Showing 54001 words to 57000 words out of 86533 words

Chapter 19 - JININMU DAYA HAUSA NOVEL

iko da 'danba" cewar Abba Bukar
Kofa Hajiya Jamila tayi ta fice
Sai bayan ta fita Abba Bukar ya jiyo ya bawa Gwaggo hakuri shima ya fice yana sanar dasu zai dawo gidan idan ya tashi daga gurin aiki
Makwabtanma hakuri suka bawa su Gwaggo suka firfito suna jinjina lamarin masu tsinewa Hajiya Jamila nayi masu zaginta nayi,da kwashe mata albarka,dama mutane jiran suke ayi,dan danki zai auri 'yar uwarsa saitazo tana hauka maiye laifin Rufaidan yarinya mai hankali.*JININMU 'DAYA*

By Sadiya Khalil❤️

40.

Hajiya Jamila da tunda ta fito gidan Gwaggo take kuka a cikin motarta bawai kukan danasani ba akan abinda tayi kokarin aikatawa da kuma furucin mijinta akanta ba illa tunaninta 'daya ina zata da wannan abin.kunyar ace dan ta zaiyi aure bata sani ba sai ana saura kwana uku kuma aure ma ya rasa wadda zai jajubo sai 'yar Hauwa'u da kowa yasan kiyayyar da take ma Hauwa'un,ganin tunanin ba shine mafita ba yasata yiwa motarta key tayi gidan Gwaggo Lariya

Abba Bukar yana fitowa gidan yatarar da kurar motarta kai ya girgiza ya shiga motarsa da tunanin abinda ya yanke aransa kai tsaye gidan wan mahaifinsa ya wuce Baba Ashiru,Abinda ya faru kaf ya fadamasa da kuma hukuncin da ya yanke a daura auren Wahid da Rufaida saboda baiga alamun Hajiya Jamila zata hakura ayi auren ba
Baba Ashiru dubesa
"Gaskiya Bukar kayi tunani me kyau,abinda ya kamata ayi kenan,tunda ita Jamila har yau bazata yi hankali ba kamar wadda ake zugawa"
"Wallahi Baba babu wata zuga danni sai yanzu nake danasanin aurenta ma....
Baba Ashiru yayi saurin dakatar da Abba Bukar maganar da yake yace
"Kul Bukar koba komai ai uwar 'ya'yankace ba kuda wata makankara sai dai muyita yi mata addu'a"
Abba Bukar ya mike ya na cewa
"Haka ne Baba ni bari zan koma wajen aiki dan Allah ka kira Baba Amadu kasanar masa dan Gwaggo da mukai waya tace gaban kaina na fara yanzu tun busu mutu ba"
Baba Ashiru yace
"Ina ruwan Zainabu ,to zan sanar masa da dukkan abinda ya faru zan fadamasa hukuncin da ka yanke amma bazan ce kai yanke hukuncin ba karmu sake yin laifi"
Abba Bukar ya fito daga dakin Baba Ashirun yana dariya
*******
Gwaggo ce tayi kokarin karaso wa inda Rufaida take ganin kowa ya watse daga gidan da ga Rufaida sai Harira da Gwaggon dafata tayi ta soma maganar ba tare da ta damu da Harira dake gurin ba dan abu ne akayi sa ba a boye ba
"Haba Rufaida kukan ya isa haka kinemi sakayya gurin Allah kawai"
Rufaida ta dan goge hawayenta ta dubi Gwaggo tace
"Gwaggo nidai dan Allah a fasa auren nan"
Gwaggo ta zaro ido tace
"Baki da hankali Rufaida auren za'a fasa saboda wannan shashashar yarinyar tazo tayi haukanta,kenan a fasa taci galaba akanmu,to koda Wahid baya sanki sai anyi auren nan dan akuntata mata"
Kuka ta kuma rushewa da shi tare da cewa
"Ni dai dan Allah Gwaggo a fasa ,kina gani fa kashe ni Umma taso yi,ga maganganun da take fada akan Umminmu,Gwaggo dan Allah mai muka yi mata"
"Kinga bafa za'a fasa ba, ita bata isa ta kashe ki ba haukan banza take,maganganu kuma taje tayi tayi ita ce mara aikin yi,kuma sharrin ta saidai ya bita"
Da haka dai Gwaggo ta lalla'beta ta daina kukan suka koma inda suke aikinsu suka cigaba dayi
***
Sallamarsu Ummi Hauwa'u ta katse firarrakin da suke jefi jefi suna aiyukansu da gudu Rufaida ta karasa gunsu ta rungume Aunty Samina dukda ba wani kuzari jikinta
Gwaggo da Harira suka amsa musu sallamar
Ciki suka karaso da fara'arsu suka zauna a babbar tabarmar da aka shinfida
Saida suka gaggaisa ,Aunty Samira ta dubi Rufaida tace
"Yanaga ba kuzari jikinki kamar kinyi kuka ga idonki duk ya kumbura"
Gwaggo tayi saurin cewa
"A'a ba wani kuka sauro ne ya ciccijeta jiya bata sa net ba"
Aunty samira shiru tayi vadan ta yarda ba
Rufaida ta ja hannun su Kalim da Khalil yaransu Aunty Samina dakinsu dan surutun ma batasan shi ko daya
Ummi Hauwa'u ta bita da kallo aranta tana tunanin tabbas da abinda ke damun Rufaida zuwa dare zata sameta suyi magana
Su Rumaisa ne suke shishshigo da kayan da suka taho dasu da sauran yaran Abdul kuwa da shiya kawosu baima shigo gidanba ya tafi gidan Gwaggo Hajiya gurin abokansa

