Showing 36001 words to 39000 words out of 103712 words

Chapter 13 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7854

inkinyi haka wallahi zai koma tsakaninki da daddynmune kuma ku kyaleta don Allah gadai shegiya nan wanan munafukan halima Asiya yarta ta fada.
Yan iska duk sai kun bar gidan nan koda tsiya da bala,i babu shegiyar yarcin arzikin da zatazo ta mamaye muna gida ta hana mutane walawa saboda kwadayi .
Mairo data shigo motan bayani taji me nace don cewa nayi cin arziki aiba akan mu aka faraba don kowa yaci saidai idan ya manta yanzu.
Lokacin ta juyo gareni tana fadin kewa kike fadawa hakan mommy kowa jin hakan ban tankata ba nace gaba da yan suraitana ciki ciki ina jan tsuki.
Koda muka isa ban tsaya binta kan halimatu ba nashige aji ranan na hasala sosai na yanke cewa idan mun koma gida zan roki daddy ya mayar dani gidan mu.
Bayan an taso breakne halimatu tazo ajin mu take fadin kingani ko kinga wanan muguwar yau dai da idanunki kin gani ke nan halinda nake ciki.
Wallahi sun yaudareni zainab sunci amanat,,,, tareta nayi da fadin ni banga komai ba don Allah bar zancen wanan matar banso tunda ba a karkashinta nake zaune ba.
Ke zaki iya tuda kina da sauran kimarki a gidan ni kuma sun rabani da hjy mum yanzu kuma sun koma hattarata ga bakin aiki kamar boyar su haka na koma a part din nan.
Abinci na bude muka faraci tanata zuba surutu dayasa har naji abincin ya fice min a rai na kudurta zan samu daddy da zancen komawa hannun iyayyena da zama.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[2/3, 07:47] Aishatu Aliyu Musa=??>?p?: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

1?? 3??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Tabbas ba a nunawa shege hanyar neman uba saidai ki sani hjy malka duk wanan dukiyan dake gareni yanzu zan kara fada a gaban iyalina kuji sanadiyar kakan yarinyar nan na sameshi.
Ni Alh musa ba butulu bane ko kaza mai ci ta goge bakinta nafi gaban wanan yau har a samu daya daga cikin iyalina yace zai gorantawa iyalan Garba wani abu a cikin gidan nan wallahi karyane daddy ke fadin hakan a gaban iyalinsa.
Da akai komai a gaban idanunsa ashe yace hjy kece shedana a madadin yan uwana dana kafaku sheda a ranan kada wani yace zai matsawa yaran nan dana dauko a gidan nan da suna riko in samu lada.
Sai gashi yau hjy malka tayi kokarin take wanan dokan da sunan gida na diyansuns don haka babu dan shan miyan da zaizo gidan nan ya takurawa rayuwansu da sunan zaman riko.
Yau yar garbace ta zamo yar riko a cikin gidana ko kuma yar saudatu kanwata ce diyar dan uwana isa ta zamo yar riko a gidan nan ya juyo yana tambayan hjy malka din da tun farkon zancen take mamaki yadda yasan wanan zance.
Da ace yaran sun dawo gidane da sai tace a bakin mu yaji hakan don mu kadaine a wajen saiko yayanta da driver to ko driver ne ya fadawa Alh din ?
Ta tambayi kanta wanan zancen cikin mamaki kafin tace amma ai Alh kamata yayi ka tambya har in ma wanine ya tsegunta maka zancen kaji meya faru har na furta hakan garesu.
A,ahaa gareta dai don ita dayan ta kasance mai baki biyu wajen ki take donke ke rikonta yanzu gidan nan ita dayan kuma da kikabi da zagine har da gori ban fahintaba ni.
Shiru tayi kafin ta dago cikin karfin hali tana fadin aida munafunkin daya fada ma anyi sai ya fada maka ita metace dani har na fada mata hakan.
Kin dai fada ke nan marka aiko yaran nan basuci hakan gareku ba gidan nan nina dauka koba Alh kuke aure ba suna da daman zuwa wajen ko wacenku su zauna a karkshinta.
Balle kuma nan din daya zamo gidan wan mahaifansu kuma yan uwanku har wanan kalamin ya fito a fatan bakinki yanzu sai yarkice zata kwaba maki karshe.
Lalai tabbas munafukin nan yakai tunda komai ya kwashe ya fadawa Alh duk yadda akayi Sani driver keda wanan munafuncin ta fada a ranta.
