Showing 27001 words to 30000 words out of 86533 words

Chapter 10 - JININMU DAYA HAUSA NOVEL

addu'oi ma banbanta



"Maraba da zuwa mutanan kasar waje" Hajiya take fa'da da murmushi da ya nuna har a saman fuskarta


Mama ce da Yakumbo suka 'karaso falon suna nuna murnar ganinsa

Inda shi ko Ra'uf yayi 'dai 'dai a kujerar falon yana maida gajiya dan agajiye yake tibis yasha wahalar tafiyar


Yakumbo ta ce "wato Hannatu ta ri'ke ka sai yau kataho ko?" ta fa'da tare da 'kara sakin murmushi fuskarta

Hajiya tayi saurin karfe zancen da cewa "ahaf ai nasan za'a rina taya zan yarda da maganar ki suwaiba ace har yaron nan yayi sati biyu kice baije gurin hansatu ba, Ai nasan da cewa nice bakwa 'kaunata"

Mama ce mai cewa haba "maman jabiru ai kinsan da yaje gurin hafsatu ba ta yadda za'ayi ki'ki sani tun jiya da su Lamido suka fara isowa"

"Suwaiba babu ruwanki tun da kinfi kowa sanin abunda yaran nan nawa suke yi min duk akan 'ya'yen Hassatu yanzu zaki zomin da wata gulma"

Kafin ta 'kara cewa wani abu gaba 'dayansu suka bar falon

Suwaiba ta dubi Yakumbo tana bata ha'kuri "Hansatu kiya hakuri kema kinsan halin yayarki muyi ta yimata addu'a Allah ya shiryeta"


"Insha Allah ,amma Halayyar Yaya Hanne, Maman Hamidu badai zance komaiba tunda kince Allah amma abu tunda jajayen sahu ake har zuwa yanzu bata canza ba" inji Yakumbo wadda ita gani take abinda 'ya'yen nata ke ma yayarta ta basa yimata sai dai ita bata gani, Kullum gani take ita ake yiwa batun yanzu ba tuntuni yayarta ta ke ganin haka , kuma ita ina taga Ra'uf 'din da idanunta banda zuwan da tayi ranar da zaizo 'kasar da guntun hawaye ta 'karasa shigewa wani 'daki


Shiko Ra'uf kai tsaye 'dakinsa ya shige yanajin shigowar wasu mata falon da suka tarar da banbamin da Hajiyar keyi da cewa "Ai ni dai na kwari kaina da na ha'da zuriya da Hansatu duk an mallakemin 'ya'ya ba jabirun ba ba usman 'din ba Zuga Hajiyar suka shiga yi 'daya a ciki nacewa "Hajiya ai tunda kika bari 'ya'yanki suka auri 'ya'yan Hansatu ai sai dai kiyi ta addu'a
Dan kuwa----"

Da wannan Ra'uf ya shige cikin daga cikin dakinsa da yake cikin falon ,bai karasa jin maganarsu ba,da baya ma kaunar jinta wato har a gabansa ma maganar mahaifansa za'ayi saboda a nuna isa da fifiko akansa shida mahaifan nasa ,dafe kansa yayi da ya ke matu'kar sara masa, Bai ko tsaya watsa ruwa ba ya fada gado yana danna wayarsa, Sai da yaga kiran momy ya katse yabi kiran suka shiga fira yana bata labarin abubuwan da suka faru bayan zuwan sa Nasiha ta dinga yi masa data sanyaya zuciyar Ra'uf sosai

Jin bu'de 'kofar tare da yin sallama yasashi saurin tashi zaune ganin mai sallamar da yake jinta tamkar Ammi da Momy a zuciyarsa,Ga ma kuma kamannin da takeyi dasu,Ba wata bace illah Yakumbo,Sakkowa yayi daga gadon fuska dauke da Fara,a yana kar'bar 'katon farantin hannunta yana cewa"Kai Yakumbo irin wannan kayan sai su ya dake ki jawomana cinya"

Dariya Yakumbo tayi tace "Su dai bello sayi badai kaiba"

Ra'uf yayi murmushi yace "To ni 'din gunma indiya zamu tafi har ki warke"