A'a marhavin lale da kanawa,Malam yake maganar da murmushi fuskarsa da shigowarsa gidan kenan ya cikaro dasu Aunty Samina suna aikin doghnut bayan sun huta sunci abinci
Da murmushi a kan fuskarsu suka gaishesa ya amsa yana cewa ina su Gwaggon suka ce masa suna daki
Dakin ya nufa ya tarar dasu a zazzaune suna nunawa Gwaggo kayayyankin da sukai wa Rufaida
Gaishe da Malam sukayi ya amsa yana musu sannu da zuwa
Zuwa can ya nisa yace
"Yau ne daurin auren fa yanzu Ashiru yake sanarmin ina kokarin shigowa nan gidan ya kirani a waya,shine nazo nasanar muku zance na shirya yanzu ,bayan daura auren zasu kawo lefe" da haka ya mike ya bar dakin dan baya san jin wani zancen su yanzu haka

"Wannan wanne irin aure ne Gwaggo daga zuwan mu yau ace yanzu za'a daura"Momy Maryam tayi maganar bayan Malam ya fice daga dakin
Gwaggo da ranta ya fara baci ita ma
"To ya za'ayi Maryam yadda suka tsara haka za'ayi"
"A'a Gwaggo kuma fa kuna da hakkin magana akan 'yar nan ai ba 'yarsu bace su ka'dai,ya daga zuwanmu za'ace yau daurin aure gaskiya babu alamun gaskiya a auren nan"
Momy maryam tayi maganar
"A'a maryam kar kice haka,mudai yi musu fatan zaman lafiya"
Cewar Gwaggo
Ummi Hauwa'u bata ce komai ba tana zaune tana saurarensu har suka gama firarsu
*******
"Rufaida Dan Allah karki nunama yayyenki ko a fuska akwai abinda ya faru dazu"Harira tayi maganar tana dafa Rufaida da suke daki zaune itada harirar tun da su Aunty Samina suka karbi aikin
" Harira ke ma kinsan halina a 'dan zaman da mukai kinsan bazan iya fada ba,abinda kuma Umma tayimin lokaci ne watarana sai labari"
Cewar Rufaida
"Harira ta nisa tace
" nifa matarnan ta bani mamaki kai kace mahaukaciya ce ,kikama 'yar mutane ki shage,shegiyar mata kodaddar banza ita banda farin tama wazai kwasheta mai bakin hali,ai wallahi dan sunga kece shiyasa zasu hadaki aure dashi da wata fitsararriyar suka samu ai bazata yarda ba a rabani da dan arziki a hadani da irin tsiya....
"Kai kai Harira wannan surutu haka kinata kwashe mata zunubi kina dorawa kanki ta hanyar zaginta"
"Ai matar ce na lura da cewa cikin dabbobi Kafin asamu irinta za'a yara"
Rufaida tayi dariya jin maganar Harira

