Showing 63001 words to 66000 words out of 86533 words
manta ni din da kake fadar hakan akaina ko makaho ya shinshina yasan cewa nafi wancan dan iskan kanin naka,wanda saboda abun kunya saurayin 'yar da iyayensa suka fasa,sai danni nawa 'dan ya taimaka musu zakayi min maganar banza,me ake da zuriya irin taku
Abba Bukar ya tunkaro Hajiya Jamila cikin zafin zuciya zai kai mata duka da take zaune kujera ba tare da tayi koda motsi ba Wahid ya mike ya rike hannun mahaifinnasa yana cewa
"Abba kayi hakuri"
Abba Bukar da idonsa ya soma ja yace
"Wahid yanzu ni Jamila ta ke fadawa wadannan maganganun,ita ta manta abunda ya faru da tata 'yar uwar ranar da ranar aurenta mijin ya fasa ta manta kuma abunda dan uwanta ya aikata da..."
Hajiya Jamila sai yanzu ta mike daga kujerar da take ta katse maganar Abba Bukar da cewa
"Bukar wallahi karka kusa,ka fadi wata magana akaina idan ba haka wallahi saikayi dana sani mara iyaka"
Cikin bacin rai ya kalli Hajiya Jamila yace
Wanne dana sani zanyi daya wuce ke wanda zakiyi"
Murmushi Hajiya Jamila tayi kafin tace
"Aini banida wani danasani,kune kukayi shi,tuntuni bama yanzu ba saboda kuskuren shigowar karuwa kazama cikin.....
Wahid ne ya yayi kokarin jan Abba Bukar ganin Ummantasu bazata fasa maganar da take,suka fito daga daki saida suka fito wahid ya dubi Abba Bukar yace
"Abba dan Allah kayi hakuri,da abinda Umma tayi yanzu"
Abba Bukar dafa kafadar Wahid yayi yace
"To ya zanyi Wahid kullum cikin hakuri nake yi,dawowar dana yi mata na dauka abun zaiyi sauki amma abun yafi nada ma,saboda don kawai na hadaka aure Rufaida"
Wahid cikin ba ya dubi ABBA Bukar yace
"amma Abba menene laifin Rufaida,bata aikata musu komai ba,haka ma ummansu Abba"
Abba Bukar yace
"To dama mai zata aikata musu Wahid kasan shi makiyi ba ya jira kayi masa laifi yake ba,yanzu ka wuce ku tafi karkuyi dare a hanya"
Jiki ba kwari su Wahid suka fito harabar gidan shida Abba Bukar gurin motarsu da Rufaida da sauran matan gidan suke jikin motar sun fito rakiyarsu
Haka suka shiga Wahid ya tada motar Rufaida ta shiga tare da Yasir da yayi girma ya fito a kyakkyawan Hausa Fulani da ya debi kamanni mahaifinsa sak
Har suka fara tafiya a motar babu wanda cikin Rufaida da Wahid sukayi wa juna magana saidai takan ji firarsu jefi jefi da Yasir don bataji akwai abinda zata iya cewa dashi shi din ma haka ne saboda bayason ta fahimci abinda ya faru shida mahaifiyar tasa a yanayin maganarsa ita dinma bata damu da hakan ba ta bude gidan gaba ta shiga jikinta babu kwari don tasan tabbas akwai abinda ya faru,a shigarsa sa dakin mahaifiyartasa,da niyyarsa tayi mata sallama sai kuma ga wadancen maganganun sun biyo baya
****
Marhabin da manyan baki wallahi sam ban tsammaci zuwanku ba"Rufaida ta furta hakan tana kokarin matsawa daga kofar falon da ta bude
Luba da ta shigo da Yusuf data riqewa hannu tace
"Ai dama haka zaki ce,uwar cika alkawari"
Ta karasa maganar tana hararar Rufaida
Rufaida tace
"Ayi min afuwa matar likita bokan turai kinsan Yasir baiji dadi ba yau kwana 2,yanzu dai ku zauna na kawo muku ruwa"
Luba ta zauna kujera tana cewa
"Var ruwan nan daga gida muke yanzu Abban Yusuf ya saukemu ya wuce asibiti"
Rufaida da take kokarin zama kusa da kujerar dasu Luba kekai tace
"Kai Yaya Kabir yana kokari, su likitoci kullum aiki kamar agogo ace har weekend ma"
Luba tace
"Hmm kedai bari kawai,yanzu aka kirasa waya patient garesu kuma ana bukatar yaje asibitin ya dubashi cikin gaggawa shine muka fito tare"
Rufaida tace
"OK Allah yabada lafiya"daganan ta maida dubenta ga Yusuf dake ta zaro ido tace
"Yusuf zo mugaisa mana ko kula ni yau bazaka yi ba"
Kafada Yusuf din ya make ya kwanta jikin Ummansa
Rufaida tace
"Au bazaka zo ba ko?"
