Showing 78001 words to 81000 words out of 86533 words
taimaka mata amma banda yan uwan mijinta dukda kasancewarsu 'yan uwanta kasancewar auren zumunci aka yi mata da mijin ta Malam Jauro da asalin sunansa Bello saidai kuma su da suka fi kusa da mahaifin nasu basa taimaka musu, Mijin Inna wuro Malam Jauro nada shekara hudu da rasuwa a lokacin Mamuda yanada shekara 16 da Hadiza a lokacin keda 13 sai Salamatu mai takwas, Allah ya amshi ran Inna wuro sosai 'ya'yan nata suka ji mutuwar mahaifiyartasu shikenan sun rasa uba yanzu sun rasa uwa bayan rasuwarta ne,'yan uwan mijinta suka kwashe 'ya'ya matan suka maidasu hannunsu,'yan uwan Inna wuro da basu so hakan ba,dan sunsan wahala zasu basu tunda suka daukesu, haka dai suka hakura,suka dauke Mamuda shi kadai zuwa gurin kanwar mahaifiyarsa shekarun inna wuro 2 da rasuwa a lokacin shekarunsa goma sha shida wani makwafcinsu da yake zuwa neman kudi Kaduna anan ya bukaci da zai koma a bashi Mamuda ya tafi dashi ya rika tayasa kasuwanci,kasancewar mutumin abokin Malam Jauro mahaifinsu Mamudan ne tundaga yarinta a lokacin ganinsa a matsayin maraya yasa shi sha'awar daukarsa haka Malam Audu ya tafi dashi wannan tafiya ita ta zamewa Mamuda silar arzikinsa
Hadiza tana isa aure ta samu mijin ta cikin Danbattan da take kai tallar fura suka hadu a nan da yake dan cikin garin Danbatta ya aureta
sai Salamatu da itace karamarsu
Mamuda da kudi suka fara zauna masa ya yanke shawarar zaiyi aure kuma ya yanke shawarar diyar Malam Audu da yayi sanadiyyar samun arzikinsa zai aura mai suna Hajara ,yana zuwa da maganar auren da yayi niyyar auren 'yar wajen Malam Audun dangin mahaifinsa suka ki yarda suka ce saidai su zaba masa mata a cikin 'yan uwansa ya aura bazai aure a dawa ba aka aura masa Hanne,ya tafi da ita Kaduna da zamansu shida Hanne daga auren nasu ya fahimci bata da mutunci ko kusa,bata ganin girmansa har suka shekara biyar da aure a lokacin tanada yara uku,Suleiman da suke cewa sule sai yasaka sunan mahaifin Mamudan Malam Jauron da sunansa Bello da ake kiran yaron da Bello sai Inna wuro da asalin sunan Inna wuron Fatima ake cewa da yarinyar Fati
Daganan ya yanke shawarar kara aure ya yanke shawarar auren Suwaiba da take 'ya ga kanwar Inna wuro mahaifiyarsa da suma yan uwan nasa basu hana saba hatta dangin Mahaifinsa don kowa yasan halin Hanne a lokacin
Suwaiba ita macace mai hakuri da kawaici aurensu da shekara daya ta haifi danta namiji yaci sunan Ubangidan Mamuda da Malam Audu da sunansa cikakke AbdulRa'uf da ake ce masa Abdu Suwaiba ta yi kiransa da suna Babban Mutum,
Gwaggo Salamatu a lokacin ciki ya bullu a jikinta hankali dangi duk ya tashi,aka tsareta da tanbayar wanda Yayi mata cikin taki fada,sai da abun yakai da bugunta ta fada Sunusi dan uwan Hanne da suke uwa daya uba daya shine yayi mata da yana jin an fara tuhumar waye yayi mata cikin ya gudu yabar garin ,koda ta fadi Sunusin ne yayi mata babu wanda ya yarda a cikin 'yan uwan nasu dukda sunsan ba ji Sunusin yake ba amma sunyi shaidar baya iskanci da yaran mutane bare ma haryayiwa Salamatun kuma ma sunusin yanzu bama ya garin,acewarsu ita dai ta rasa wanda zata yiwa kazafin ne ta yiwa Sunusi taje wajen tallar furarta amma ta ciki zata zo ta yiwa Sunusin Sharri dukda kasancewarsa dan uwanta,tuni mutanen gari da 'yan uwan Salamatun suka shiga goranta mata,da binta da bakaken maganganu da habaice habaice indai zasu ci karo da Salamatun,wannan bakin cikin yasa Salamatu barin garin su don gujewa maganar mutane akanta da 'yar da zata haifa ko da idan Allah ya nufa
Wannan labarin batan Salamatun,ya ba kanta ran zuriyarsu Mamuda ciki harda Mamudan da nai man duniya yayi wa kanwarsa bai sameta ba harya hakura,da saida bacewar salamatun aka sanarmasa dalilin batan kanwar tasa har kuka yayi jin irin kaddara da ta samu kanwarsa kuma ma Sunusi shine yayi mata wannan aikin da shi yanada yakinin Sunusi ne,amma Sunusin ma neman duniya an yimasa ba duriyarsa.