Aunty Samira da take tsaye bakin kofar dakin dasu Rufaida ke ciki azo kiran Harira ta tayasu aikin da suke tayi niyyar shigowa taji suna wannan maganar bata shiga ba ta dawo inda suke aikin tana jinjina lamarin aranta ashe shiyasa suka ga alamun damuwa a gidan da suka zo har Rufaida bata wani nuna murnar zuwansu ba,lallai akwai matsala a wannan auren amma yaza suyi itada ko kusa bataso auren nan Rufaida ba koda ma ba wata matsala dan tana son Rufaida kamar Samiha.
Aunty Samina ta kalli Samira tace
Yadai Samira maike damunki
"Kedai bari kawai Yaya ashe 'dazu surikar Rufaida ce tazo tayi wa Rufaida duka ta shake wuyanta ta kusa kasheta"
Maganar suka cigaba da tattaunawa saida Harira ta karaso wajen sukayi shiru


*****
Sallamar Abba Bukar a falo yasa kowaccensu amsa masa da kokarin yi masa Sannu da zuwa ya amsawa matan nasa da ko wacce da maganar dake bakinta ga mijin nata ganin vaidawo yadda ya saba dawowa ba dan har hudu ta gota yanzun daya shigo,maganarsa ya dawo dashi daga tunaninsu
"Yadai kowacce tayimin kasake kamar nayi tafiyar shekara ba wadda ta iya koda mikewa ta kawon ruwa" yayi maganar da murmushi kan fuskarsa
Hajiya Kubra tayi hanzarin cewa
"Abban Wahid ka manta yauba girkin daya daga cikinmu na Maman Wahid ne kuma tunda ta fita har yau bata dawo ba"
"Kinga Ku share zancen ta"
Abinda ya faru ya sanar musu,ya kuma sanar dasu an daura auren Wahid da Rufaida da azahar a babban masallacin Zariya, kowacce ta jinjina lamarin,
Ya sake cewa
"Har yau babu mai kawan abincin da ruwan"
Hajiya Kubra ce ta mike ta kawo masa abincin da ruwan kadan yaci ya aje yakallesu yace
"Kayan lefe suna gidan ,Baba Ashiru kuje ku dauka akai musu,nayi wa Wahid magana asabar zaizo ya dauki matarsa kayan dakin kuma acan za'a siya ayi komai"
"To Allah ya sanya Alkhairi", suka fada badan sukansu sunji dadin wannan auren ba,da wadannan tunanukan suka shiga ciki su kara shiryawa busu jimaba suka fito suka yi ma Abba bukar sallama da har lokacin yana falo yana yiwa Ubaidullah wasa da shi baya bukatar a kara shiryasa Aunty Amarya ta daukesa suka fita a motar Hajiya Kubra suka fita taja su zuwa gidan Baba Ashiru

Kaya kam sunyi kyau da tsari kala arba'in ne akwati 6 su Momy Maryam busu kushe kayan ba sai dai auren ne basa so ko daya da su Aunty Samina suka fada musu abinda ya faru da Aunty Samira taji su Rufaida suna tattauna maganar da Harira, sun bawa masu kawo kayan tukwici mai yawa daganan masu kawo kayan suka tafi da tarin kayan soye soyen da aka hada su dashi da lemuka da Abdul ya siyo musu aka basu.*JININMU 'DAYA*

