattpad Sadiya Ibrahim Khalil
SHAFI NA TALATIN DA BIYU 32

KUYI HAKURI MASOYAN LITTAFIN JININMU DAYA BAZAKU RIKA SAMUN TYPING DINA KO YAUSHE BA,SANNAN A WATTPAD BAN FARA UPDATING BA ANA UKU NAKE A WATTPAD MASU SO DAGA FARKO SU RIKA DUBAWA ACAN.IDAN SUNAYI SABODA ANAMIN MAGANA BANASAMUN DAMAR TUROWA.

Minti na da basu wuce arba'in ta sada su da garin Danbatta a, a kofar wani gida suka yi parking 'din motarsu gidan siminti ne sai dai babu shafe a kofar gidan Yara ne suka baibaye motar domin suga mai fitowa a ciki Ra'uf ne ya fito da gudu yaran da suka san shi mata da maza suka baibaye shi suna masa oyoyo, Hannun yaron ya rike suka isa kofar cikin gidan da gidan yake 'bangare uku 'bangaren yakumbo ne farko said 'bangaren kawu sunusi da na kawu Lami'do gidajen ginin zamani ne bangaren Yakumbo ya nufa kai tsaye sai da ya 'kwan'kwasa mata 'kofarta ta 'karaso 'kofar tana fa'din ince dai wannan yaron ba ne Salmanu ta'karasa maganar ta na bu'de 'kofa, Ganin Ra'uf ya sata saurin matsawa ta basa hanya ya shigo ciki cikin 'dakuna ne guda uku a biranda sai kuma kitchen da 'bandak a daga gefe da kuma 'karamin 'daki

Cikin fara'a take cewa"lale marhabin da babban ba'ko, a garin Danbatta" Tana ko'karin shinfi'damasa tabarma a saman tiles 'din dake barandar gidan da take share, Tsaftar yakumbo tana birge Ra'uf dan shi dama mutum ne mai son tsafta

Zama yayi yana cewa"Yawwa Yakumbo sarkin tsaftar garin Danbatta"

"Kai rufamin asiri ina ni ina zama mai tsaftar Danbatta gaba 'daya , Ko ka 'dauka 'kan'kantarta kamar garin jajayen fatar nan ne

" A'a Yakumbo Allah Delhi ta lin'ka Danbatta sau million ma"

"kada fa karaina Danbatta dan nanne dai asalinka ko ka'ki ko kaso"

"Eh haka ne , Amma kuma gaskiya na fa'da ta lin'ka Danbatta sau 'dari ko fiye da haka,Kuma Allah Yakumbon mu mai tsaftace "

"Ahaf ka dai fa'di gaskiyya da kace ta linka Danbatta sau million To ai yaro tsafta cikon Addini ce, Allah yasa dai Matar taka mai tsafta ce, Ba irin yaron yanzu ba masu 'dan karon son jiki, Dai dai da abinci ma 'danye suke yin shi, Bare a saran shara da wanke wanke"

Bai ce komai ba har yaron da suke shigo da kayan tsarabar da ya tsaya a hanya suka siya da Mukhtar su kashigo da ita , Mukhtar ya na ta yasu, Tsarabar ya bawa yaran suka fice da murnarsu suka nufi gida suna nunawa

Sai a sannan suka gaisa da Yakumbo
Yake tanbayarta ina Baffa

"Tun safe ya tafi gona shida kawunka sai zuwa ya manyar nan muke saran dawowar su"

"Allah ya dawo dasu lafiya , Amma ya kama ta Baba ya daina zuwa gona Amma har yau ya'ki ha'kura"
"Amin , Kai kajini da yaro idan baya motsa jikinsa wacce lafiya zaiyi jini baya yawo yadda ya kama ta"

Mukhtar da ke gefe zaune kusa da Ra'uf dariya yayi

Ya gaishe da Yakumbo yana cewa, "Kwarai kuwa yakumbo kin fa'di gaskiyya

"Ra'uf yace sai kaje kai ta zuga su"

Ruwan hannunsa ya a jiye yana kallon Mukhtar da ke gefen sa saman tabarma yace "Yakumbo bari muje muyi sallar la'asar naga a nata shiga masallaci"

"A dawo lafiya "

A 'kofar fita gidan suka ci karo da Kawu Lami'do 'kanin mahaifiyarsa, Har 'kasa su ka durkusa gurin gaishe sa, Ya amsa musu cikin sakin fuska "yana cewa a'a Ku tashi",

Bayan sun fito gidan Lami'do ya kalli Ra'uf da shima ya fito tafiya masallaci yana cewa "wata saban gani gani yaushe rabanka da zuwa Danbatta sai nace anyi shekara biyu ko anfi haka ma"

"A'a kawu shekara biyu kenan"

"A fa'dar ka ba", Mukhtar shekara nawa raban Ra'uf da zuwa"