Banyi magana bane don naga takai ga samun yadda takeso zubar mutuncinta don ko yarinyar ta bata ansa a bakinta ai yadda zata iya kwatan kanta gareta .
Kallon mijin nasu tayi yace agabana komai ya faru malka da wani zai fada min ba zan yarda ba zance yai maki kazadin da kike fada kullun an maki agidan nan ne amma sai gashi idon ki ya rufe har kuka tafi baku san ma ina tsaye a wajen ba nida bakona a lokacin.
Kai ta dukar kasa lalai in ba ta mata ba motarshi tana wajen a lokacin ashe yana ciki ke nan ake nufi lokacin lalai ta tafka babban kuskure nayin hakan a ranan data bari tabi shawaran yarta Asiya zaifi mata sauki amma ina zafin zuciya ya hanata yin hakan alokacin.
Muryan dadine ke fadin don haka kan taka min doka zan dauki kwakwaran matakin da nace zan dauka akan ko waye yace zai takurawa yaran nan tun farko.
Kafin daddy yakai karshe har hjy mommy tace dashi don Allah Alh kayi hakkuri kusukure aka samu ba za,a karan hakan ba insha Allahu bacin raine don Sadiya sata take mum sosai yasa naso in horata ga hakan.
Duk suka kallota tace kwarai kuma saida na tabbatar da hakan gareta nagane itace take daukar min kudi da wasu abubuwa yasa na dauki mataki.
Itama yar uwan shine tambayan da nake mata taso ta kawo min rashin kunyane harka jimu da ita idan ba haka ba aini ba ruwana da sha,aninsu.
Kuma ita din ta saka kanta cikin harkan kishin mu bata kallon kowa da kima a gidan nan lokacin hjy Kuburah tayi magana tace bako Mama ba don ba mecewa tayi mai rashin kunya don ba halinta bane.
Idan batayi yau tayi min ko karya nayi mata kuma ta fada a dan hasale don hjy mum tayi magana a lokacin abinda bata kauna ke nan taji don tana ganin batayi matsayin da zata saka baki a rigimanta ita da mijinsu ba ai.
Saida Dada ta saka baki ganin yadda hjy malka ta kwanta yasa daddy ya hakura bayan ya kara jadada masu akan kafin suka watse har lokacin hjy malka bata yarda cewa daddy ne yaga abinda ya faru da idanunsa ba.
Koda muka dawo ina cika saiga hjy mum tafito min da zancen nima nayi mamakin jin zancen a bakinta takuma fada min matakin da daddy ya dauka akai wanan yasa naji dan sasauci a zuciyana.
Sai gashi kuma a yammacin anty Nafisa ta dawo gida ba dadi ita da miji har abu yakai ga sakin daba gyara a tsakaninsu ga kuma karamin ciki a jikinta duk uban kudin da aka kashe da wanan bukin da baifi wata uku ko hudu ba a yanzu ya tashi ga banza tunda auren ba gyara kuma .
Mun dawo daga islamiya muka tsinci wanan bakin labarin a bakin Dada daketa yankan fada a dakinta don nashiga ingaida ita tunda tun safe ban shiga ba mun gaisa.
Nan take fada muna abinda ya faru cewa ashe shi din dan duniyane wai baison haihuwa matarsa ma ta gida haihuwa biyu yasa ta dakata da haihuwan.
Saboda baison mace mai haihuwa yasa ya nemi anty Nafisa din don yaga kanta a waye yake zatayi na,am da bukatashi sai gashi takiyin planning din daya bata tayi ciki ya baiya daga kaita gidanshi.
Wanan ya kawo masu fitina ba dadi yace ba zai zauna da ita ba tunda tun farko ya fada mata shirinsa taki daukan mataki don haka ko a zubar da cikin tayi planning ko kuma su rabu tace ba zata zubar da ciki ba tunda ta samu.
Sunsha rigima kuma uwarta ta sani amma bata fadawa kowa ba saidai tana tausan yar nata dako yaushe cikin bugo mata waya take tana kuka idan sunyi rikici dashi din ta bata hakkuri wai kada aji ai masu dariya saboda bakin kishi.
A karshe dai sai takarda ya mika mata ta bar mai gidansa hakan ko akayi da tace saita haihu zata bar gidan amma ya dauko mata yan sanda da mota yasa aka kwaso mata kayanta kaf a lokacinne gida aka sanda zancen.