**********
Suwaiba a haka suka cigaba da haihuwa kusan a tare da Hanne da Suwaiba Suwaiba nada 'ya'ya biyar a shekarar da bata fi 10 da aurenta ba
Abdu,Hamidu,Salamatu,Adam,Karima
Hanne tana da yara shida
"Sule,Bello,Fati,Jabir,Usman,Asiya
Dukkansu kansu a hade yaran suke kasancewar Hanne ke juya gidan shine dalilin zaman yaran inuwa daya Suwaiba kuwa macace mai kawar dakai halin Hanne data sani shiyasa su zama lafiya a gidan kuma matsayin Hanne na 'yar uwarta bazata so su rika hayaniya ba
Batun dukiyar Mamuda kuwa kullum bunkasa take yi a lokacin yaje Makkah yakai matansa ma
******
Malam Basiru da matarsa Saude 'yan asalin jihar jigawane karamar hukumar Taura da zama ya kawo su garin Kaduna shida matarsa da Malam Basiru ke sana'ar dukanci a babbar kasuwar Kaduna Central Market rayuwa suke cikin rufin asiri da yaransu uku
Aliya,Amina,haladu,daganan haihuwar ta tsaya musu
Aliya da itace Babba tana da shekara sha hudu da ta kasance kyakkyawar macace,
Samari suka fara nuna aha'awar aurenta amma dukta kisu sai wani mai suna Tijjani da yake kasance dan asalin sokoto sana'ar gini ta maidosa Kaduna,anan Allah ya hadasa da Aliyar da yake a unguwarsu harda shi a masoyan Aliyar da Aliyar duk cikin manemanta shine yafi kwanta mata a rai,dandanan ya fito ganin Aliyar ta amince dashi aka yi musu auren so da kauna
Shekara guda da auren Amina ta haifi yaronta namiji mai suna Ahmad.
Amina da tasowarta tafi Aliya kyau da farin jini samari suka fara tururuwar son auranta,cikinsu duk Habibu tafi so da yake abokin Tijjani mijin Aliya da Habibun shima magani ne kamar Tijjani
Malam Basiru a kullum cewarsa Amina matar manya ce,shiyasa duk yaki bawa manemanta damar turo magabatansa, Allah ya amsa Addu'ar mahaifinta taje sayayya Central Market Allah ya hada ta da Mamuda da taje siyayya shagon nasa
Shiko Mamuda yana ganin Amina a shagon nasa da taje siyayyya ganin nutsuwar yarinyar ta kwanta masa a ransa har yaji yana son ya kara aure da ita
Abokinsa da suke tare a shagon sanda taje siyayya ya tanbayesa koya santa ganin sunyi magana yace masa
"Eh yasanta a unguwarsu take mahaifinta ma a nan kasuwar yake sana"ar dukanci"
Sosai abin da abokin nasa ya fadama sa yayi masa dadi ganin yasan ma mahaifin Aminar Malam Basiru mutumin sane ma sai dai bai taba zuwa gidansa ko wani abu ba a iya kasuwar suke hurdarsu anan ya yanke shawarar zai fadawa Malam Basiru yaga yarsa yana son aurenta
Malam Basiru da Mamuda yayi masa wannan maganar ba karamin dadi yaji ba,ganin koba komai Amina zata auri babban mutum Kamar Mamuda da yana sane da cewar Mamudan yana da mata biyu da 'ya'ya goma sha daya amma shi koda Mamuda ya fadama sa yawan 'ya'yan nasa da matansa har su biyu bai damu ba,kudi sun rufe idonsa,koda yajewa da Amina da mahaifiyarta batun auren Saude kin amincewa tayi ya za'ayi akai Amina gidan mai mata bama mace daya ba a'a har biyu ga yaran sa 11 da take da tabbacin a 'ya'yan nasa akwai sa'ar Aminar
Haka dai Malam Basiru ya shafa wa idanunsa toka yace arziki yana kiran 'yarsu suna gujewa waccen shekarar yaji labari yakai matansa makkah,shine ita Saude zata yiwa 'yarta bakin ciki Saude da har garinsu taje akan maganar auren da yakeso ya yiwa Amina bataso ita Aminar akan a hanasa aurawa Amina Mamuda amma da suka masa magana bai saurare su ba,sam ya ki hangen gaban da su suke masa hange
