Showing 45001 words to 48000 words out of 86533 words

Chapter 16 - JININMU DAYA HAUSA NOVEL

da gaishe ta amsa gaisuwar
ta dora da cewa tana gidan Malika sai zamu tafi zamu dauketa mu wuce,na kirkira ka kashe wayoyinka tun jiya nake 'ko'karin kiranka ba ta shiga ba saboda Momynku ta cemin ka taho"

"Eh Ammi na biya ta Danbatta nama su Baffa sallama, tun a Danbattar na kunna wayar da muka je amma babu network mai 'karfin da zai yi kira"

Ammi cikin nuna damuwa a kan fuskarsa da tausayin yaron nata mai tsananin biyayya a gare su da bai kamata kan wani banzan dalili a hanasa za'bin ran sa ba da ta tabbatar ba wani 'kau'karar dalili ba ne amma an rabasa da Rufaida saboda suna so suna na isar su akan Ra'uf dan datasan abinda zata tarar ke nan da bata zo nigeria ba magana ta soma yi tana cewa "Ra'uf dan Allah kada Rabuwarka da Rufaida ya janyo wani sauyi daga rayuwarka dama wani lokacin sai ka rasa wani abun kake samun wani abun a rayuwa"

"Insha Allah Ammi"
Ammi tace "yawwa Ra'uf"

Amma Ammi Su Abba Suleh sun fa'damiki wani abu ne da yasa suka hanani auren ta

Kai ta girgiza tace "a'a ko 'daya ba su fa'da mana komai ba sunce dai an yi musu wula'kanci da ni narasa kalar wula'kancin amma hajiya ta 'dauki zafi da haka sosai sai dai kayi ha'kuri"