Luba tayi dariya tace
"ai kema kinsan bazai zo ba tunda yaga baiga Yasir ba,yana inane ko jikin ne yayi zafi"
Rufaida tace
"Ai na fahimta,yanzu suka fita shida Abbansa,kinsan mara lafiya da kwalama ice cream yakeson sha"
Luba tace
"A lallai kuwa,nifa na dauka lafiyarsa kalau ashe da gaske baiji dadin ba"
Hararar Luba Rufaida tayi ta na kokarin furta wani Abu sukaji sallamar Wahid a falon amsa masa suka yi ya karasa shigowa Yasir da ya hango Yusuf yayi saurin sauka a hannun Abban nasa yayi wajen Yusuf 'din suka fara wasa
"Sannu da zuwa" suka yi kokarin hada baki duka gurin ce masa
"Yawwa,wa nake gani haka kamar Maman Yusuf hala makuwa kikayi ko?"
Wahid yayi maganar da murmushi kan fuskarsa
Luba tace
"Ai nafi matarka ita ko makuwarma yaushe rabon da tayi tazo gidanmu"
Wahid da yake kokarin zama kujerar gefensu yace
"Kuma tanbayarta kiji laifinta ne ba nawa ba"
Rufaida sai lokacin tasa baki tana dan hararar mijin nata ta wasa tace
"Kaji ka da wani zance,dan dan dai banasan tone tone amma da saina ce,anfi kwanan wata ina tanbayarka zani baka bani amsa,sai shekaran jiya kace.min naje,sai Yasir ya tashi da ciwo/a ranar zuwan namu"
Wahid ya kalli Rufaida yace
"To yanzu duk wannan dogon bayanin,me kikai inba tone tonenba"
Dariya sukayi gaba daya
Luba tace
"Oh Dadyn Yasir bamu gaisa ba hira tayi dadi,ina yini,ya aiki"
Wahid yace
"Gaskiya kuwa,lafiya Alhamdulillah ya abokin nawa dafatan yana lafiya"
"Alhamdulillah,tare muka fito ma yanzu zai karasa asibiti ne"cewar Luba
"Ok,sufa aikinsu babu hutu"fadin Wahid
" wallahi kuwa,yanzu muka gama maganar da Rufaida,gwara aikinku sosai"fadin Luba
"Kai Maman Yusuf babu wani gwara mutum ya fita tun safe shida gida sai yamma"Rufaida ta sa baki a hirartasu,gurin fadin haka
Luba ta rike baki tace
" iye mai miji yaushe kikeso ya dawo to?"
Harararta Rufaida tayi tace
"So nake 2ma tayi masa a gida"
Tsaki Luba taja mata
"Rufaida ta kalli Wahid tace
" Dady kaji ta harda tsaki ko nayi laifi ne?"
Ya 'dan rausaya kai yace
"A'a baki laifi ba,kinga bari nakira Kofur Musa ya karo yawan Ice cream din nan"
"Rufaida tace
" au dama buku siyo ba?"