Haka yasa Mamuda ya kawo kudin aure shida makwabtansa suka ansa ba tare da wani dan uwansa ya sani ba,saboda yasan basu son auran
Amina da ita ma a bangarenta tunda aka kawo kudin hankalinta ba a kwance yake ba sam ba son Mamuda take ba zuciyarta tana gurin Habibu,
Mamuda ko yakan zo zance gurin Amina dukda Aminar bata wani sakin jiki tayi fira da shi saboda yadda zuciyarta bata garesa amma sam shi bai kawo bata san sa ganin yana da duk abinda za'aso shi danshi,kuma ma bai taba ji koda da wasa ba wani yace masa Aminar bata sonsa ba saboda shi soyayyar Aminar ta gama mamaye cikin zuciyarsa jinsa yake a lokacin indai bai aureta ba akwai matsala a rayuwarsa don shi Amina ce daga kallo daya da yayi mata a rayuwarsa yaji yana tsananin sonta fiye da kowacce mace,banda Hajara diyar Alhaji Audu ubangidansa da ya fara so 'yan uwansa suka yi masa auren gida da Hanne dukda bawai sonta yake ba haka ma Suwaiba matarsa ta biyu auren hadi aka musu da ita itama bawai sansu duk yake ba ya auresu
Sanda labarin auran da Mamuda ya zowa Hanne gaba daya kiyayyar duniya ta dorawa Amina tun kafin ma taganta haka ta tashi hankalinta ta kuma tashi namijinta, haka ta shiga bin bokaye da malamai akan maganar auren
Itako Suwaiba ko a jikinta dan ita dama tasan namiji mijin mace hudu ne,saidai dan kishin da taji dan kadan da baza'a rasa ba
*****
Anyi bikin Amina da Mamuda lafiya an gama lafiya Amina ta kasance mai hakuri da zabin mahaifin nata da Allah dama ya riga da ya kaddara auren basu,amma bawai da son ran Saude mahaifiyarta ba dama 'yan uwansu baki daya,haka bada son ran Hanne ba
*****
Amina shigarta gidan duk soyayyar duniya Mamuda ya dauketa ya dora mata,bangare guda ya gina mata a matsayinta na Amarya
"Wannan ya kara bata ran Hanne ganin duk shige da ficen da take da asarar dukiyarta da take duk a banza suke tafiya,Mamuda yanzu bama ta tasu yake,wannan ya kara hura wutar kiyayyar da Hanne take yiwa Aminar
Amma itako Amina tana ganin girman kishiyoyinta da 'ya'yansu sam batada mummunan manufa a ranta game da su
Shekara guda da ta zago da auren Amina da Mamuda ta haifi diyarta mace kyakkyawa mai kama da mahaifiyarta sak,tare da kishiyarta Amina ta haihu wato Suwaiba da ta haifi diyarta Malika
Safiyyya nada wata shida abubuwa suka fara sauyawa game da zaman Amina da mijin nata babu kwanciyar hankali, dama abokan zama duk ba shiri suke ba dan hatta Suwaiba Hanne ta fara zugeta akan Aminar,saidai ita Suwaiba tunanin da take baza ta ki Hanne da take 'yar uwarta ba tace zatayi shiri da bare da basu da alaka a tsakaninsu,gama halayyar Hannen da ta sani tuni inda ta fahimci shishshigin da take wa Aminar zata iya cewa akwai kullin da suke,ita ko Suwaiba macace mai gudun magana,wannan shine dalilan Suwaiba
Malam Basiru tun kafin aje ko ina ya fara dana Sanin aura wa Mamuda 'yarsa Amina don shi tunaninsa yana aurawa Mamuda 'yarsa shikenan sun samu hanyar samu gurin Mamudan,dukda a farko mamudan ya gwada hakan bayan bikinshi da Aminar abinci ake saukewa iyayen Aminar amma yanzu ko ko buhun gishiri basa samu
A yanzu haka Malam Basiru gani yake gwara Tijjani mijin Aliya akan Mamuda mijin Amina,saima da Aminar tazo gida bayan komawarta gidan mijinta bayan haihuwar ta da taje gida goyon ciki harta haihu yarinyar tayi wayau ,nan yana ganin Aminar yadda dukta rame daga komarwata gidan daga goyon cikin da tunda Aminar tazo Mamuda ke faman zarya gidan da naman kaji da lemuka amma daga komawarta duk ta rame nan iyayenta suka shiga tanbayar maike faruwa ba ta boye musu komaiba ta fada musu,tunda boyewar mai zatayi bayan ita dama Mamuda ba zabin ta bane,haka Malam Basiru da yasan shine silar auren 'yar tasa, nan ya fara rokon Aminar da mahaifiyarta yafiya
