Showing 69001 words to 72000 words out of 103712 words

Chapter 24 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7848

hada zancen a tsakanin ku kafin kazo wurina watau ni gani tsohuwar banza mai yukan yanke zumunci bari kazo wajena ka laba ayi yankar kauna ko ?
Ke Dada wai bakya ganewane shifa so wani abune kada ku tauye min rayuwata mana don Allah zaku hada baki ku cinna min wanan mahaukaciyar yarinyar in kaita ina don Allah ?
Inda ubanka yakai uwarka nace inda ubanka yakai uwarka Dada tafada a hasale cikin mikewa tana haki kamar zata dokeshi daga inda hjy malka take tsaye ta kwala masa kira tace hafiz bakaji ko zan saba maka idan baka fita part din nan ba yanzu.
Kallon mummy din yayi kafin ya juya a kasalance wurin Dada din yace na dauka zaki taimaka min ki rabani da wanan auren alkakan da daddy keson yi min she duk bakin ku daya ban sani anywhere kuyi karku fasa din ai .
M ummy ce ta karaso acikin masifa agareshi tana rantsuwa idan bai fice daga part din ba zata saba mashi rai fiye da tsanmaninsa.
Lokacin Anty Nafisa ta dago kai ta kalleshi tace Hafiz wai bada kai mummy ke magana ba ka bari a lalaba zancen nan mana tunda ku duka bakwason junan ku.
Wani kallo yayiwa yar uwartasa tace yes kamar yadda baka son hadin nan ko ita sister na tabbatar da bata so don ko bashiri a tsakanin ku .
Shine daidai idan anyi auren sai suje can su shirya a tsakanin su tunda sunfi kusa Dada ta fada cikin daga murya har ya juya ya fara tafiya jin hakan yasashi ya dan dakata yana mai juyowa ya nuna Dada din da hannunsa.
To indai har hakane babu wanda ya isa kaf ya fasa wanan auren acikin uban nan ku muddin ina da raina ya nunata yace aisai ki zauna da ita ki jika kisha tunda kince hakan.
Shege ka fasa tunda kace haka in maka na mahaukata wallahi hafizu idan kaga an fasa wanan auren tsakaninka da Abu tabbatar bana raye a doron kasa ta karasa zancen a cikin bacin rai.
Anty Nafisa ta mike tana fadin saika fita tunda ka bata komai dama haka kakeso ai Dada ce zaka sama ko daddy dayayi ma wanan hadin meye na Dada a cikin zancen nan.
Kai ya girgiza a cikin yakaici yana fita daga falon yakai iya kololowan tashin hankali don yanzu ya tabbatar da wanan auren da daddy ke ikirarin ya zaba mashu mata yar mutunci yar albarka ba fashi sai anyisa.
Idan gaskiyane meyasa ba aiwa ya Addil auren dole bashi saishi da aka raina za a kakaba masa wanan kucakar yarinya da sunan aure wai fa zeey a matsayin matarsa.


ZAINAB IDRIS MAKAWA

[2/21, 14:52] Maman K: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

2?? 3??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.


Yawan jinini da mita irin na tsofi da Dada keyi yasa har zancen yazo kunnen hjy mum matar daddy Enugu take tseguntawa mum din nidai naji mum na fadin wanan abin matsala kawai yake son kawowa a cikib gidan nan da abarshi kawai zaifi amma Alh ya kafe dole sai anyi bai daukan shawaran kowa kan zancen nan.
Nikan ban tsaya ba don nasan cakwakiyarsu gidan ba karewa yakeyi ba sai randa rai yai halinsa garesu ranan da ba dayansu kila zasu daina rigima da baki kishi a tsakaninsu.
Sai gashi bayan magariba an gama isha,i daddy ya bugo yana kiran mum kuma tazo dani falonsa bamu kadai ba kowane ashe nagidan aka kira lokacin.
Kusan mun samesu afalon mune muka shigo karshe nida mum gabanane ya fadi azatona zancen karatuna daddy zaiyi a lokacin na samu waje na tsuguna ina gaida daddy din sai lokacin na kula da daddy Enugu a zaune falon shima nagaida dashi.
Na daiji daddy nafadin kaga abin ko kagani dukkansu nan suka shigo muna sokai sokai dasu don rashin tarbiya amma mama tana zuwa da yake tasan darajan mu ai kaga ta bimu tana gayarwa daya bayan daya.
