Showing 51001 words to 54000 words out of 103712 words

Chapter 18 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7832

sakewa dashi kaf inkin debe anty Nafisava cikin yaran gidan duk ko da dadewan da na danyi a gidan yanzu dasu.
Kitchen din na nufa don in duba abu mai sauki naji wanan ya Hafiz na fasin me zata dafama ta wuce baka fada mata bafa kada tayo muna jagwalgwale don Allah.
Aiba don ka zanyi ba don dan uwana zan dafa amsan yazo min a takaice kuma na fada kowa naji ni kaina amsam yazo min ne a hasale don rainawa mutane wayau da yakeyi.
Kanshi kawai ya girgiza cikon wayencewa ya kuta nashige yake fasin mum wata rana saina karyawa yar nan taki kafa tana wasa dani wallahi ya Nasir yace wayaga ball ke nan.
Abinci lafiyayye nadafo masu kuma suka zauna sukaci harshi miskilin da suke faman cika wasu takardu a part din mum din wanda nasam shiya kawoshi part din dama.
Daki na samu mum kwance na zauna a kusa da ita muna hira take ja min kunne kan na kiyayyeshi don ba hankali ko kunya ke garesu ba insun tashi tsiyarsu.
Haka dai zaman ke tafiya a gidan muka koma hutu don ya kare munsha dogon hutu a lokacin daga komawa aji shidda zan shiga nida Halimatu sai kuma aka samu akasi sunan halimatu ya fito cikin yan repeating dole saita maimaita shekara kuma.
Aikuwa nasha zunde a gidan mu don sheri suka laka min cewa wai ina hurda da malamai a asirce yasa suke passing dina ko wani jerabawa son sunga ina da kyau.
Ita mummy ce wanan karon ta kashe wanan zancen kafin ya fito fili amma duk da hakan saida zancen ya dawo kunnen mu ranan kuwa hjy mum tayi fada saida anty Nafisa tace ai mummy tayi masu fada sosai kan hakan.
Don agaskiya mum tayi niyar kai zancen wurin daddy amma jin hakan yasa ta kyale zancen gashi kowa ya gani zai yaba sai cewa ake nayi kokari na
Wanda hakan yake karaba halimatun haushi sosai don har kyauta daddy yayi min don cin na farko da nayi ya sayo min lace mai kyau da takalma har da hand bag na yan gayu sai murna nakeyi.
Nasan yayi hakan ne don yan uwana suji haushi suyi kokari don tare zamu zauna dasu yanzu su kara zana jerabawan nasu a school din mu din.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

[2/14, 11:14] Aishatu Aliyu Musa=??>?p?: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