Saude tace"ai karshen kwadayinka ne dama yakai ka ya baroka gashinan tun kafin aje ko ina ga yadda ta dawo,kaje ka kai 'yarka cikin kishiyoyi kuma kowacce da 'ya'yanta bayan bata rasa ma rasa matar ba saboda son abin duniya ka manta ubangiji ke azurta bayinsa,amma idonka ya rufe tunaninka ai mijin Aminar shi zai a azurta mu ko ya azurta 'yarta mu,in banda zama babu kwanciyar hankali mai take yi"
Wannan abun da Mamuda yake yiwa 'yarsa ya yiwa Malam Basiru ciwo nan ya shiga neman Mamuda a kasuwa akan ya sakar masa 'yarsa amma Mamuda yace shi yana son matarsa ko ina zasu je bazai sake taba haka malam Basiru ya hakura
Aliya ma ta sake haihuwar diyarta mace Bilkisu sunan kakarsu Aliyar da ranar da Aliyar ta haihu aka saka
wa yarinyarta ta Bilkisu da aikowa da su Aliyar a lokacin da Aliyar ta haihu da kwana daya da rasuwar Bilki kakarsu Aliyar ta wajen uba wannan yasa Tijjani sakawa 'yarsa sunan kakar matar tasa Aliya
Wanda bayan haihuwar Aliyar Tijjani ganin sun fara tara 'ya'ya daga daya har suna biyu yanzu ga yanayin yanzu babu wani samun da suke a harkar ginin yasa ya yanke barin anan ya yanke shawarar zai dauki Aliya su koma Sokoto haka yadauketa zuwa sokoton da niyyar Tijjani da duk shekara zai kawo Aliya gida ta ga gida ba dan san ran mahaifan Aliyar da 'yan uwanta ba tabi mijin nata kuma gashi yace zai rika kawota gida wannan yasa shi jin dadi
Safiyya na da shekara biyar da haihuwa Amina ta sake haihuwar 'ya mace aka saka mata suna Hauwa'u wato ni da har nafi Safiya kama da mahaifiyarta mu Amina,a lokacin Saude mahaifiyar Amina ta haifi diyarta mace da ita Saude ta fidda rai da haihuwar ma a lokacin dan Haladu yayi shekara goma sha biyar sannan aka yi masa kanwar da taci suna Bilkisu aka sake maida sunan Kakarsu Aminar ga kanwarsu
Duk shekara sai su Malam Basiru sun zuba ido ko Aliya zata zo amma babu labarinta bana mijinta har tsawan shekara shida, duk wanda suka tanbaya a abokan Tijjani 'yan Sokoto idan sunje gida maiyasamu Tijjani har aka dauki wannan lokacin bai kawon Aliyar Kaduna ba amsarsu itace aisu Tijjani basu koma Kaduna ba wanda a wannan lokacin ne kuma Allah ya karbi ran Malam Basiru 'yan uwa da abokan arziki sunji mutuwarsa Amina da Mahaifiyar Saude da Haladu har sunfi kowa jin mutuwar Malam Basiru Bilkisu kuwa tana goye a lokacin batasan mahaifin nata ya rasu ba
Naji korafin page din danake muku nasan nima yana gajere amma kunsan yanayin rayuwa saboda karna rika barinku shiru yasa nake kokarin turo muku kullum ammah zan rika tsallaken rana indai kunaso sau uku a sati zan rika yi muku amma pages da yawa indai kun amince shikenan.
Nagode da yadda kuke nuna soyayyar littafin nan
[10/13, 8:18 PM] Sadiya Khalil Muhammadđ„°: A*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Khalilâ€
Book 2
5.
Shekaru na uku da haihuwa kanwar Mahaifiyarmu ta bace Bilkisu,da take sa'ar haihuwata sakamakon aiken da akayi mata siyo maggin miya shagon unguwa,neman duniya anyi mata amma ko alamun za'asake ganinta babu gidan Radio ba inda ba'a zagaba gurin cigiyarta amma babu duriyarta harma Inna Saude ta fidda rai gaba daya.