"Allah ya 'kara kiyayewa" inji YAKUMBO, Ra'uf ya amsa da "Amin dai yakumbo"

Abincin ta shiga zuba masa Inda take sanar masa ita tayi girkin Dan shi ka'dai kawai


Ra'uf ne ya dubeta bayan yagama cin abincin yace "Gaskiya yakumbo kin iya girki idan nayi aure ke zaki koyama matata irin girkinki"

"Kamar gaske auren zaiyi?, Ga dai Ahmad nan zaiyi ya barka saura kuma bello shima, kai ka tsaya ruwan ido, shekarunka yakai talatin yanzu amma ka'ki yin aure,

Murmushi yayi ganin Yakumbo so take dai dan dole sai ta cikamasa shekaru takaisa inda baije ba yace " Eh yakumbo da gaske nake nasamu matar da nakeso nima yanzu, na yarda dai Ahmad yarigani aure amma bazan yarda bello yarigani ba insha Allah, ya 'dora dacewa ba ruwan ido na tsaya ba sai dai yanzu ne nasamu wadda tayi daidai da tsarina".

Inda ya shiga bawa Yakumbou labarinta, da a koda yaushe yake jin sonta aransa ya kuma kasa daina jinsa.


Ita kanta Yakumbo taji lokaci guda ga labarin Rufaidan da ABDUL-RA'UF ya bata ta shiga ranta

Karfe Biyar su Ammi suka iso Nigeria Dan-ladi driver yaje daukosu dakai tsaye gidan Malika ya fara kaisu suka aje Safiyya da itama kanta batasan shiga cikin wannan ahalin gudun kar a batawa Safiyya rai yasa Ammi ta yanke shawarar ta zauna gidan Malika duk da anan ma bata tsira ba Safiyyan amma bakamar a gidan Hajiya ba
Sunyi murnar zuwan Ammi gaba daya ahalin kasancewarta cikakkiyar yar ahalin musamnan RA'UF kamar ya shekara baiga mahaifiyarsa ba yake jin murna da kowa sai da ya fahimci haka

Zaune suke a babban falo wajen large tara na dare da yawanci bakin wasu duk sun kwanta hakan yasa"BAFFA ALHAJI ya zauna a falon cikin 'ya'yensa da matansa da jikokinsa da MA'U ke zaune cikinsu tana bawa kowa tsarabarsa da RA'UF ke taya ta godiya suke sosai "RA'UF da tun 'dazu yake son tanbayar AMMI ina Safiyya ya dan dubi AMMI yace "AMMI ina SAFIYYA ban ganta ba kuma nasan da ita za'a taho "tana gidan Malika " Jin ko haka da Hajiya tayi "yasata bata rai ta fada" wallahi MA'U indai baku fitar da wannan yarinyar daga cikin zuriyarmu ba zan sallama miki JABIRU tunda bashi ka'dai na haifa ba,Kin zamar masa fitina a rayuwarsa kin mallakesa,har wayau bazan daina danasanin ha'da zuriya da HANSATU ba"BAFFA ALHAJI jin maganganun da HAJIYA keyi marasa da'di gaban jikokinta wadanda ma busu San halitta ba da ba'a KADUNA suke zaune ba yace"Haba HANNE irin haka baikamata ba yarinyar nan SAFIYYA itama ta muce kuma 'da na kowa ne bakasan wazai tallafeka ba,kuma komai lalacewa"MA'U ma taki ce ke kina fadar haka a kanta mai zahana ki hana wasu fara"ganin fadan da BAFFA ALHAJI ke mata gaban mutanan falon yasata tashi ta fice fu kamar iska"mutanan falon da duk jikinsu yayi sanyi nan yanayin halayyar Hajiya HANNE da har yau suka kasa sabawa BAFFA ALHAJI,ya shiga kwantar musu da hankalin da nusar dasu ita haka Hajiyar take tuni batun yau ba sai dai su cigaba da hakuri da halayyarta.



HAJIYA HANNE ce ta maida dubanta ga Ammi tana cewa "yanzu Ma'u sai an je har Sokkwato saboda d'aurin auren nan?"