SADIYA KHALIL🖊️😊*❣️JININMU 'DAYA*❣️
BY SADIYA IBRAHIM KHALIL

HAPPY SALLAH ALL MUSLIM UMMAH ALLAH YA MAIMAITA MANA🤲🏼

34.
34
*Rufaida muddin kikace bazaki bi Abba Bukar ba kinada tabbacin ni zaki jawa zagi bakowa ba,haka koda Aliyu bai kasance miji gareni ba duk abinda na mallaka suka nuna suna so nawa zan basu,saboda sun nunamin soyayya kamar wadanda muke ciki 'daya bare ke din mallakinsuce duk abinda suka yanke gareki bazance don meba"
"Rufaida da take zaune jikin mahaifiyarta saman gado da tagama jin kalaman Ummin nasu ta soma magana"
"Ummi naji zanbi Abba Bukar amma banason auren Yaya Ahad tunda sunqi aurena da Ra'uf naji na hakura amma wallahi banason auren nan Ummi ,nasan bazanyi auren farin ciki ba don Allah Ummi kice karsu auramin shi"tayi maganar tana fashewa da kuka
Lallashinta Ummi Hauwa'u ta fara da itama hawayen take zubarwa ita kanta batason 'yarta tayi rayuwa irin wadda tayi a baya,da tasan saboda Hajiya Jamila ne yasa batason auren na Ahad din badan tana kin Ahad dinba,saida Ummi Hauwa'u taji Rufaida tayi shiru ta soma magana
" Haba Rufaida ya kike abu kamar ba musulmaba bakida masaniyar ko Ahad shine zaifi zama miki Alkhairi a rayuwarki tanan gaba idan kina wannan maganar to kenan imaninki ya soma rauni kenan ko,kuma ki tuna da cewa duk Wanda Allah yaso da Alkhairi saikiga ya jarabceshi da wata musibar,idan bakiyi kokari kin cinye jarabawarki ba mai kikeso kiyi a duniya,ko kinfiso ke rayuwarki ta kasance kullum cikin jin dadi ki tuna da za'a tona zukatan wasu aji meke cikinsu da kinyiwa Allah godiya akan ke taki jarabawar,ki fahimci cewa Alkaluma sun riga da sun bushe babu wanda ya isa ya kauda kaddarorin rayuwarsa domin sun rubutu akan alkalamin da baya gogewa,kowa kika gani kafin ya samu abinda yakeso saida yasha wahala ,nasan kinason Ra'uf tuni batun yauba nasan da haka,amma hakuri zakiyi abubuwan da son zuciya ya zama silarsu ya farraqa soyayyarku,maza ki share hawayenki ki cigaba da kaiwa Allah kukanki.
"Dago ido Rufaida tayi tana share hawayen fuskarta ta ta jinjina lalle mahaifiyarta uwace mai girma a rayuwarsu lallai mahaifiyarta ta samu tarbiyya daga iyayenta gashi har tasamu nutsuwa da kalaman mahaifiyartata dole mahaifinta ya sota fiye da tunanin dukkan mai tunani da duk wanda ya tabata a dangi to sai Inda karfinsa ya kare dukda dangin nasu dayane,saidai abu daya daya shige mata duhu sanin waye 'Danbatta Family da zuriyarsu basa son haduwa da zuriyar Danbattan.
Murmushin karfin hali Rufaida ta qirqira ta dora ido ga mahaifiyartata
" Ummi na amince da dukkan maganganunki kuma na yarda da nasiharki gareni,kuma nayi alkawarun bin abinda kikace,saidai ki fadamin maiyasa don Ra'uf ya fito data zuriyar Danbatta bazaku auramin shi ba"
Murmushi Ummi Hauwa'u tayi ta dafa Rufaida
"Ni kaina bansan dalili ba mahaifinkine da Abba Bukar kawai suka sani amma ki dauka a ranki baki taba jin sunan 'Danbatta Family ba har abada,amma ni bance kimanta da masoyanki na gaskiya ba har karshen rayuwarki ba,kinga maza taso ki shirya kayanki mubar wannan maganar kinsan Abba Bukar bayasan jira.
Jiki ba kwari ta mike da tasan lallai akwai rina a kaba Ummince dai bazata Sanar mata ba itama kuma batasan tilastawa Ummin tasu
Da haka suka Shiga loda kayannata a trolley da Ummi Hauwa'u ke tayata sunayi tana sake yi mata nasiha
10pm
Motar Abba Bukar ta tashi da Rufaida take rungume da Umminsu da Rumaisa da take ji a ranta tamkar rabuwarsu kenan ,bazasu kara haduwa ba,shikansa Abdul kuka yake yanasan kanwarsa gashi an rabata da abinda take so za'a kaita inda ba'asonsu don zalinci ji yake aransa ina ma shi wani ne wallahi da bazata bisu ba hatta Umminsu da kannensa bazasu cigaba da zama a tare da Abbansu ba da sunaji suna gani ake fadawa mahaifiyarsu bakaken maganganu don kawai anga ita din mai hakuri ce.
Horn din da Abba Bukar yayi ne yasa Rufaida Shiga gaban motar ya tayar tana hange 'yan uwanta da Umminsu suna hawayen rabuwa da ita da dagamata hannu da hatta mahaifinsu ta hangi siririyar kwallar da dafito daga idanunsa Abdul Rashid daya bude musu gate din Hawayen yake da daga musu hannu har waje ya fito saida yaga baya hangen motarsu ya koma gida itama waigensa take har suna bacewa ganinta sunyi matukar sabo da da 'yan uwanta tare sukai rayuwa tun daga mara dadi har zuwa yanzu da suke ganiyar yin mai dadi da Umminsu take gine dasu ko yaushe akan nuna musu su kaunaci junansu tunanin baya kawai Rufaida ta lula tana hango komai kamar a mafarki.