"Eh mana da baki ga leda a hannu na,muna fita mukayi kicibis da Musa shine ya amshi key din daya motar na masa sautu dan banajin zuwa Shoprite a lokacin shi kuma har can zai karasa, mu kuma Unguwa muka zaga da Yasir"
Wahid yayi wannan maganar
"Ok,lallai kunsha aiki" Cewar Luba
Daganan suka cigaba da firarsu,Wahid ya mike bayan ya gama waya da Musa ya fito waje shida yaran ua barsu a falon suka cigaba da firarsu
Sai sannan Luba ta maida dubenta ga Rufaida kacokam ta soma magana
"Rufaida yanzu nakejin labari gurin,Kabir cewa AbdulWahid zai kara aure da wannan Ruqayyan da suka zauna da surikarki anan gidan amma Wahid din yace shi sam baya sonta"
Jin Luban ta kawo karshen zancenta yasa Rufaida kallonta,dukda bai taba fadamata zancen aurensa ba amma ta dade da sanin zancen Ruqayya tunma kafin suyi aure hakan yasa bata daga hankalinta da taji Luban tayi maganar yanzu kuma bata nuna mata rashin sanin taba tace
"Eh haka ne,Luba nidai indai zata zo da Alkhairi ina maraba da ita"
Luba ta jinjina kai tana mamakin jin wannan Kalmar daga bakin Rufaida don ita kanta tasan Rukayya ba alkhairi bace muddin ta shigo gidan Rufaida a matsayin kishiya bare kuma Rufaida tayi zaton haka,tun kafinma suyi kishin bata zo da Alkhairi ba bare yanzu da zasuyi zaman kishi,ita kam har mamakin Rufaida take lokuta da dama don gaskiya da itace bazata bari ayi mata haka ba,saboda tana samun wani labarin gurin Kabir mijinta ta dai yi kokarin kauda tunanin nata tace
"Hm Rufaida kenan,kina tunanin Rukayya ce Alkhairi,a zamanku kinadai sane da abubuwan da suka riqa faruwa a zamanku dake dasu,nima kuma ina ganin wasu da idona,kedai kiyi fatan Allah ya hadaki da abokiyar zama tagari badai Rukayya ba"
Rufaida tayi murmushi tace
"Don me za kice ba Ruqayya ba,bakya tunanin ta iya sauyawa idan anyi auren,shifa namiji ne shi zai saita gidansa"
Luba ta danyi dariya
"Au kina tunanin Rukayya zata canza lokaci guda,kintuna zagin da suka riqa yi miki ta uwa ta uba,da ita da surikarki,kuma ina gidan lokacin,karki yaudari kanki Rufaida, don hatta Abba Bukar yace bai amince da Wahid ya auri Rukayya ba,don shima kansa yana sane da komai"
Rufaida tace
"Duk da hakan da ya farun kinsan dai,Ruqayya tanasan Yaya Wahid zata daina koma meye,Abba Bukar kuma zai sauko"
Luba tace
"haka dai kikace,nidai kawai abinda zance miki ki cigaba da addu'a nima kuma zan cigaba da tayaki"
Da haka suka cigaba da hirarsu,da sai dare Luba ta bar gidan Rufaida don kawance suke sosai kamar sun dade da sanin juna kasancewarsu hatta a shekarun haihuwarsu daya shiya kara musu karfin kawancensu kuma kowacce ta yaba da halin kowacce"
Ayi manage don Allah kunsan yau da gobe sai Allah
Kardai ku manta mun dan waiwaya bayane amma next page insha Allah dawo Inda muka tsaya sai a dora insha Allah
Nagode masoya a duk inda kuke ina godiya Allah ya bamu iko anfani da sakon da littafin yakeson ya isar
Sadiya Ibrahim Khalil
(Sadiya Khalil)
*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Khalil
46.