By Sadiya Khalil

41.

yanzu Gwaggo Lariya inaji ina gani 'dana ya zai auri irin tsiya"
Hajiya Jamila tayi maganar bayan cire hannunta daga abincin da Gwaggo Lariya ta kawo mata.
Gwaggo Lariya ta kalleta tare da cewa
"Eh to muddin ki ka zauna ba,amma da zaki tashi ki rabawa malamai kudi sai kiga aiki,tunda dai bakyason auren"
Hajiya Jamila tayi murmushi tare da cewa
"Lariya ke nan kina tunanin kan auran nan nawa ne ban kashe ba,da naji shiru na dauka asirin nawa ya fara aiki amma ashe lamfa lamfa aka yi min"
"Gaskiya kuwa dan nima abin ya bani mamaki danaji kai kayan shiyasa na fara shakku akan saninki dan nasan vazaki yarda ba,dan koni ma vazan yarda inaji ina gani surajo ya auri Rufaida ba bare kuma ke"
Gwaggo Lariya tayi maganar dan ta sake tunzura Hajiya Jamila
Hajiya Jamila tace
"Wallahi kuwa Lariya munafuntata sukayi,yanzu nama rasa mafita dan a dazu so nai nakashe banza"
Gwaggo Lariya ta jinjina kai daga bisa ni tace
"Yanzu dai tunda har yau ba'a daura auran ba yanzu zan hadaki da wata aminiyata tana da shige shigen malamai,nima tana yi min tayin naje nace mata bani da kudin biyen malamai"
Hajiya Jamila cikin murna da doki tace
"Yaushe zamu je gidan nata,kinga gobe zan tafi Nasarawa da sassafe"
Gwaggo Lariya ta nisa tace
"Ki bari anjima baban Surajo idan ya dawo saina tanbayesa muje gidan nata"
Da haka suka cigaba da fira kafin wayar Gwaggo Lariya tayi kara wayar dake gefenta tasa hannu ta 'dauka ganin mai kiran nata Gwaggo Hajiya yayarta yasata saurin 'dagawa da sallamarta Gwaggo Hajiyar ta amsa saida suka gaisa Gwaggo Hajiyar take cewa"
"Ki kira mijinki ki fa'da masa zaki gidan Yaya Ashiru,anjima zamu hadu gurin daurin auren nan Rufaida da Wahid,kuma za'a kai lefe
Gwaggo Lariya tayi saurin cewa
" Yaya Hajiya ina ce sai wani satin aka ce"
"Eh da hakane amma matar Bukar 'dazu tazo 'dazu tayi wa mutane Hauka a gidan Yaya Zainabu,ta kusa kashe 'yar mutane aini bansan munafunki da ya kai mata zancen ba"
Gwaggo Lariya ta shiga zaro ido jin zancen Gwaggo Hajiyar harda kiranta munafuka to da tasan itace ta fadi hakan fiye da munafuka fadamata Gwaggo Hajiyar zata yi,da haka dai sukayi sallama da cewar sai tazo
Daidaita nutsuwarta tayi bayan katse wayar dan kada Hajiya Jamila ta fahimta da take can daddana wayarta jin Gwaggo Lariya ta gama wayar yasa Hajiya Jamila dago kanta ta kalleta da cewa
"Naji kamar unguwa zaki fita"
Gwaggo Lariya da sauri tace
"Eh wallahi zanje gidan Yaya Hajiya,zamu tafi wata unguwa,amma ba zamu Dade ba zamu dawo yanzu yaro zanyi kira yaje wajen aikin su Baban Surajo ya fada masa",dan tasan muddin ta kuskura bata jeba zarginta za'ayi harda hadin bakinta Hajiya Jamila ta san zancen tunda itama kiri kiri take nuna kiyayyar su Rufaidan,da haka ta mike ta fita daga dakin zuwa wani ba jimawa ta fito kasancewar batada karamin da yanzu haka cikin adonta na kure adaka ta fito ta dawo dakin da tabar Hajiya Jamila data sameta tana waya wayarta ta dauka tana cewa Hajiya Jamila saita dawo ta fice Hajiya Jamila data bita da kallo a ranta tana ayyana tabbas babban abu ake tunda taga Gwaggo Lariya ta caba wannan adon baki ta tabe ta cigaba da wayar da take saida ta gama ta lalubi lambar AbdulWahid amma a kasheta ta sameta dan haka yasa ta hakura da kiran dan tuntuni take kira suna sanarmata akashe wayar take.