2pm
Suka karaso Zariya da kai tsaye gidan Abba Bukar suka nufa inda yayi horn mai gadi ya bude musu gate din Abba Bukar ya dosa hancin motarsa cikin gidan mai gadi da take masa Sannu da zuwa ya dagawa hannu yayi parking inda aka tanada wajen aje motoci ya fito ba shiri Rufaida ta fito itama tana sake duban gidan da duk sanda ta shigo tarihin rayuwarsu a gidan yake zuwar mata kamar yanzu abin me faruwa tsoro da fargaba ya shiga yawo a cikin zuciyarta to yau karo na biyu da tazo gidan da zama wacce irin rayuwa zatayi kafin lokacin bikin nasu da Ahad yazo tasani ta bayance dai rayuwartasu zatayi koma ta linka ta bayan tunda kaddara tasa zata auri dan matarda take da cikakken iko da isa a gidan na Wan mahaifinnata.
Maganar Abba Bukar yasata dawowa daga dogon tunaninta inda yace
"Shiga cikin gidan kafin Dan-liti (mai gadi)ya shigo miki da kayan naki"
Da to ta bisa dan ta fara tafiya cikin sanyi ta is a kofar falon bata sami kowa a falonba dalilin daya sata jin dadi kenan harta isa kofar da zata sadata da bangaren da shine nasu dasuka zauna a gidan da har yanzu yake nasu da idan sunzo gidan shine gurin zamansu
A share bangaren yake kai kace wani na zama a cikinsa.
Sallamar Baba Dan-liti da Abba Bukar yayi masa izinin shiga ya kaiwa Rufaida kayanta yasashi shiga,don iyakacin aikinsa gate.
Amsa masa Rufaidan tayi ta gaishesa ya amsa ya aje mata kayan a falon ya fito.
Jakar dake zagale a kafadarta ta aje saman kujera tareda cire hijabin jikinta ta zauna tana maida gajiya tana mai cigaba da tunanin rayuwa ganin tunanin bazai mata ba yasa ta mike tayo alwala ta tada sallah ta dade tana addu'o'i kafin ta mike tabar dakin da nufar dakin matan gidan gaishesu
"Wawa sakarai dama don haka kace bakasan Rukayya don kawai kanason macen da banbanci dake tsakaninku mai girman da bansan adadinsa ba ne, Rufaida da take kokarin tura kofar dakin Hajiya Jamila tajiyo furucin nata da dama tasan fiye da haka saita faru bama ga Ahad dinba har gareta tunda zai aureta,gudun hakan yasa take tsoron auren Ra'uf dukda bawai sonsane itama batayi ba saidai wannan matsalar take hangowa,da ita kullum tunaninta sanin banbancin dake tsakaninsu dasu Ahad da har yau takasa fahimtar menene banbancin jin furucin Ahad ya katse mata tunaninta"
"Umma inasan Rufaida tunda tazo duniya banasan Rukayya da soyayyar aure, amma kifadamin banbancin mu ko zaisa ya zama silar hakurata da auren Rufaidan amma ni nasan Rufaida 'yace kamar kowa,bana haufi akan bazata cutar dani ba har ma daku"
"Dakata Malam ai banbancinku sananne ne da kowa ma ya sanshi sakarci da wauta ne yasa kaika manta dashi kuma tunda ka kafe sai ka aureni Rufaida to nima zan kafe a au.....
Bata tsaya jin karashen maganar Hajiya Jamilarba tabar kofar dakin nata tana kokarin hana hawayen idanunta fitowa,
Hajiya Jamila mutuniyar garin Nasarawa state ce acan Abba Bukar da yaje bautar kasarsa ya ganta ya Aurota acan
yaranta biyar Abdul-Ahad ne babba a gidanma gaba daya sai,AbdulMalik,Abdul-Jabbar,AbdusSalam,Wasila
Kai tsaye dakin Hajiya Kubra ta shiga cikin sakin fuska suka gaisa ta zubo mata abinci taci tana sake nusar da Rufaida yanayin rayuwa Hajiya Kubra mutuniyar kirkice auren zumunci sukayi da Abba Bukar 'yar cikin garin zariyace, kuma aurenso da kauna da ba hadasu akaiba Allah ne ya hadasu da take mutuwar son Abba Bukar dalilin dayasa takesan kowa nasa kenan dukda itada Abba Bukar din abu dayane,amma sonsa ne yake tasiri a zuciyarta dayake kara mata kaunar 'yan uwansa dukda itama din nata ne,amma bata banbanta wadannan sunfi kusanci gareta indai akan abinda ya shafi mai gidan nata ne
yaran Hajiya Kubra a lokacin Hassan,Hussaini,Aliyu,Umar,Usman.
cikin kwarin gwiwa Rufaida ta fito ta shiga 'dakin Aunty Amina suka gaisa da itama macace mai kirki saidai batada yawan surutu amma dai tanada kirki batada yawan magana bare harta fadawa 'yan uwan Abba Bukar din wata magana mara dadi rashin maganarta ne yasa wasu ke ganin batada kirki amma shi Abba Bukar sam baya ganin haka don ta fadamasa laifin da nasa suka mata to lallai za'a dade yaranta biyu a lokacin don itace amarya
Sadiq,Ubaidullah da take goyo
Tana fitowa ta shiga dakin Hajiya Jamila da ko sallamar da tayi bata amsa ba haka ma gaisuwarta haka ta gama zama ta fito da Hajiya Jamila ta biyo ta dajan tsaki.*❣️JININMU 'DAYA❣️*
BY SADIYA IBRAHIM KHALIL