Anan kuma bayan dan sandan ya korawa daddy komai yace baison har cikin ya yafe gidansu su rike idan ta haihu nan daddy yace a fada masa bai isa ba ko dan gidan uban waye shi a garin.
Da kyar dai dan sanda dayake na Allahne shi yabawa daddy shawara akan a kyaleshi idan an kwana biyu ko bayan ta haihu a makashi kotu ko kuma da daddy zasu iya hakkuri wata rana dole zai waiwayi abinda aka haifa masa shida kansa gidan.
Dada tace wanan ya dan kwatar da hasumin da daddy din keyi don bata san abinda ya tuno ba da kalamin dan sanda har ya hakkura lokaci guda.
Dada din kuma ta daukemu zuwa dakin Nafisa din wace muka samu kwance duk ta rame ta lalace ba zakice Nafisa bace da akai bukinta lokacin tana baka sha,awa.
Muna shiga dakin muna sallama Dada na fadin Allah sarki kibar kukan nan hakana yar nan tunda ya riga daya cuceki dan banza wanan yasa ake kyautata zurfin bincike akan mutum kafin ayi aure.
Haba Dada ki barta taji da abinda ya sameta koda anyi bincike din tunda Allah ya kaddara hakan saiya faru tsakaninsu ba makawa sai hakan ya faru din.
Tayi hakkuri tabarwa Allah komai ta dinga istigifar ga ubangiji shi zai duba mata lamarin insha Allahu na fada daga inda nake tsaye bayan Dada din mun kura mata idanu muna kallonta cikin tausayi.
Allah ya saka maki da mafificin alherinsa anty ya kuma saukeki lafiya ya baki mai albarka amin na fada ina shirin barin dakin yayinda halimatu itama ta amsa da amin daga bayana har mun juya naji tace Sister nasan dani takeyi don haka take kirana tun zuwan mu gidan har lokacin bukinta din dashi take kirana a gaban kowa.
Najuyo tace idan kinje ki dawo don Allah na amsa da to nafice nikan ina zuwa part din mu na manta da zancen ta don na samu mum tana fama da ciwon kai ko girki bata iyayi ba a ranan gashi kuma ya Addel yana gari yazo .
Hakan yasa na kwabe hijjab dina zuwa kitchen na dora ruwan zafi naji muryanshi a bayana yasa na juyo ina gaidashi yace ruwan zafi nake son in kaiwa Mum tasha magani tace kina nan.
Ruwan dana saka din na debo mashi a cup na hada dana surkawa na gora na mika mai ya karba har ya juya sai kuma ya tsaya yana fadin idan abinci zaki girka ki bari dare yayi zan fita inyo maku take away na amsa da to.
Bayan fitarshi na kashe wutan gas din na gyaro kitchen din na fito na koma wajen mum a falo na sameta zaune da alaman har tasha maganin a lokacin.
Kara gaida ita nayi kafin na kai zaune a gefenta zan fada mata abinda yace saita rigani ta dan dago tana fadin yayanku yace kibar girkin dare yayi ko ?
Nace ehh shine nazo in fada maki tace nima nayi tunanen hakan yaushe zaki gama dare bai maki ba yanzu shida da rabi har ya gwauta ai.
Nabi ta part din hjy mommy ne nagaida Dada sai kuma ta tsaya bamu labarin abinda ya faru da anty Nafisa kinsan Dada bata bari na fito ba ta kaimu wai gaida ita.
Gaskiyane basa so ai dama nasan hakan zai faru tunda basu tsaya sunyi dogon bincke ba a kansa suka dauki yarinya don kada ranta ya baci suka mika mai.
Damani ina ganinsa nasan dan duniya ne don daganinsa irin tashin turai din nan ne ba kwabo komai a sagarce yakeyinsa suko hakan naga bai damesu ba illa murna da sukeyi yarsu ta samu gidan hutu.
Dan gidan nan wani irin hutune bai samu ba inba yanzu da Alh ya kori yan aiki muke yan aiyukan mu da kanmu ba da yan aiki nawa ke gidan nan nasa dai akaji amma da za a zauna dashi shima ya fadi nasa nasan tana da laifi itama.
Bayan sallah isha,i har lokacin ina lake a wajen mum dana shafawa abonake a jikinta don tace ko ina jikin bata jin dadinsa a lokacin.
Ya Addel ya shigo falon da ledoji a hannusa da sauri na mike na karba na aje a gefen mum din fita nayi na wanko hannuna dake warin man na dawo mum ta dago tana fadin na dauka ai plates kije dauko muna.