Batun Hakuri kuwa da Mahaifiyarmu take yi a gidanmu yana da yawa baga kishiyoyi kadai ba a'a har ga mijinta da 'ya'yansu dai dai kune cikin yayyenamu basu kama zugar da Hanne ke musu a kanmu da Mahaifiyarmu ba
Kwanaki sunzo sun wuce kamar kiftawar ido dukkanmu a yanzu haka mun soma girma dan Safiyya a yanzu tanada shekaru 11 ni kuma inada 5 Safiyya ta soma girma kuma ta taso da kyawunta Mahaifiyarmu takance ita da yayarta Aliya tafi kama,inda muka tanbayeta ina Umma Aliyar mu bamu santa ba anan ne take sanarmana labarinta haryau babu duriyarta da mijinta
Yau da wuri muka dawo makaranta muka shirya zuwa gidan kakarmu nida Yaya Safiya mu amso abincin da muka saba amsowa a kusan kowacce rana ta duniya
Tunda mu sam ko abinci bamu samu a gidan namu indai ba Ummanta mu tayi girki ba matan gidan hanamu sukeyi suce badan ita suke girkin ba,idan ta fadawa Baffanmu saiyace shi dai har da ita yake bada kayan abinci don haka ta kwatarwa kanta 'yanci ta rika amsar hakkinta gurin kishiyoyin nata,amma shi sam bazai yi mussu wata magana ba,kuma vazai bata wani abincin baba ta girka ,Ummantamu da tasan ko tayi maganar ba zata samu ba,wannan dalilin yasa duk ranar da ba itace da girki ba gidan Inna Saude zamu tafi mukarbo da ita din abincin saidawa takeyi a lokacin rayuwar tata abin tausayi muda muke a wannan babban gidan da zamu taimaka mata amma muke zuwa amsar taimako
"Umma ina kudin machine dinmu"
Fadina
Umma ta kalleni
"Kudin machine kuma Hauwa nan da unguwar Bellon saina baku kudin machine"
Safiyya ta harare in
"Umma kyaleta,batasan zuwa ne kawai"
Muna cikin hakanne yaya Jabir ne ya shigo bangaren namu,da shi da Yaya Usman da Yaya Malika muke shiri,akaf gidan namu da ya turo kofa da sallamarsa muka amsa masa ya na kokarin zama kujera muka gaishesa ya amsa mana da murmushi a fusakarsa ya 'dan kallemu
" ina zaku da ranar nan,naji ana cewa wata a cikinku bata da niyyar zuwa,kuma naga yau Alhamis babu makaranta"
Yaya Safiyya ta dan sosa kai
"Zamu je gidan Inna Saude ne,shine Hauwa tace saidai muje a machine"
Umma da take kallonmu ita Yaya Jabir ya kalla
"Umma mai zasu yo gidan Inna Saude da tsakar ranar nan,kuma a kafa ai akwai nisa, ko bata jin dadi ne?"
Nice nayi saurin yin magana kafin Umma tayi
"Yaya Jabir lafiyarta kalau abinci zamu je ansowa"
"Abinci kuma wanne irin abinci,kodai abinci zaku kai mata"fadin Yaya yana tsare ni da ido
Umma da Yaya Safiya da suke ta hararata ina kallonsu na cigaba da maganata a ganina boyewar mai za muyi
"Yaya ai indai ba girki Ummanmu ba bamu samun abinci,gwara ma girkin Mama Suwaiba takan bawa,Yaya Malika ta kawo mana a boye da idan Mama Hanne ta gani bata bari akawo mana"
Yaya Jabir da ransa ya baci ya kalli Umman tamu
"Yanzu Mama Amina,kuma kika yarda a rika yi miki hakan,ba zaki dauki mataki ba"
Umma tayi murmushi
"To Jabir mai zan iya yi,tunda bani na girka musu ba,mai gidan ma da nake ga zai iya tsawatar dasu yace bazai yi wata magana ba"
"To ai Baffa ba yi da laifi don yace hakan kece mai laifi,tunda yaga ba kisan ki kwatarwa kanki 'yanci ba fiyema da haka ce miki zaiyi, ke zaki kwatarwa kanki 'yanci,idan yaga kin yi jarumartar tararsu da maganar shine zai yi musu magana shima"
"To amma taya ya Jabir,kasan sunfi karfina sunfini manyan 'ya'ya ko ku sasa ku dokeni da 'ya'yana"Umma tayi maganar cikin raunin murya
Yaya Jabir ya zaro ido
" duka kuma