Mukhtar yace"Kawu shekara biyu kenan"

"Wato kaima ka biye ta tashi kenan, Dan kaima kaga ba zuwa ka ke ba"

Da haka suka shiga cikin masallacin da baida nisa da gidan

Ra'uf ne ya hangi su Baffa da suke fito wa daga masallaci da fatanya a rataye a kafa'darsu, Saurin 'karasawa gurin su yayi kafin su Mukhtar su 'karasa fitowa gaishe su, cikin ha'din baki suka amsa, Inda Baffa yace

"A'a wa nake gani kamar Abdul-Ra'ufu , Sunusi dubamin shi nagani, Baffa ya fa'di haka"

"Kwarai kuwa nine babu ko kwanto Baffa"

Baffan yace "yaushe Raban duniya da aiya raye", su Kawu Lami'do na 'karasowa, Suka gaisa da Mukhtar su ka shiga cikin gidan"

'Bangaren Baffa suka shiga Fa'da suka sameta ta nayi da yaran da suka shigo 'bangarenta tana cewa su fita karsu 'batama ta gida su koma suyi wasan gurin iyayensu, Ba za'a turo mata su ba su 'bata mata gida ba iyayensu sun gyara nasu gurin, Su ko sunyi shiru suna cigaba da wasa, Da 'kara ta bisu 'kofar 'Bangaren nata inda yayi dai-dai da shigowar su Ra'uf 'din bayan su suka 'boye kada ta dokesu, Karan tayar ta koma ciki, Da yaran suka shigo Baffa da kawu Lami'do suka ajiye fatanyar a biranda, suka shiga falo suka zazzauna, Ra'uf ya kalli yaran da suke zaune kusa da shi da suke su hu'du, mata biyu maza biyu, Yace musu ku Kyale yakumbo idan na sake dawowa tare zamu tafi na maida ku gurin Ammi, Tsalle suka farayi inda Yakumbo ta shigo musu da abinci ta samesu suna tsallen murna tsaki tayi musu tace
"Wannan 'kauyawan za'a kai birni"

"Kwarai kuwa Yakumbo tunda Ammi bata da 'kananun yara ga shi ba kya barinsu suyi wasa a bangarenki"

"Ahaf ai wa'dannan yaron idan ka kaisu wannan 'kasar sai ka kirani ka fa'damin 'barnarsu kuwa"
"Ai yakumbo mun daina ki tambayi su umman mu kiji" yaran suka ha'da baki gurin cewa haka

Kawu Lami'do yace wato su salmanu ana son tafiya birnin india, ya fa'da yana dariya

Abinci suka ci Kafin ya fito su shiga zaga dangi da yawanci suna zaune a kauyen kunya kauyen Danbattan da yake yawanci kauyeb Fulani ne duk inda yaje da irin alkhairun da yake musu da yara ke raka shi a motar sa


Yakumbo ce ta kallesa da ta shigo ta zauna a falo inda Ra'uf da Baffa suke ciki Ra'uf ta duba tace "a lallai Ra'uf yau ansha yawo"

"Wallahi ko Yakumbo ai yau na zaga gari ji nake kamar duka kunya da Danbatta danginmune"

"Baffa yace kai Ra'uf Danbatta fa ba 'kauye bace mai gida nan sai kayi gaba ka tarar da wani,dama kunyan kace saina yadda

"Kyalesa dai baffa ni narasa maiyasa yaran nan suka raina Danbatta, Har da fa yaron nan Bello"
"A'a Yakumbo Allah ba mu raina Danbatta ba"

Hira suka cigaba dayi inda Baffa ya kallesa yace"ya labarin bikin naka yake , wata nawa a ka sa"

Kansa yana duban 'kasa da yake 'ko'karin maida hawayensa yace "Baffa ai an fasa biki su Abba Sule sunce bazan aure taba"

Baffa da ransa yake 'bace ya soma cewa a kanme bari na kira Sulen naji akan me? shi duk sanda yaran nan zasu nemi aure sai ya kawo wata matsalar ta daban ita kanta yarinyar da Ahmad ya aura sai da yaso kawo wata matsalar mara tushe, To inda baku yi auren ba mai yakeso kuyi"

Yakumbo tace "a'a karka kira sa tunda sunfimu iko da yarannan ka barsu kawai mu zuba musu ido sai dai mu tayasa da addu'ar Allah ya ha'dasa da wata ta gari idan kuma da rabo saika ga ya aure ta komai 'kin su da haka"

Baffa ya amsa da Amin

Tare da kallan Ra'uf ya ce "masa Ra'uf kar kuma hakan ya saka nemi yiwa 'yan uwan mahaifinka da mahaifiyarka rashin kunya ko nuna rashin darajasu domin dai ba kada kamarsu , Kuma kowa ha'kuri yake da halin 'dan uwansa wata rana sai labari"