Su ba yan gata bane su gaida mutane suna kallon sunfi kowa aduniya babu yar banza irin halima wajen nan data dauki rigan aro a yanzu ta yafawa kanta don girman kai.
Ku barta abindata sama anayine agidan daddy ya fada cikin takaici har mummy zatai magana ya daga mata hannu yana fadin dakata don Allah muyi abinda ya taramu a nan mu watse.
Saida ya kallo kowa ko din ya tabbatar da kowa yana fallon ne oho yace nasan ba wanda yasan dalilin dayasa na taraku a nan yanzu ko kuma wasu sun sani dai.
Dazun da safe zan fitane hjy tazo ta sameni da wani zance koda yake bankai ga jiba akai min sallama nafita shine yanzu na taraku a nan ayi zancen agaban kowa dake gidan nan yaji.
Hjy ko zaki maimaita muna zancen mu na dazun dake don Allah idan ba takura saiki kara muna bayani agaban kowa gamu gaba daya anan yanzu.
Dada ta gyara zama tana fadin akan zance da yaron nan ne hafizu na shekaran jiya hankalina bai kwanta da kalaminsa shine nazo na samu mahaifinsa kan zancen shi kuma bai samu saurarona ba sai yanzu da ya kiramu din.
Nan ta kwashe komai tana mayarwa su daddy din yadda ya kasance a garesu ranan saidai bata fito fili ta ambaci sunana ba saida mum tace Allah sarki ai itama mama din bata ko san anayiba wallahi don ban taba fada mata ba kuma ban tsamanin wani ya taba fada mata a gidan nan.
Ko a fada ko kar,afada ai yanzu baida magani boyon don dole dai tasan hukuncin da muka yanke a kansu din ina dai gaba dayansu duk mu muka haifesu don haka ba wani cikinsu da zan kafawa doka ya ketare minshi gaba dayansu ko.
Haka nace zan hada aure tsakanin hafiz da ita mama ita kuma mairo da jafar din salisu dake bauchi ni daddy mairo tace cikin zaburowa da mamaki.
Daddy din yace ko ban isa ba ke kiyi shiru don Allah mummy ta fada yace idan ma ba zatayi shiru ba tunda tana da wani uba bayan ni aisai ya isar mata tunda ni ban isa ba .
Kiyi shiru mairo kinji Nafisa dake gefe ta fada ke kuma Asiya da Nura dan babanku musa dake katsina sai halima da shawaran mahaifanta nake jira yasa abin dan daukan lokaci don sunce a bari suyi shawara kila suna da wani wanda suke son hadata dashine can gida ban sani ba.
Amma su wayan nan shawaran dana yanke ke nan a kansu yanzu don haka kowa a nan yasani aure nan da wata biyu masu zuwa insha Allahu.
Hannun hjy Mum ne a kafadana ta yadda babu mai iya gane hakan tana min alaman kada nayi wani motsi ko magana daga Allah saini sai ita muka sanda hakan na fahinci me take nufi hakan yasa banyi wani koda motsi ba a wajen.
Zaune nake ban motsa ba sai gumi da nake ji adukkan sassan jikina yana fita ina kasa fahinyar bayanin da daddy din keyi a karshe don gaba daya ban cikin hayacina a lokacin.
Muryan anty Nafisace da iyayi ya kaita ga magana tana fadin daddy adai duba wanan zancen don ke rufamin baki mara kunya har me kika dauki kanki a gidan nan ?
Dama ina tafe kanki ai ko baki nuna min kina nan ba kar kiji wai a rana daya zan daura maki aure dasu ko kin kawo miji ko baki kawo ba ina da wa yanda na yaba da natsuwansu da hankakinsu a tare dani zab samu daya daga ciki in daura naki auren da maishi a ranan.
Wani kallo tayiwa mahaifin nata sai Dada ne tayi karfin halin fadin amma kasan bata yaye danta ba tukuna a dan daga mata kafa har tayi yaye.
Hjy yaron nan baida matsala yana da kafansa ko ina yana zuwa ta yayeshi kafin lokacin dana diban masu yayi tayi aure kowa ya huta nagaji da nunani da mutane keyi agari hakana kanta.
Ina fatan kowa yaji abinda na fada suma mazaje na sanar dasu tun wacan satin donsu fara shirye shirye kafin lokaci .
Ya juya wajen mummy yace ke kuma ki fadawa danki bani hukunci in tayar yasani in yana son mu zauna lafiya yabi zabin da naimasa shine alheri agareshi.