Ammi ta ce "to ya za'a yi Hajiya? Yanzu haka ma Ra'uf ya fa'damin sun yi nisa, kuma Ahmad ya fad'a min ba 'yan asalin Kano bane, sai dai mu taya su da addu'ar dawowarsu lafiya, amma sun fa'damin da amaryar za'a taho".

"Oho musu dai, ace mutum ba zai yi auren zumunci ba sai yaran da ba wanda yasan asalinsu"

Ammi ce ta mi'ke wannan hirar tasu da dama gaisheta taje yi ta tareta da wannan zancen tace"Hajiya bari na shiga gurin Maman Karima naji ance acen ake aikin abincin bikin"tace"Eh hakane,ki kiramin NAFI daganan"ta amsa mata "to"da haka ta fice daga dakin tayi hanyar bangaren MAMAN KARIMA 'din*JININMU 'DAYA*
Na Sadiya Ibrahim Khalil
(Sadiya Khalil)

*WANNAN SHAFIN NAKU NE MASOYAN LITTAFIN JININMU 'DAYA SAKON GAISUWARKU YANA ZUWARMIN DA ADDU'AR FATAN ALKHAIRIN DA KUKE MIN ALLAH YA BAR KAUNA😊😊*
Page 20
Abba Aliyu da Sallama a bakinsa ya qarasa shiga cikin falonsa kallonsa Ummi Hauwa'u tayi kafin tace "sannu da zuwa Abban ABDUL-RAFI" ya amsa da "yawwa Hauwa"mikewa tayi daga zaman da tayi daga baiwa RA'IS abincin da take ta tashi ta nufi kitchen RA'IS gurin mahaifinsa kai tsaye ya nufa ya daukesa yana masa wasa mintina kalilan UMMI HAUWA'U ta daw falon da sallama da ruwa dauke a hannunta da Kofi saida ya sha ruwan kafin ta kallesa cikin nutsuwa tace
" Ya naga ka dawo gida tun yanzu ina meeting(taro)da za kuyi"
"Hmm kedai bari,ai sam director bai kyauta ba tun fitar da nayi muna can jiransa,bai zoba sai yanzu yayi mana waya ya fadama bazai samu halartar taronba?"
"Kai amma bai kyauta ba amma kila yana da uziri amma da ya fadamuku tun wuri kaga ai da muntafi bikin nan"
"Kedai bari HAUWA'U ni kaina abinda ya qara batamin rai kenan naso zuwa daurin auren SAMIHA ko dan yadda iyayenta da ita kanta suka dauke mu"
"Wallahi kuwa to ya za'ayi haka Allah yaso,amma gasu ABDUL-RAFI sun wakilcemu ai"
"Hakane kunyi ko waya da yaron ma kuwa?"
"Eh munyi waya dazu da ABDUL-RAFI yace,a lokacin shirye-shiryen 'daurin auren ake"
"Allah sarki ,dama 'daurin auren Safiya ne"
"Eh ai naji suna KADUNA za'a kai SAMIHAN kuma da 'yan daurin auren zasu tafi,na dauka kaga Invitation 'din ai,na gansa akan lokar 'dakinka jiya"
"A'a bangan shiba ina Sauri zan fita SAMIR ya kawomin , ina ga yaron ne yake aiki acan KADUNAN,amma ai shi iyayen yaron ai anan suke da zama,baban yaron ICP ne na yanzu"
Murmushi tayi kawai tace"Eh nagani a Invitation Allah ya sanya Alkhairi,ya basu zaman lafiya"
"Amin,ina sauran yaran ne"
"Suna ciki amma RUMAISA ta fita na aiketa gidan HAJIYA RABI"
"OK" daga haka suka cigaba da firarsu
********
'Karfe 11 na safe
Aka daura auren SAUDAT HASHIM SARKI da MUJAHID AHMAD TIJJANI
sai SAMIHA HASHIM SARKI da AHMAD USMAN MAHMUD 'DANBATTA