"Insha Allah Baffa bari na je na gaida su Umma ban shiga ba 'dazu kuma gobe na ke son tafiya na kira Bello ya samamin Viza za mu tafi jibi nida Ammi zamu kwana gidan Bello daga nan saimu tafi tunda yacemin jirgin safe za mubi"

"To shikenan sai ka fito"

Da haka ya mi'ke yabar 'dakin ya sami Mukhtar suka cigaba da fira a dakin da suka sauka*JININMU 'DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
Wattpad SadiyaIbrahimKhali

SHAFINA TALATIN DA UKU 33

_Dady ya kalli Momy Hannatu yace ya banga Ra'uf a falon ba ta dubesa tace "ya tafi Kaduna zai bi yaya Ma'u su tafi tare jibi"

"Kan wannan abun zai ta fi shikenan to yafi ruwa gudu yaro mara sanin ciwan kansa akan wannan 'karamar magana ya tafi ba sani na idan yana ganin tsira zaiyi idan ya tafi kadunan

Momy shiru tayi tana jinjina al'amarin Dady lokaci 'daya ya birkice saboda san zuciya irin nasu sun hana yaro auren za'bin ransa falon Momy Hannatu ta bari ganin zaman ma baida anfani a gurin ta Dan gaskiyya saita fa'di gaskiyya indai ta zauna su kuma ta lura bamai san gaskiya a cikinsu

________________________________
Abba Aliyu da ya sami Ummi Hauwa'u a zaune gefen gado gefenta shima ya samu ya zauna da shigowar sa kenan cikin 'dakin ya dubi ummi Hauwa'un yace

" Hauwa'u magana na keso muyi bata wasa ba kuma, yanzu yaya Bukar ya sanarmin zai tafi da Rufaida ko dan ta manta da yaron nan gaba 'daya,kuma su fahimci juna itada Ahad kafin ayi aurennasu.

"Amma Abban Abdul ba ayi shawara da niba kwatsam sai azo min da maganar tafiyarta kuma harma da kudurinku na auren Ahad kana sane da kiyayyar da mahaifiyar yaron ke nunamin nida 'ya'ya na

"Ki fa'damin wake da iko da yarinyar nan ne wai"Abba Aliyu yayi firicin da alamun ransa ya soma baci

"Cikin sanyin murya tace kai ne amma gani nayi kasan komai akan zaman da mukayi nida Hajiya Jamila yanzu kuma ace Rufaida ta auri danta"

"Cikin 'bacin rai Abba Aliyu yace"ke harkinada sauran magana akan 'ya'yana kinmanta da abinda kika mana dake danasan da sa hannunki a ciki"
*****"*"
Ra'uf ya fito Cikin shirin sa shadda milk colour jikinsa 'dinkin mai yalwataccen fa'di da tayi matu'kar yi masa kyau da 'kara haska sa, ya fito da'ki da Mukhtar tuni ya fice da kayan sawarsu yasa a boot da yake waje yana jiran fitowar Ra'uf, da Baffa Ra'uf yaci karo tsakar gida yana 'ko'karin yin alwala

"Baffa sallar walhar ce"
"Eh Abdur-Ra'uf ba dai har tafiyar ta tashi ba
Eh baffa sai dai kuyi mana addu'a Allah ya 'kaddara saduwarmu"

"Baffa ya furta amin da ya ajiye butar ya 'karaso gun Ra'uf da yake 'ko'karin su fita tare da Ra'uf, Yakumbo da ta shigo gidan ta dubi Ra'uf da cewa "ba dai har ka fito ba tun yanzu, Wato da tuni sai da nazo na iske tafiyarka daga fita makwabta yi musu barka shiyasa Baraka tace na tashi kar ka tafi yanzuma take shaidamin ashe har gidan ka shiga jiya kayi musu abin arzi'ki

" A'a Yakumbo zan Shiga nayiwa su Kawu sallama , Eh mun shiga nida su salmanu da salmanun yace min mu shiga gidan 'kawar Yakumbo, sai dama muka gaisa na gane ta Gwaggo Baraka ce sai dai naga kamar ta fiki tsufa yanzu"

"Banga alama ba zaka jira dawo wataba, Abdul-Ra'uf kenan ai Baraka abar a tausaya mata ce musamman yanzu da ta 'kara tsufa a zaman 'kauye kenan da kaya basu lunka ku'din zabi ba kamar yadda suke yi a cikin birnuka,Yaran nata duk sunyi karatu amma ba wanda ya samu abinyi yanzu haka dai iro yana birni ya kammala digri yana tsaron shagon unguwar da ya zauna har ya gama karatun to gaba 'daya ku'din da yake samu basu taka kara sun karya ba kuma a hidimar iyaye suke 'karewa a hakan ma badan sun isa ba"