Amma Alh bakai mi adalci ba gaskiya Malka na fada hakan kuma za,ayi banga abinda zan tsaya jira da yaran nan ba don ba wanda bai isa aure ba acikinsu.
Ko so kike a maimaita abin kunyar da kukaja min keda yarki a garin nan na zabin ranku da kukayi ba wani dogon bincike ni kuma na biye maku.
To ku sani bazan lamunta da wanan ba yanzu tafarkin gidan mu da muka gada iyayye da kakanni nakoma wanda kuma keda wani magana ko ja sai yayi inji .
But mummy ta mike tafita daga falon cikin matsakaicin tashin hankalin da bata taba tsanmanin zuwansa ba a rayuwanta yaya uku koma tace hudu duk a auren dole har da da namiji sam ba zata yarda ba .
Tana fita daddy ya kallomu yace kuna iya tafiya dan nagama daku idan ba mai magana kuka sosai Asiya tasa Dada sai fadi take lalai zamani akan zabin mahaifiki ke wanan kukan.
Mu lokacin mu har asaka lale akai gidan miji baka taba sanin mijinka sai anyi kwana uku kafin kasan waye mijin kuma haka zaka zauna dashi amma yanzu don jin dadi ai maku gata ku tsaya kuna kukan iya shege.
Ba Asiya ba koni ji nayi kamar in shake Dada ranan saboda bakin ciki kalaminta suna kara min zafi a zuciyana sosai ina jin takar da gaiya take zancen tana kara zuga daddy din lokacin.
Akwai cakwakiya a gidan nan lokaci daya ace za,a aurarwa mace da diya kuma bada saninta ba gaskiya .
Alh ya kamata ka dubawa hjy malka idan na matan za,a farayi kabar namijin ko kuma a farayin na namijin abar matan har muyi shirin mu irin na mata.
Wai dadatace ke wanan maganan tana nufin a fara aurar dani kafin su Asiya din da daddy yayi niyar hadamu a tare ke nan lalai ashe Dada ba kaunata takeyi ba a zuciyanta tunda har ta nuna tafi jin tausayin jikokinta a kaina gaban kowa.
Aiko mum naji tana fadin hjy idan akai hakan kuma ita mama din fa da za,a aurawa hafiz gashi ta kwallafa rai ga karatunta kafin Dada ta bada amsa dake bakinta daddy yace.
Abinda na tsara ke nan ba ruwana da wani shiri don nagama shirya komai akan auren nan ko bayan buki abinda Allah ya hore masu suna iya kaiwa yayansu a dakunan su.
Allah ya kyauta mum tafada ta mike tana kamoni tare da fadjn tashi muji mama ganin ban iya motsawa ba yasa mum din kamo hannuna ta mikar dani muka fice daga falon.
Har muka kai part dinta ta zaunar dani saman kujera kafin tace ki yarda da kaddara mama banson ki nuna komai akan hadin nan don nasan Alh yayi hakane dawani manufa da sai nan gaba za,a fahinci manufarsa nayin hakan akanku.
Duk wani abinda kowa zaiyi koya fada agaban ki kan auren nan banson ki nuna komai ki daure kiyi biyayya ga iyayyenki Allah na sane damai hakkuri baya barin ki tabe insha Allahu.
Mataukar kikaiwa iyayyenki biyayya baki watsa masu kasa a ido ba sai yai maki sakayya ta hanyar da baki zata ba don haka nake son kiyi hakkuri ki rugumi kaddaraki na aurensa da hannu biyu.
Kiyi kokari ki hade komai azuciyanki game da komai da zakiji akan hakan Allah zai saka maki da alherunsa insha Allahu na tabbatar Alh baiyi wanan hadin da wata manufa mara kyau akanku ba sai duba da yayi da yawan alherun dake cikin abin .
Kuka kawai nake haba mama kibar kukan nan kinsan dai bacza a taba hada kai dani a gidan a cuta maki ba abune na magabata bamu da yadda zamuyi akan hakan ki daina kukan nan.
Wanan yasa dan uwanki yayi tsaye saida Alh ya yarda da zancen karatun ki don ya samu dai ki samu karatub da kike buri kada aure ya tauye ki ga murdinki nason yin karatun nan.
Yasha fama da Alh kafin ya yarda da zancen karatun ki duk baki san wanan ba don haka nunawa kowa kedin mai biyayyace ga iyayyenki din ki nunawa kowa hakan bai dameki ba ki tashi maza yanzu ki shiga ki wanke fuskanki kada wani yashigo ya sameki kina kukan nan haka.