Ayi manage don Allah ba yawa kuyi min afuwa nace saura 1page adawo bayan da aka waiwaya yanzu kuma, saura 3page yanzu kuma saura 2page kenan ayi hakuri da spelling mistake
Sadiya Ibrahim Khalil
(Sadiya Khalil)
Jin sallamar Wahid a 'dakin yasata kokarin tashi daga kwanciyar da tayi a gado tana danna wayarta ta tashi zaune tana amsa masa sallamarsa
Kallon Rufaidan yayi yana kokarin zama gefen gado yace
"Badai har kin kwanta ba"
Murmushi tayi ta kallesa
"A'a ina kokarin kiran Samiha ne,kuma nagama bata dagawa"
Yace
"Kila bata kusa da wayar ne"
Tace "Eh nima nafi tunanin hakan"
Dube dube ya fara kafin yace
"Ya banga Yasir din ba"
"Gashi nan dakyar na samu ya kwanta bayan ya gama rigimar tafiyar Yusuf" tayi maganar tana nuna masa Yasir din da yake kwance gefenta
Murmushi Wahid yayi yace
"Ai Yasir da Yusuf shakuwarsu kamar tagwaye"
"Gaskiya kuwa" fadin Rufaida
Gyara murya Wahid ya danyi ya dubi Rufaida ya soma magana
"Dama inaso muyi wata muhimmiyar magana"
Kallonta ta maida kacokam garesa tace
"Ina saurarenka"
Wahid ya gyara zamansa ya soma da cewa
"Rufaida,nasan dazu kunyi maganar auren Rukayya da Umma takeso na kara keda Luba sai dai maganar gaskiya bana son aurenta saboda ke irin halarcin da kikayimin da biyayyar da kikayi wa su Abba dan nasan tuntuni ba nine zabin da kike so ba,amma da Allah ya zaba miki ni sai kika hakura,ki amshi zabin da Allah yayi miki da hannu biyu,kuma kika zama mai hakuri da irin barazanar da Umma tasha yi miki,da zagi da cin zarafinki kafin auranmu dukdan saboda kice kin fasa aurena,dama yanayin zaman mu yadda yakasance bayan aurenmu da Umma da Rukayya suka shigo cikin rayuwarmu,kuma suka riqa yi miki abubuwan da zasu bata ranki amma duk kika jure,amma yanzu bana tunanin nayi miki adalci muddin na amince da abinda Umma take so nayi,na auri Rukayya,saboda nasan Rukayya sai tayi barazanar tarwatsa zaman mu,ni kuma banaso na rasa mace kamarki a cikin rayuwata"
Murmushi Rufaida tayi jin ya kawo karshen zancensa tace
"Karka damu Yaya Wahid,ka aureta din,insha Allah babu abinda zai faru garemu,kuma zata kasance alkhairi a tare damu,zamu rayu nida ita saboda faranta ranka,da tarbiyantar da yaranmu hanya madaidaiciya"
Murmushi yayi jin maganar da tayi yace
"Haba Rufaida wannan tunanin na kine kawai ba nata ba,ita abinda zai kawota rayuwarmu so take ta wargaza zaman mu ni da ke kamar yadda Umma take so"
Murmushi ta sake yi tace
"Karka bari wannan tunanin yayi tasiri a zuciyarka domin Allah shine mai gyara ko wanne al'amari ba tare da munyi tunanin hakan ba"
"Eh haka ne,mata ta,zan fahimtar da Abba dan shi haryau yakasa amincewa da maganar auren,saboda yana tsoron karsu yima diyarsa wani abu"fadin AbdulWahid
Rufaida ta murmusa jin karshen maganar Wahid din tace
" Allah yana tare da mai gaskiya,nayi alkawarin zan rike gaskiya a zaman mu,zan kira Abba na sanar masa indai saboda nine bayason ka auri Rukayya toni nace babu komai,saboda inasan mijina ya kasance mai biyayya ga mahaifansa,bana so na zama silar kasawarsa"
"Au harda,kinasan mijin naki zaki fadawa Abban" fadin AbdulWahid
Rufaida ta 'dan hararesa tace
"Eh mana tunda kasan ba nida kunya"
Dariya yayi yace
"Oh dan kin fadawa Abba irin son da kikewa mijinki shine rashin kunya"
Ta sake harararsa tace
"Oho ma"
Ya dan sake yin murmushi yace
"Wallahi Rufaida,ban taba tunanin zaki so ni haka ba a baya can"
Ta 'dan zaro ido
"Saboda me"
"Hmm,saboda ba nine zabin ranki ba"
Fadin Wahid
"To waye zabin ran nawa bayan gaka"
Fadin Rufaida
Murmushi yayi jin maganar ta yace
" 'dan uwanki shine zabin ranki mana,ni rashin uwa ne yasa akayi uwar daki dani"
Murmushi tayi ta dan zaro ido kadan tace
"Ko daya kaine dama zabin da Allah ya zaba min,kuma waye dan uwan nawa nufinka Ra'uf ai bamuda dangantaka da shi"
Dariya yayi kadan yace
"Eh mana dan uwan kine,tunda kun hadu a dangin Annabi Adam"
Murmushi tayi tace
"Ah to sai dai hakan,yawwa bana fadama,ka dai na min maganar wani tsohon saurayi na ba,bansan mai yasa baka kishi na ba?"