"Da gaske nake yakumbo ina zan tafi ban sake saki a ido ba, To amma Yakumbo mai yasa baki fa'dawa Momy ba tasa Dady ya sama masa aiki"

Baffa yace "kaga Abdul-Ra'uf ta ho ka tafi ka daka ta Yakumbon ku ba abinda zaka yi tunda dai ba ka tafi ba ta dawo ai shikenan, ka shiga ka yiwa kawun naka sallama"

Suna 'ko'karin fita Yakumbo tace "Ahaf a baki ba amma nasan da tuni ka tafi ba muyi sallama ba"

Baffa yace "saiki ta yi dai amma wannan abokin nawa ba haka yake ba"

Yakumbo tace"kana dai tare masa ne kafin mu jiku a rana"

Da haka suka 'karasa 'bangaren kawu Lami'do da suka tarar suna karyawa gaisawa su kayi sauran yaran kawu biyu duk maza suka koma gefen Ra'uf suka zauna
Umma ta ce "Amira jeki kawo wa su Baffa Abincin karin kumallonsu yanzu nake cewa ta je takaimu Ku tace sai tayi karin kumallonta zata kai muku
" Baffa yace barshi Zuwaira Yakumbo tun asuba ta 'dora sanwa saboda Abdur-Ra'uf mun 'karya tun 'dazu Allah ya yi muku albarka yasa kuma naku su yi muku"
"Umma tace" Amin Baffa"
Ra'uf ne ya dubi Amira yace "Umma Amira tayi girma kyau a ha'data aure da Bello sai mu'kara 'karfafa zumunci ni jiya ma banganta ba a gidan"

Umma tace "Ai kasan yaran yanzu basa san auren zumunci wani 'dan bayan gidan nan take so,ta je gidan kawu isuhu sai dare ta dawo"
"Kin ji Umma shine fa ke sona ba ni ba Amira ta fa'da"
Kawu Lamido yace" ina wani so da yake miki tunda kinsan tsinke baya saidawa kin 'ki ha'kura da shi, Ga makaranta saura watanni Ku gama makarantar gaba da fira mare
Baffa yace "Bar ta Lami'do da yaron nan abokin Ra'uf na birnin tarayya Abuja da ya sake dawowa zance ya turo magabatansa"
Amira ta zun'buri baki tace gaskiya Yaya baka kyautamin ba dan ni bana son wannan abokin yaya Bellon nan

Ra'uf yace "kyautawar kenan yarinya , to shikenan tunda ba kya son sa a ha'daki da Bello dan ni banida sha'awar mata biyu ai da nayi ta biyu dake"

Amira tace "Allah ya kyauta nayi auren Zumunci, ta 'daya ma ka kasa ka tsaya ruwan ido bare kayi ta biyu dani"
Ra'uf yace "eh naji gwara ni keda da zaki ba wan ba 'kanin fa"
Baffa ya ce "nidai nagama magana ta Bilal zaki aura abokin Bello"
Ra'uf yace dama Bilal ne ai da shi a kayi bikin Ahmad yaje har Sakkwato 'daurin aure yana da kirki sosai Baffa"
Amira gurin ta bari saida zasu tafi rakonsa ta fito domin rakonsa




'Bangaren Kawu Sunusi suka shiga harda su Kawu Lami'do basu jima ba a 'bangaren Kawu Sunusi ba suka fito inda suka fito tare domin ganin tafiyar sa har bakin mota suka rakasa kafin motarsu su tashi su juyo gida inda sauran yaran ke cewa yaushe zai zo 'daukarsu, Yace musu sai sun ganshi da sunga yazo tafiya ce

Misalin 'karfe biyu suka isa Kaduna ana fitowa daga masallaci Motar su ta dira sai da suka tsaya sukayi sallah a wani masallaci kafin su isa gidan

"Horn biyu a ka bu'de musu gate 'din gidan a ' Harabar gidan suka tadda Baffa Alhaji"

Da murmushi ya tari Ra'uf yana cewa "maraba da bakano kaje kano ka guji Kaduna garin gwamna"

Hakan ne yasa Ra'uf sakin ransa da tunanin ta yiyu baza'a sake masa maganar Rufaida ba yace " yawwa 'Dan tsoho mai ran 'karfe, amma wa zai 'ki Garin Gwamna"

Mukhtar ya fito a motar suka gaisa da Baffa Alhaji

Kai tsaye yana shiga falon 'dakin Ammi ya shiga da ya yi sa'ar bai sami kowa a falon ba
A zaune ya sa meta tana 'ko'karin ha'da kayanta
Sallama yayi
TaAmsa masa tare da 'dago kanta
Kafin tace "wato sai yanzu zaka zo ko ka fison tafiyar dare ko?

" a'a Ammi ki yimin afuwa ina Safiiyyan"inda ya 'Dora

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login