Shigowar amaren cikin falon da suke tare da 'yan uwansu da suke 'yam mata da kawayensu 'dai'daiku da suka taho tare daga kano da a kawayen SAMIHA RUFAIDA ce da NASIBA kawai sukazo bikin,cikin ankonsu suke na atamfa da yayi musu kyau gurin da su MOMY MARYAM suke zaune cikin falon itada 'yan uwa da abokan arziki yasa su karasawa suka gaggashesu amsawa sukayi da murmushi kan fuskar kowaccensu suna yi musu addu'ar fatan Alkhairi da haka suka mike don barin gurin MOMY MARYAM ta tsaida RUFAIDA da cewa"YAYA BILKI kinga 'diyar HAUWA'UN RUFAIDA da nake ce miki kawar SAMIHA"
"Masha Allah gatanan 'yar kyakkyawa har kama suke da SAMIHA,banga mamarta taba"
mikewa RUFAIDA tayi da wannan zancen ba tare da taji mai MOMY MARYAM da sauran matan dakin zasu fada ba
***
Amaren ne suke karasowa jikin motar da angwayen su AHMAD da abokansa ciki yarda RA'UF da suka fito don gaisawa da yi musu iso cikin gidan su SAMIHA suci abinci ayi photuna daganan kasancewar gidansu SAMIHA babban gida ne kuma gidan sarauta mai 'bangare 'bangare
*AHMAD RA'UF yake tabawa yana nuna masa amaryar da kawayenta da suke tahowa da ya kasa cire idanunsa ga RUFAIDA da take tsakiyarsu da kallo daya yayi ganeta itace suka taba haduwa waccen ranar a store dan kullum saiya tuno fuskartabanda addu'ar da kullum yake Allah ya qara hadasu ,AHMAD ne kallesa ya katse masa tunanin da take da fadin
"YAYA RA'UF ya ya dai meya faru"
"Kalli waccen yarinya ta tsakiya da suke tahowa da amaryarka"
AHMAD fuskarsa ya 'daga ya kallesu da RUFAIDA ya gani ita ce a tsakiya a layin da suka yi,da kafin yace wani abu suka karaso wajen da sallamarsu,amsa musu sukayi gaba 'dayansu abokan angon gaisawa suka yi da RA'UF ya kafe RUFAIDA da kallo ko 'kiftawa ba yayi tunda suka iso gurin da suke
"Amarya bata laifi kota kashe 'dan masu gida"abokan AHMAD suka fa'da cikin tsokana da fara'arsu sukai maganar"
Kawayen SAMIHA sukayi saurin cewa
"Bata kashe ba dai da har gida za'a korota karewar laifi ma"
"Haka dai kuka ce" inji BELLO da yake cikinsu RUFAIDA data 'dago kai taga mai son karyata maganarsu anan suka hada ido da RA'UF taga iron kallon da yake mata tayi saurin dauke kanta zuwa 'kasa"
NASIBA da itace tasa baki a maganar yanzu tace
"Ai haka ne, yanzu dai mu dai mu shiga daga ciki,kuci abinci da lemo kun shawo tafiya"
Murmushi su AHMAD da abokansa sukayi kawai,su RUFAIDA ne da amarya SAMIHA suka yi gaba ,angwayen suka take musu baya da RA'UF a cikinsu gani yake hatta AHMAD bai kai sa murna ba shida yake ango danshi yau muradin zuciyarsa ya gama a nasa tunanin.*JININMU 'DAYA*

*SADIYA IBAHIM KHALIL*
*(SADIYA KHALIL)*

*WANNAN SHAFIN NAKI NE AYISH HUMAIRA MUHAMMAD MY SISI INA MIKI BARKA DA DAWOWA ONLINE KIYI YADDA KIKESO DA WANNAN SHAHIN DONKE AKAI KAWAI*