"Sorry matata,ina kishinki matukar gaske,amma kuma yanzu ke matata ce babu mai kwace min ke yanzu,ji nayi kawai yau ina sha'awar tuna baya"
Ya karasa maganar yana jiran jin amsar da zata basa sai yaji tana cewa
"Tuna bayan har saika tuna da Ra'uf kuma bayan babu wata alaka tsakanin mu bare har yasa mu dinga tunawa da shi a cikin bayanmu"
"Muna da alaka da shi a bayanmu mana,tunda ya taba shiga cikin rayuwar kanwata"
"Hmm to naji,abar maganar tasa
Cewar Rufaida
" shikenan,amma wallahi ban jidadin abinda ya faru ba da ya zama sanadiyyar baki aure saba,nasan da shine zai kula dake fiye dani"
Karar wayar Rufaidan yasa Rufaida maida maganar da take kokarin fada ta maida hankalinta ga wayar ganin Samiha ce yasata sakin murmushi ta nunawa Wahid wayar
"Kaga mutuniyar taga kiran ta biyo" daganan ta kara wayar a kunne tare da gabatar da sallama
Samihan ta amsa
Rufaida ta fara tsokanarta
"Uwar biyo ya kike ya ya takwarata,yaya Ahmad"
"Wato uwar biyu ko?,Duk muna lafiya yaya Wahid,da surikina"
"Eh mana uwar biyu zance tunda ni banida shi,Gashi nan yana jinmu,Yasir kuma ya kwanta"
"Zaki yi shine,yawwa bawa Yaya Wahid wayar naji ya akai zai karo mana kishiya"
"Gurin wa kikaji wannan zancen"
"Kinga nidai bashi wayar muyi magana"
Da haka Rufaida ta mika masa wayar tana ce masa
"Ungo Samiha tana so ku gaisa"
Ya amsa wayar da murmushi kan fuskarsa,yasa a kunne ya fara magana
"Assalamu Alaikum uwar biyu"
"Wa'alaikumus salam ,au harda kai amasu cemin uwar biyu zan rama ne"
Yayi dariya
" Eh mana,amma kafin ki rama zaki rame"
"Eh amma dai na rama,hmm ba mu gaisa ba Yaya Wahid, ina yini ya aiki ya kawata"
"Lafiya Alhamdulillah,ya UK ya maigidan naki ya takwararmu"
"duk muna lfy ba lafiya ba"
"Subhannallah maiya sameku"
"Eh to cutar kishi ke da munmu munaso muji maine kawarmu bata yi maka,har daga aurenku zaka kara mata kishiya"
"Au sai mace bata yi ma wani abun zaka kara aure kun manta karin auren Allah ne yace ayi,matukar mutum yana da sararin yi kuma yanada bukatar karawar ,kuma yasan zai iya adalci a tsakaninsu"
"Eh hakane amma dai"
"Amma me fadi"
"Kamata yayi kukai shekara kamar hudu zuwa biyar sai a fara maganar auren"
"Nima naso hakan amma Umma ce take so nayi yanzu,saboda Rukayyan ta kusa kammala karatunta,sai tayi service bayan aurenmu,kuma kawarki ta fahimce ni"
"To Allah ya tabbatar da Alkhairi yasa ta gari ce"
"Amin Samiha,yau ma tukun waya fada miki wannan zancen"
"Ai kasan abun duniya baya buya"
"Hakane kam,amma dukda hakan ana samun wanda yake fadar wani zancen har wani ya sani"
"Eh to haka ne"
"To Waya fada miki kodai Kawarta kice?"