*HAPPY SALLAH ALLAH YA MAIMAITAMANA AMIN*

35
*****
Kukan da take ta tsayar ta maida kallonta ga wayarta ganin number din Samiha yasata saurin daukar wayar da sallamarta saida suka gaisa Samiha tayi gyaran muryar ta soma magana
"Rufaida banji dadin abinda su Abba suka ma danginsu Ahmad ba sunsan tun farko yaya Ahad sukeso su aura suka boye masa,bakiji haushin da Ahmad yaji ba dan sai alokacin da aka hana Ra'uf aurenki ya fahimci bamuda alaka dake"
Rufaida jin Samiha tayi shiru yasata kokarin cewa
"Ni kaina Samiha banso abinda aka ma danginsu Ra'uf ba ga uwa uba inasan Ra'uf amma iyayena sun rusamin burina,batare da nasan dalili ba, sun fadawa Ummi maganganu mara sa dadi sai kace itadin Ba jininsu bace akan kawai suna zargin da hadin bakintama Ra'uf yazo neman aurena,gashi suna kokarin tilastani auren Yaya Ahad dakema kina sane da irin kiyayyar da Umma Jamila ke gwada ma...kukan da take makalewa ne ya kufce mata,Samiha da takejin kukan kawarta ta har saman kanta ta soma rarrashinta
" Haba Rufaida kukan meye haka nima Idan kinayi wallahi nima yi zanyi ke kawatace danike jinki a jinin jikina wallahi son danake miki ko Yaya Sauda bana masa kwatankwancinsa yi hakuri daina kukan kinji kawata dan Allah"
Kukan Rufaida ta tsayar Kafin ta cigaba da magana
"Samiha busu kyautaminba nida Ummi sun rabani da mutumin Dana fara so a duniya akarshe sun yiwa Ummi kazafi sun muzanta ta muna kallo bayadda muka iya nima suna kokarin hadani da wani tashin hankali Abba yanaji bai hana Abba Bukar yanke wannan shawararba gaskiya bazan iya....Samiha bata bari Rufaida takarasa maganar da takeson yiba tayi saurin dakatar da ita da cewa"
Haba Rufaida karki furta wata mummunar kalma ga iyayenki dukda nasan busu kyautamiki ba kiyi kokari ki manta komai ki tuno da abubuwan da suka miki tunda ga haihuwarki har zuwa yau sine suka maidake cikakkiyar mutun suka baki tarbiya da har Ra'uf ya ganta tattare dake yaso aureki karki manta hakan ki fadi mumnunan kalma garesu ,nasan abinda suka yiwa Ummin busu kyautaba amma ya zakiyi ita ta suce,saidai fadan ne da sukai mata ni mamaki ma ya bani itada bata sansu ba amma sai a huce akanta amma komai sukayi mata tasu ce dai,sannan batun auren yaya Ahad ki fahimci bad Umma Jamila zaki zauna ba sai kinje inda take ko wani Abu yakawota gunki zata fadamiki wata magana tunda yaya Ahad nasanki ai shikenan.
Rufaida da.maganganun Samiha suka shigeta
"Gaskiya nagode kawa tagari"
Babu komai kinfi ganan Rufaida ke kamar jinin jikina ce"Ahmad da ya samu Samiha a falo yaji tana cewa Rufaida ya fahimci da ita suke wayar ya umarci ta bata wayar su gaisa danshi bayida haufi akan Rufaida yasan bata da laifi
Bayan sun gaisa da Rufaida da kamar da zata cewa Samiha karta basa wayar sai kuma taga bata kyautaba tunda shi da akamusu laifi bai kullaceta ba sai ita,jin muryar Ahmad yasata dawowa daga tunaninta
"Amaryar Ahad,ashe dama yayanki zaki aura shine aka mana kora da hali ko?"
Yadda yayi maganar yasa Rufaida ta fahimci bai dauki zafi ba shi,yasa itama cikin wasa ta mayar masa da amsa
"Kai Yaya Ahmad ba laifinmu bane laifin 'Danbata Family ne"
Zaro ido yayi baiyi mamakin jin sunan a bakinta ba saboda Samiha
"To ke kuma ya sunan naku Family da sainace sune masu laifin"
"Tafida, yaji ta fada da tana fadar hakan ta yanke wayar ta daga Koran Ummi da take mata
" to sune masu laifin"Ahmad ya fadi hakan,jin bata amsa ba ya sashi duba wayar ganin takatse kiran Samiha ya mikawa wayar
"Ungo kawarki ta katse wayar ta soma fahimtar munfisu gaskiya" ya karasa maganar yana murmushi ya shige ciki.
Suna gama wayar da Ummi da kannenta da suke fadar yadda sukayi kewarta sakar zuci tafara ta yadda komai ya sauya mata lokaci kankani tunanin Ra'uf shine dankare a zuciyarta sai dai kuma an raba wannan soyayyar data ginu a tafarkin gaskiya tanason ta kirasa taji muryarsa sai dai idan ta kirasa mai zata ce masa ba wani zata aura idan ta kirasa ya daurar kanta zatayi
Da wannan tunanin barci ya dauketa
***********
Kajan yo ma zuriyarmu wulakancin da babu wani bil adama dan cikin zuriyarmu daya taba janyomana face kai Hajiya Hanne ce take fadar maganar cikin bacin rai wacce take zaune a durowar gefen gado wanda wanda take maganar danshi ke zaune kan gado yana kokawar sa agogon hannunsa