******
ABDULWAHID
Da farin cikinsa ya kasa boyuwa da albishirin da mahaifinsa ya tare sa dashi dan tun yana Abujar yaso sanar masa to sai ga matsalar Network baya samunsa a waya koda ya daga wayar ta katse ga wadannan kwanakin aiyuka sunsha kan AbdulWahid din kwana biyu

Saida aka shiryawa Rufaida gidanta sosai da kayanta masu tsada da Abba Bukar duk shi yayi komai sannan AbdulWahid ya dauki matarsa Rufaida suka tafi tare da wasu daga cikin "yan uwan Rufaidan su Aunty Samina da har kwanakin suna Zaria da zasu ganin gidan Rufaidan Ummi Hauwa'u da ba yadda ta iya ta hakura da irin auren da aka yi wa 'yarta da Gwaggo ta dinga yi mata ban baki kafin ta hakura
*****
Gwaggo lariya ta maida dubenta ga Hajiya Jamila
" Jamila kiyi hakuri an riga da an 'daura auren,Rufaida da Wahid sai dai mu sauya shiri,fitar da nayi 'dazu najiyo labari gurin Yaya Hajiya"
Wani kallo Hajiya Jamila ta yiwa lariya kafin tace
"Lariya wannan wanne irin magana kike min ta rainin hankali aure kuma aka daura kuma kicemin baki sani ba aiko a garin mahauta muke bazan yadda ba kikasan maganar kai lefe bare ta aure, ai a dazu na fahimci fitar tafiya kai lefe kikayi ashe ni zaki munafunta nufinki ban fahimci wayar da kikai bane"Hajiya Jamila ba tare da ta jira abinda Gwaggo Lariya ke fada ba ta zari hijabinta da makullanta ta fice tana kokarin ficewa daga gidan gaba daya da har zaure Gwaggo Lariya ta karaso tana bawa Hajiya Jamila baki amma taki koda sauraronta motarta da take kofar gidan ta shiga ta yiwa key tabar gidan ta nufi gidan wata aminiyarta da zata yi kwana daya a gidan daganan ta nufi gidansu nasarawa a ranta tana jinjina halin dangin miji

" Yanzu Yaya inaji ina gani 'dana ya auri wannan yarinyar ba yadda na isa nayi,kina gani ko waya raban da AbdulWahid ya kira ni yau ake kwanan sati don karna masa maganar Auren nan,ga uwa uba ubansa ya koreni daga gidansa"
Cewar Hajiya Jamila da take zaune a babban falon gidan shema'u take wannan maganar
Murmushi Aunty Shema'un tayi kana ta dubi Hajiya Jamila ta soma magana
"Ki kwantar da hankalinki Jamila ai idan sunsan wata basu san wata ba,dama nagama yanke shawarar ku tafi Abujar yau keda Rukayya ku zauna acan tunda shi Bukar baida mutunci idan yaji kina can zaice ki koma dakinki dan ba saurara mata zaki ba idan kuka je,tunda gashi Bukar din ya zuga gaba 'daya 'ya'yanki bama Wahid ba tunda kika zo nan waye cikinsu ya kira ki sai munafukan kishiyoyinki da ba kaunar zamanki suke a gidan ba bayan duk arzikin Bukar din dake akasha wahala gurin samu su da suka zo zuwan daga baya"
Murmushin jin dadin wannan shawarar da 'yar uwarta ta Hajiya Jamila ta mike tana cewa
"Ai Yaya yau ba sai gobe ba zamu tafi" da haka ta shige ciki tana murmushi