Na amsa da hannu na wanko mum bari na dauko yana zaune shidai haka halinsa yake koda uwarsa bai yawan magana kamar sauran yan uwarsa zai zauna yayi shiru kamar maraya ashe shi.
Sai uwar ke magana ina shigowa da plate din tace amma kamar wanan abincin yayi muna yawa fa lokacin ya dago yana cire tagumin da yayi din yace ba abinci bane ai mum don nasan da wuya ki iya cin abinci a yanzu.
Ledan nake kiciniyar budewa jin yace ba abinci bane take away na fruit sald nagani guda uku sai dayan leda kaza guda biyu manya irin gyaran shagalinka kudinka din nan.
Sai kamshi ke tashi na dora daya a saman plate din nakai gaban mum din na aje komai a gabanta harda madaran hollandia na lwali kananu guda hudu.
Ina kokarin dora masa ya sake dagowa yace no ki barshi nawa na cikin mota idan zan shiga zan dauka nakune wanan ya fada kamar a gajiye yake.
Mama matso muci kinji ta fada shidai wanan abin da farin jini yake watau don dai nasan ba,a kwana biyu bamuci kazaba amma wanan din na daban ne na motso kamar yadda tace din.
Na mika hannu ina dan yaga naman takai hannu ta dauka mukaji sallaman daddu ya shigo hakan yasa ya dan sauko da sauri yana gaida daddy din da wuni daddy din yace.
Aliyu dama ka dawone ashe to ya Abuja din da fatan ayi nasaran tafiya dai ya dan sosa kai yana fadin dama yanzu nake son in nagama in shiga ina dakon kagama cin abincine sai inje in maka bayani.
Don yanzu shigowana ke nan gidan dazun munyi waya take fada mjn bata jin dadi shine na tsaya nazo mata da magani har na makara .
Ai nazo mata da wani Hafiz ya fada min nasoyo mata tasha da zanshigo ai kace nazo a makare ke nan ashe ka rigani tallafawa a nan suka danyi murmushi yakai kallonshi ga abinda nakeyi yace uwata babu ko tayi ?
Murmushi nayi ina fadin daddy sannu da dawowa yace naki ai baki ganni ba tunda kina gaban uwarki Allah daddy ina jiran ku gama da yayane ingaida kai na fada ina kumshe kaina cikin kunya.
Yau dadi za acine haka ya kara kallon abincin yana fadi mum tace dadi kan ai kullun kana bamu shi gidan nan munaci wanan danka ya sayo muna yace kada kanwarshi tayi girki yamma yayi .
Ka kyauta gashiko dama idan mutum ya tashi ciwo yana jin kawa kaga wanan abinda matasan yanzu basu ganewa ke nan sai su dauka kudi kawai iyayye ke bukata akullum ba kula ba.
A saka makane mum ta fada da sauri ya Addel din yace no ki barshi bari na dauko masa nawa a mota sai in sayo wani .
A,a ka bar abinka wata rana zaka saya min da sauri ya mike yana fadin a,a daddy ya fice daddy ya kai zaune yana fadin yaron nan tausayi yake ban koda yaushe kamar yana cikin damuwa yake ko an tambayeshi yace ba komai.
Shi sam baya da sakewane shiyasa nake fita???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? zancenshi mutum ya zauna kullun shi kadai yayi ta tunane ka rasa abinda yake tunane kuma lokacin yayi sallama ya shigo da ledan irin namu yake fadin daddy akaima can ne ciki ?
Yace miko min nan kafana kafan kayata fruit din nan yafi min komai dadi a cikin kayan nan don ina sonsa sosai su kuma suna kiuyan hada min shi kullum.
Ayya mum ku dinga hada masa don Allah yana da kyau wanda yakai shekarun ku yana shansa kullum don yana kara lafiya sosai a jiki.
Kai rabu da babankun nan fa mum ta fada a daidai lokacin da wayansa ya dauki kara yana kiciniyar fito dashi daga aljihunsa ya kara akunne.
Mu dai munji yace ina zan tsaya kuwa ina nan part din hjy kubura nazo duba jikinta kome tace mun daiji yaja tsoki ya kashe wayan yana fadin mutum bai girma.
Wanda keda tashin hankali haka gabansa zai tsaya wani fadan shirme inba hauka ba ni wai ko malka tana da tabin hankaline dai.
Wani abu ya farune ya Addel din ke tambaya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login