"Ko daya kaga bata wayar ma"
"Au bazaki fadamin ba"daganan ya mikawa Rufaida wayar da take jin abinda suke tattaunawa a wayar dukda batajin abinda Samiha ke fa'da amma ta fahimci akan mai suke tattaunawar yana mika mata wayar ya fice daga dakin
Samiha ta soma magana
" yanzu Rufaida kina ganin Wahid yayi miki adalci duka yaushe kuka yi aure da zai kara aure,abin ya dauremin kai kodai kina masa wani abu ne"
"Babu ko daya Samiha umarnin Ummansa ne karin auren da zai yi wadda zai aura din ma Cousin sister dinshi ce"
"Au wai banda kokarin kashe kin data kusa yi kafin auren shine zata hada ki kishi da 'yar uwarta bakin ciki ya kashe ki kenan"
Jin furuci Samiha yasa Rufaida ta zaro ido kamar Samihan na ganinta,da alamun mamaki
"Waye ya baki wancen labarin ke kuwa"
"Aunty Samira ce ta fadamin,tun sanda abin ya faru,ganin baki min maganar ba yasa ta nima ban miki ba,gaskiya Rufaida wannan auren naki hatta Ummi Hauwa'u bata sanshi dandai yazo da rabo ne,amma tun muna yara kike bani labarin abubuwan da Ummansu Wahid take yi muku,kuma nima nasha gani da ji,don wallahi da na isa na fadawa Abbanku da ba zan yarda a aura miki Wahid ba,duk da dai shi yana sanki,amma uwarsa fa,irin wannan abun ake gudu gashi tun ba'aje ko inaba ta sako masa maganar aure so suke su kashe ki"
"Haba Samiha maida wukar komai mukaddari ne niba zan sauya komai ba kidai cigaba da tayani addu'a insha Allah babu abinda zai faru dani tunda dai nasan halin Rukayyan ai komai zaizo da sauki"
Murmushi Samiha tayi kamar Rufaida na ganinta tace
"Kinga Sanin hali bashi ne mafita ba addu'ar dai itace mafita kuma zan ta yaki Insha Allah"
"Yawwa nagode kawata"
"Babu komai " yar uwa, yawwa kinsan Cousin dinsu Ahmad Nasiba ta aura kuwa,tuntuni inata so na fada miki ina mantawa"
"Ke dan Allah fa bansani ba,Nasiba bata fadamin ba"
"Wallahi,kuma muna hirar a Group naga bakya duba wane shiyasa,mamar angon yayar surikina ce Ahmad ma yazo daurin aure,saida suka dawo wajen daurin auren da muka yi waya nace masa ya ganki yace a'a baki na Abuja ba,nace masa kinzo goyon ciki a gida kika haihu kuma kina gidan bikin ranar daurin aure,yace min baisaniba aida ya nemeki kun gaisa"
Cikin farin ciki Rufaida tace
"Ah ashe dai muda Nasiba no parallel"
"Eh mana,kece ma mukayi parallel din ma"
"To ya za'ayi haka Allah ya tsara,kinga wallahi na fara jin barci fa zan kwanta"
Da haka sukayi sallama Rufaida ta aje wayar ta lula duniyar tunanin rayuwarta
Bana typing mai tsawo shiyasa wasu zasuga kamar littafin zai yi tsawo
Allah ya shiryardamu bisa tafarkin tsira amin*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Khalil
47
Not edited
*RA'UF*
"Ammi sannu da gida" Ra'uf yayi maganar yana karasa zama gefen kujerar da Ammin ke kai
Ammin ta dubesa ka'dan
"Yawwa Ra'uf,yanzu na tanbayi su Husna kana ina suka cemin kaje gidan Shureim"
"Eh wallahi Umma can naje naje dakinki na fada miki zan fita na tadda kina barci,a gajiye nake ma"
Harararsa Ammi tayi tace
" 'yar wannan tafiyar ace harka gaji,dafatan suna lafiya dai ko su Inteesar 'din?"
"Eh Ammi lafiyar.su kalau Irfan ne dai bayajin dadi shine naje na dubasa"
"Oh Allah ya bashi lafiya,dama yaro da yazo duniya zaka samu ya fara rashin lafiya"
"Wallahi kuwa Ammi"
"Au kako ji Samihan Ahmad