****
ABDULRA'UF
" Ra'uf anya kana da cikakken hankali kuwa"Ra'uf yayi saurin dago kansa daga kwanciyar da yayi saman kujerun falonsu jin maganar da Ammi tayi masa ya soma magana da cewa
"Ammi maina aikata kuma?"
"Kafi kowa sanin koma maikayi ace daga wannan lamarin yanzu ka daina hatta da zuwa aiki baka yi kadaina walwala bayan Ahmad ya sanarma ita hartayi aurenta ta manta dakai amma kai tana makale a ranka ,tunda muka dawo baka leqa gurin aiki ba"
Mikewa yayi daga kwanciyar da yayi ya maida kallonsa ga Ammin nasu yace
"Ammi sam yadda kike tunani ba haka bane,wannan maganar ba ita bace ta hanani zuwa aiki ba,kinsan hali na daban manta da itaba bazan hakura ta auri wani ba,kawai dai nasan inajinta a cikin jinin jikina har yanzu"
Ammi ta dan tabe baki kana tace
"Ai saikai tayi, Shureim ya kirani a waya na lallabeka ka koma gurin aiki dai"
Murmushi yayi yace
"Ammi kenan,eh gobe dama zan koma,dama hutun dana daukane bai kareba"
Murmushi tayi jin abinda Ra'uf ya anbata ta maida duk natsuwarta garesa tare da soma magana
" mai zai hana kaje kanemi Auren Inteesar Khan Dawud abokiyar karatun Sophie ina lura da yadda take nuna ma soyayya tun tuni,kaje gurinta a tsaida magana nasan su ba zasu yi mana haka ba"
Ido ya zaro Ra'uf tare da jin wata faduwar gaba lokaci guda taziyarcesa ,inteesar din zai nemi aurenta yarinyar da abokinsa Shureim yake fadamasa irin son da yake mata yadai kasa furta mata ne
"Ya kayi shiru Ra'uf ko ba kai maraba da shawarata ba"Ammi tayi maganar tana kokarin katse shirun Ra'uf kallon Ammi yayi yace
" Ammi shureim ne ke san Inteesar yanzu koda zanje gurinta saidai naje saboda na shigar da soyayyarta gareta"
Tsaki Ammin tayi jin gaba daya dan nata har yau hankalinsa baya ga duk zancen da zata yi masa ya karkata ne kawai ga Rufaida,banda haka ina zaice Shureim yana san Inteesar mikewa tayi ta bashi guri rai a bace
Da kallo Ra'uf ya bita dukda baya san bacin ran mahaifiyarsa amma dai gaskiya bazai amince da shawarar taba na ya auri Inteesar yarinyar da abokinsa ke so dukda ita bata sani ba amma shi ai ya sani idan yayi masa hakan bai kyauta ba ko 'daya, ga uwa uba shifa a tsarinsa bazai iya auren macen da ba 'yar kasarsa ba.

"Ya ko aminci da maganar da kikaje masa da ita"Dady ya tari Ammi da wannan maganar da take kokarin karasa zama gefen gado Da dady yake zaune akai shima
" ai dama na fadama bazai amince ba,kaima kasan halin yaron nan da gaddama,tunda ya nuna waccen yarinyar yakeso kuma bai same ta ba zai wuya a yanzu ya amince da wata macen"Ammi ta karasa maganar da alamun bacin rai a fuskarta
Dady ya girgiza kai tare da cewa
"Wallahi Asma'u ina san farin cikin yaron nan,sai dai a karo na farko nima ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login