Kinsan gidan nan yanzu yazamo gidan tsegumi ba,a raina abin magana yanzune zakiji ana fadin abinda bashi kan haka don haka nake son ki nunawa kowa baki damu da hakan ba .
Da kyar na tashi nashiga ciki don yin abinda mum din tace nayi na shiga na wanko fuska na dawo na zauna samab gadona don hawayen da sukaki tsaya min alokacin.
Ina nan zaune najiyo muryan maman Yusura uwargidan daddy Enugu tashigo a raina nace gaskiyan mum ashe nan zancen ya kawota ba wani abu ba alokacin.
Ranan yadda naga rana haka naga dare barci sai wajajen asuba nasamu don ko mum bansa tayi barci da dadi rainmba a rana kowa zuciyashi ba dadi a gidan.
Washegari monday haka na tashi ina shirin bin anty Nafisa school har na shirya mum tasa na dan kurba ruwan shayi mai zafi don cikina ya walwale don tasan banci komai ba da dare tun abincin safene dana karya acikina na jiyan.
Bata zo sai waya data bugowa mum ajan cewa inna shirya in fito gata waje tana jirana koda zan fita saida mum ta kara ja min kumne kan kar in yarda inyi wani zancen dabai dace ba da wani.
Zaune na sameta cikin motan tana jirana ina zuwa ta bude min gaba gefen drive nashiga na zauna muka tafi mun dan bar kwanan gidan take fadin waike zancen daddy ne har yanzu a zuciyan ki ?
Zancenshi yakeyi kawai don yasan wanan abin da yake sonyi ba abu bane da zaiyuyu haka don wanan zamanin ya shige na auren hadi abin ma babu ko dadin ji ai gara dake.
Asiya da za,a dauka zuwa katsina fa ansan aure yana iya kai mace ko ina amma ace wai kamar Asiya za a hada da wanan don Allah.
Me Asiya tasani fisabilillah gaskiya idan daddy yai haka bai maku adalci ba a raina niko fadi nake wani dama da auren mashayi ai gara zuwa kauyen koda kuwa kauyen kauyayyene.
Itama din danata bacin rai don cewa tayi sister kiji min Dad fa wai zai min auren dole ina karamata haba dai sai kace ku di??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????n nan ba aimin auren hadi a daba balle yanzun nan dako mijin nan yaga iskanci.
A gurina mai saukine idan daddy yace na bar mai gidansa kawai saina tattara inbar gidan in kama haya ko in nemi gida aban nan quarters din staff din mu in zauna.
Amma wanan auren hadin gaskiya ba mai min shi a yanzu dai kan koda banyi ba balle yanzu wai kinsan mun taba soyayya na yara da Addil tun lokacin mummy ta sakani gaba saida ta rabamu tun wanan auresu na gida ya fita raina.
Duk da na tabbatar dashi nake aure a yanzu da duk wanan bai sameni ba da ina gidan mijina a zaune don Addil mijin aurene halinsa yana da matukar kyau sosai wallahi amma mummy ta rabamu.
Halin da nake ciki bai barni nayi mamakin zancenta ba don jin abinda ta fada kan dan uwan namu watau wanan yasa dukkansu sukaki auren hadi sukayi na son ransu ke nan.
Muko anki bamu dama mu gwada sa,anmu a wajen mugani koda sa,a sai wani hadin ganbiza da daddy yai muna inani ina ya hafiz mai zuciya kuma dan giya koda yan uwanshi da suke uwa daya ina ganin yadda suke kwasa dasu kullum shi basuyi daidai ba a idonsa.
Balle ni yanzu da zan zauna da sunan aure dashi ya rayuwan zata kaya a tsakanin mu nida yakewa kallon bagidajiya yar kauye kuma fa ?
Nasan akwai fitina kwance a kasa ga aurenki da hafiz tunda hafiz ba zai hakkura ba don yace ke ba kalan macen da yake so bace bayan hakan kin masa karama ga aure nasan da hakan.
Amma naso yayi hakkuri kubi umurnin daddy din yaki ya fahinceni shida mummy yanzu kuma ga zancen auren su mairo ya taso gaskiya daddy baiyiwa mummy adalci ba a nan.
Shi yana duban nawa auren yadda ya kayane shin daddy baisan da kaddara bane dama Allah baiyi zamuyi dogon zama da habbib ba ko kuma dayan mu na iya mutuwa zaman ya yanke ai.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login