PAGE 21

Zaune suke angwayen a falon hankalin kowa naga abincin da aka kawo musu Friend rice da sinasir sai kayen soyeye soye,Ahmad Ra'uf ya duba da yake kokarin kai ruwa bakinsa yace
"AHMAD kasan yarinyar dana nunama 'dazu ta tsakiyar SAMIHA naji har magana kayi mata" yayi maganar yana aje gorar ruwan da ya bude yasha a kasan carpet
"Eh nasanta Cousin's din mata tace Rufaida sunanta lafiya maiya faru"ya karasa maganar yana kallon RA'UF kallon rashin fahimtar a inda ya santa"
"Bakomai nasanta ne"
Murmushi yayi Ahmad kana yace
"Malam kodai itace kayi gamo da ita kwanaki kafadamin gaskiya kar naki baka ita tinda kasan kanwar matatace kuma kawarta"
"Wallahi baka isa Ba idanma kace haka toni da nake matsayin kaninsa zan tsaya masa ayi komai" cewar Bello dayake kai lomar doughnut bakinsa
"Yawwa fadamasa dai ni dan Allah kiramin yarinyarma please (yi hakuri)"
Abokan ango sukayi dariya da yawanci abokan sune duka suka ce
"Kai Ra'uf ai duk saurin unguwar zoma tabari a haihu"
Ahmad yace
"Kuma kwa fadamasa dai"
"Kaga idan zaka kiramin ita kakirata hakurin kwana nawa kakeso nakuma yi,vayan wanda nayi a baya" Ra'uf ya karasa fadar haka yana daukar wayar Ahmad ya danna yasa a kunne
"Tunda bazaka kira ni bari nakira"
Abokan nasu dariya suka sa ciki harda Bello da yaji suna neman kwafsa masa ya mike yabar musu falon ya nufi kofar fita daga falon jin an 'daga yasa shi tsayawa daga kofar falon
"Assalamu Alaikum,Amarya Samiy" Yayi saurin katse maganar da Samiha keyi
A daya bangaren aka fara magana
"Wa'alaikumus salam,Yaya Ra'uf" saboda ta fahimci ba Bello bane tasan idanko vashi bane to baya wuce dayan biyu ko Ra'uf
Murmushi Ra'uf yayi jin ta gane muryasa ya katse tunaninta da cewa
"Dan Allah daya daga cikin kawayenki mukeso tazo"
"To shikenan bari naturo ma wata"
Da haka ya katse wayar sai da ya katse ya fara tunanin maiyasa ma baice Rufaida yakeso tazo ba tsaki yaja yana addu'ar Allah yasa Rufaida ce zata zo,da wannan tunanin ya koma cikin falon abokan nasu suka cigaba da zolayarsa shi kuma murmushi kawai yake abinsa