Fadan ta cigaba dayi batare da tsayawaba nidai tun lokacin da zuriyata ta hadu da ta hafsatu babu ranar da farin ciki ya wanzarwa zuciya ta iyayenku sun shanyemin 'ya'ya na guda biyu dalili mai karfi da yasa shima dan uwan naka yaje ya auri wadda babu sanayya ko guda daya da na sani game da ita shiyasa kai dinma kaje neman auren irin su saiga irin cin fuskar da kai da karen kanka kajanyoma a halin naka ca nake kai dakanka kafi kowa sanin irin soyayyar da karima ke kokarin gwadama amma kaidin da karan kanka kafurta bakasan 'yar uwar jininka wadda kai kanka kasan tafi yarinya irin mayu aini dai sam banyi sa ar surikai ba daga uwar taka har hannatu yau kimanin shekaru akallah 4 rabon ubanka da zuwa inda nike kuma baidama niyyar zuwa itako uwar taka rabonta da zuwa kaduna tun barinku kasar nan amma inajin labarin bata shekara biyu bata zo taga uwarta ba saboda ni bata daukeni uwa ba duk irin halaccin dana yimusu daga ita har hafsatun wadda a kaf zuriyarmu babu wadda nayima abinda nayima hafsatu a matsayinta na yar uwata mafi kusanci a gareni amma yau ga irin abinda kajanyo ma kanka ka janyo ma zuriyar ka haba *Abdur ra'uf* .jin ta tsagaita maganar tatane yasa shi mikewa yana fadin haba Hajiya duk mai ne ne anfanin fadin haka inji AbdulRra'uf din da yamike yana kokarin daukar wayarsa ya cigaba dacewa tun a lokacin da abun yafaru yakamata aman ta da maganar.hajiyar ce ta kara dacewa naki mantawa da maganar idan kai bakasan ciwan kan zuriyar ka ba aini nasani nasan tozarcin da akamana nidai hada ji'bi da zuriyar hansatu bai kareni da komai ba wato ma kawai nabar maganar . saurin ficewa daga dakin yayi danshi dayasan kalaman na hajiyar yana da cikin mizanin muni nada ga gareshi da baiyi jimirin zama a 'dakin nashiba shidai sam kalaman hajiyar sun masa matukar munin da bazai sake son jinsu ba wadda shidai sam hajiyar bata kasance macen da zai duba amatsayin uwa ga mahaifinsa ba domin da hakan yakasance yasan tabbas bazata zamanto
Mai sake kokarin jefa zuciyarsa tasa bisa ga kangin damuwa ba duba da irin kiyayyar da aka nuna masa a bangaren gidansu Rufaida wanda shi yasan ko da bai san dalili ba Ahalin nasane silar rugujewar farin cikin nasa a karo nafarko yarasa yarasa masoyiyarsa mai matukar son farin cikinsa wadda tarbiyyarta ce silar son cigaba da zama da ita na tsawon har abada yana cikin tunanin ne yakarasa bude kofar wani daki yashiga da sallamarsa. Gefen sallayar da yasamu dattijuwar matar fara yazauna yana fadin ammi sannu tasbahar hannunta ta ajiye akasa tana mai amsa masa sallamartasa dafadin yawwa *RA'UF* kafin tadora dacewa sarkin a zama har naga kashirya tun a subar fari tafada tana mai kau da kanta daga kallonsa *RA'UF* 'din ne ya kalleta yana fadin tuba nake *Ammi* tun 'dazu nagama shirya komai wannan rigammiyar tsohuwar ce ta tsaidani nagama shirina ta tsaidani *Ammi* ce ta dubesa tace kaidai kasani yawwa *Ammi Ra'uf* ya anbata dama har yau Hajiya na nan da fadan ta mara karewa idan ta fara Dariya abin yabawa *Ammi* tace sai hakuri zama da hajiya. Ina fata dai ka kammala shirya kayan naka eh ammi danladi ma har yasa su a mota.




Ko a jikin motar da hajiya tafito yi musu rakiya ita da sauran mutanan gidan fadan ta hau yi tana fadin idan kakoma kasar fararen motar ka mutu babu aure kannen ka kuma baza su fasa aure ba kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login