*****
Rufaida Samiha ta kalla bayan ta gama wayar da take kusa da ita gefen gado dasu biyune kawai a dakin ta soma magana da cewa
"Rufy Dan Allah kije gurinsu Ahmad,yanzu Brother dinsa (dan uwansa)ya kirani sunason ganin daya daga cikin kawayena,kinga suku ma sauran sun tafi gidansu Zainab din Momy Balki"
"Eh hakane,amma banda haka Allah Ba inda zani" ta karashe maganar tana mikewa
"Maiyayi zafi kuma haka Rufaida ko Ahmad yayi miki laifine"
"Ko daya wallahi baimin laifi Ba illah dai abokansa kallo garesu musamman wani wanda ya dan darasu haske"
Murmushi Samiha tayi tare da fadin
"Nidai ki taimaka kije karsu sakemin waya"
"Naji" da haka tasakai tavar dakin Samiha ta bita da murmushi har ranta takeson kawarta sai dai gashi sunkusa rabuwa har watarana ta yiyu ko wacce tayi wuyar gani
********
A hankali take tafiya cikin nutsuwa harta kusa isa kofar falon Ra'uf da ya hangota Kasancewarsa yana waje yana amsa waya wayar yayi saurin katsewa ya karaso yasha gabanta da murmushi a fuskarsa da gavatarmata da sallama dago idonta tayi ta dubeshi kallo daya tayi masa ta shaidashi shine mai kallon ta dazu gefe takoma ta amsa masa sallamar ta sake gaishesa karo na biyu ya 'dan murmusa kana ya soma magana
"Gimbiya Rufy ya hidindimun biki"
"Alhamdulillah"
"Kinko shaida fuskata koda yake ta yiyu in ban sace zuciyarki ba, bare harki matsawa zuciyarki gurin neman wannan barawan"
Murmushi tayi ka'dan
"Gaskiya ban shaidaka ba ,nashiga goma satar me nayi maka dan Allah ka fahimtar dani"
Shima murmushi yayi
"Kar dai na tsorata Gimbiyar matan ,kin tuna kwanakin baya a store ban riqe dai sunan store din ba, munyi karo dake a lokacin to tundaga nan kikayimin satar zuciyata"
Sai a lokacin ta tunosa ta fahimci kallon sani yake mata a dazu sai dai ita a dazu bata ganesa ba"
"Naganeka "
"Yawwa Rufee,karna cika ki da surutu bari na gabatar miki da kaina ni sunana AbdulRa'uf Jabir Danbatta cousins din Ahmad ne ma'ana dai (Abbansa kanin Abbana ne) haka momynsa kanwar momyna ne ina Delhi da zama da mahaifana kuma ina aiki acan,a takaice kenan ,naganki a tun wannan lokacin naji ina qaunar ki kasance mata a gareni insha Allah ina fatan ki amince dani kuma da yiwa kaina fatan Allah yasa bairigani ba,dukda bazanso haka ba amma dai zan baiwa zuciyata hakuri idan har haka ya kasance"
Murmushi ya subuce mata jin karashen maganar tasa tayi shiru ba tare da tace komaiba
"Kinyi shiru ko dai zuciyarki bata amince dani"
Sauya maganar tayi
"Bari na karasa cikin falon,inda ake kira na"
Zaro ido yayi
"Wato ba zaki amsamin maganarba kika canzamin da wata,to gurin wa zaki cikin bayan ga basaraken dake kiran gimbiyarsa to tunda ta gansa babu abinda yayi saura ko"
Jinjina karfin halin Ra'uf itadai Rufaida takeyi wato daga haduwar sau daya zata amince masa
"Kinyi shiru gimbiya"
"Kaya hakuri..." Bai barta ta karasa maganar ba ya zaro idanunsa duka
"Hakurin me harkinsa zuciya tayi raunin"
Ita dai murmushi tayi
"A'a cewa zanyi zan koma ciki tunda kafadamin sakon"
"To naji vani number dinki yanzu"
"Banida waya"
Bata jira cewarsa ba tabar gurin dan ta lura baida niyyar kyaleta ta tafi
Ganin tabar gurin yasa shi murmushi ya kyaleta dan yana ganin alamun nasara ko a yanzu,yana sane da balallai tayi masa doguwar magana ba kasancewar ba gida yazo ya je ya sametaba da haka ya bar gurin ya koma falon

*****
"Angon gobe gaskiya gayu bikin Ahmad mu sashi a tarihi" abokansa da suke hangosa shida Rufaida ta kofar falon da take a bude sukayi hanzari fada yana shigowa falon
Murmushi yayi
"Kai Guys haka zaku ce"
"Eh mana haka ne,ko ba haka bane gayu" inji daya daga cikinsu ya fa'di hakan
"Khalifa ka kiyayeni"
"To tuba nake ranka ya dade"
Ahmad da ya shiga firar a yanzu ya soma cewa
"Dan uwa Allah kayi sa'ar mace"
Khalifa yasa baki karo na biyu
"Gaskiya ne Ahmad babyn kyakkyawa tayi ba karya"
"To naji dai,yanzu dai ka kira mana amarya muyi hutunan ayi shirin tafiya da amarya na matsu na koma KD"
"Kadai fadi gaskiya malam Ra' uf kodai so kake muyi mu koma gobe a dawo bikinka ne"inji Bello
Tsaki yayi ya sake ficewa daga falon dan yasan zasu takurasa ne da magana indai ya cigaba da zama sukayi dariya ganin ya bar musu dakin.



*SADIYA KHALIL😊😊**JININMU DAYA*
By Sadiya Ibrahim khalil (Sadiya Khalil)

*Wannan shafin naku ne group mai albarka Sadiya khalil group Allah ya sadamu da alkhairi ya bamu ikon rubuta abinda zai anfanemu duniya da lahira Amin kuyi yadda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login