1?? 8??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Hjy mummy da mamaki ta dawo gidan tana barazana wai bata yarda yarta ya haihu ba watakila an mata hakan ne donvta dawo daga unguwar.
Wanan yasa tun a mota da daddy ya kirata take yankan sababi dashi ya za,ace ta haihu kuma wai agida abu kamar almara don haka ita bata yarda ba har saida ta shigo gidan .
Ta fara ganin alaman gaskiya don jin hayaniya yan gidan da ake a ciki murna kamar yadda ake taya mai haihuwa da wanda ya shafa fari ciki a kasan hausa.
Nan ta shigo tana fadin wai dagaskene baby ta haihu din abinda ta shigo tana fadawa mutane ke nan a dakin cikin fada tana shigowa falon dake cike da yan gida suna murna da haihuwan don yanzu gidan ya koma gidan jama,a cike yake da mutane don daddy Enugu daya dawo da nasa iyalin.
Kallon mamaki kowa ke mata don basu tsamaci hakan gareta ba farin ciki da jin dadi suka zata a wajenta don Allah ya sauke yarta lafiya a gida kuma.
Mamakinsu bai kare ba saida ta furta wanan ai gangancine dole a dauketa akaisu asibiti daga ita har abinda ta haifa din a duba lafiyansu a can.
Lalai Marka baki da imani kuwa ina wanan zance mara dadi haka ya fito a bakinki kuma ga yar ki ana farun ciki zakizo da zancen banza yanzu kuma ?
Wani asibiti kuma kike zance yanzu Allah ya rabata da talan munta gaban mutane ta haihu daki daga ita sai kanwarta data dafa mata baya lafiya yanzu kizo muna da zancen banza.
Don kudi yaiwa mutane yawa haka kuma kice aje asibiti yanzu don hauka ai wanan ya zama kuwa bayan halri ke nan kuma ai saida aka haihu za ayi zancen asibiti.
Wani kallo mai alaman shock tayiwa rasarkuwar nasu Dada tana fadin wace kanwarta wai badai mama ba don yanzu dole itama da mama take kirana agidan ko uwar masu gida tun ranan da Dada taci mata mutunci a gaban mu kanta kirani da Abuwa.
Wa kuwa inba Abuwa ba itace dai me wanan karfin halin ita ta karbi haihuwar yar uwan,nata sai kiran mu kawai sukayi daga baya bayan sun gama zugansu a dakin su kadai.
Wai baby tana da hankali kuwa Maamah ce zata kira ta kama mata haihu mama dabata ko san inda ke mata ciwo ba tunkun ya Malka ai farin ciki dai zakiyi tunda ta sauka lafiya Allah ya tsare gaba kuma matan daddy enugu uwargidan ta fada daga inda suke tsaye cirko cirko suna kallonta cikin mamaki don basu zaci hakaba gareta.
Fitowan hjy mum da jariri a hannu tana fadin ku shiga mungama tana ciki yasa mummy din juyawa tana kallonta mairoce ta mika hannu da sauri tana fadin hjy mum kawo babyn mu gani me aka samu.
Tace gashi kun samu baby boy mai kama da ubansa sak har dan dingon nan na habib yaron nan saida ya dauko don kara ta fada tana???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? dan dariya fuuuu mummy ta wuceta ba tare data shiga ba sai sauran suka bita a baya.
Nikan wajen su mairon muka tsaya munawa baby din kallon kwam da shawa,awa tare da jin dadin haihuwar yar uwar tamu din a lokacin don abin farin ciki ya samemu.
Kunya nakeji naji ance wai ai zainab ce ta tsayawa anty Nafisa ta haihu don ko kowa haka yake fadi a gida ta haihu ita da maamah ai maamahce ta karbi haihuwan.
Muna part din har yamma na tsaya kara gyara dakin da fiddo mata da kayan da zasuyi amfani dashi ita da jaririnta su daddy suka shigo su ukkunsu dashi da mahaifina da daddy Enugu.
A falo muka tsaya suna fadin ina abokin namu ance mun samu abokin kokuwa mai karfi jin muryansu yasamu fitowa ko maijegon fitowa tayi tare damu don ta gaidasu din.
Muryan mommy data rigamu fitowa tana fadin gashifa mai karfi dashi haka tayi kasadan haihuwa a gida su kuma suka biye mata bayan kowa yasan yanzu yadda haihuwa yake tattare da hatsari gashi kuma na fari.
Sai naji daddy din na fadin Allah ya kawo muna sauki an haihu a gida shine saukin aida ake fata daddy enugu ya fada yan kuda na kwana inji manya yana karban yaron daga hannun Asiya.
Mr Enugu gasadane hakan ai daga ita sai maamah suka haihu don maamahce doctor tayi karban haihuwan don wauta ta fada rai bace.
Daddy dasai murmushi yakeyi yace interesting ashe zan samu likita mace a gidana ke nan gaba kinyi kokari sosai mamana haka ake son karfin hali ga mutum ya koya ya iya Allah ya raya ya fada yana karban yaron a karshe shima.
Hjy mommy bataso jin hakan ba ta juya ta shige tana jininin abin babane ya kallo inda nake yace ku bani dabino da dan ruwan zamzam idan akwai.
Daga inda Anty take zaune don basu girma ta dan kalloni tana fadin kije cikin side drower dina suna ciki ki dauko ashe ita kan ta tanadi komai akan haihuwan na fada a raina lokacin dana juya.
Na dauko na kawo mashi ya karba ya dan saka dabinon a baki yayi laushi kafin ya fitar ya karbi yaron daga hannun daddy din ya gyara da kyau ya dan daga yaron daidai kunnuwanshi yana mashi ikamah duka kunnuwa biyu.
Kana ya dan kwantar dashi ya zuba mai a baki tare da addua a bakinshi ya dauki lokaci yana hakan muna tsaye mun zuba masu ido.
Ikon Allah saiko yaron ya lashe yana tandan baki muka sa dariya ya dade yanawa yaron addua kafin ya mikawa daddy Enugu shima yayi suka mikowa mummy datafito ta tsaya a gabansu.
Ni dai daga nan ban koma ciki ba part din mu na nufa nayi dan gyare gyare kafin yamma ya karasa don ba zancen taya mum girki ranan don nagaji nama samu tayi abinta.
Ban koma part din hjy mummy ba don jikina daya fara dibge min saboda rikon da anty tayi min har bayana nake jin yana dan min ciwo da hakarkarina saboda wuyan da naci a lokacin.
Ko washe gari haka na kwanta baya nayi sallah don gaba daya jikin nawa yayi min tsami ina jin kamar zazzabi iri mai taunan jiki din nan zai kamani.
Saida na dan farka nasha magani jikin ya dan sake haka kuma da nayi wanka sai naji wasai har na samun daman leka maijego ina shiga tana zaune taci kwaliya tayi kyau zakice ba ita bace ta koma jagwal a yan kwanaki.
Har mun dauka ko damuwan rabuwa da mijintane yasa haka saboda ko yawan surutu ma batayi sai yawan jan tsuki da ajiyan zuciya sai idan naje ina damun ta da tambaya takan dan sake har muyi hira wani lokaci.
A Kwana biyu ban samun hutu hankalina ya kasu ga karatu ga jigilan maijego da kusan komai nike mata haka kuma ban yarda na sake abinda nake dan kamawa mum ba a part din mu don gudun zuciya.
Yau ma shiga nayi na atamfar ghana da mum ta dinka min lokacin wani bukin kawarta da sukayi yana cikin wanda tayi min na fitan buki don gaskiya mum akwai kulawa sosai ba laifi.
Kida ke tashi a part din hjy mummy dabi,ansu ke nan da zaran daddy ya fita za,a kure kida kamar gidan kafirao wasu yan gaye har kitchen nabi hjy mummmy nagaida ita ta amsa min ciki ciki kamar yadda ta saba don ba sakin fuska ko annashuwa tsakanina da ita sai agaban mutane niko ban saba sai nake shareta idan tayimin hakan.
Har na dan juya naji tace yauwa maamah taimaka min ki kaiwa yayanku abincin nan tun dazun ya bugo min wai yana jin yunwa niko sai yanzu nagama.
Dan tsayawa nayi ina tunanen wani yayan nawa a ciki take nufi ganin hakan tace yayanku hafiz mana mika masa yana dakinsa kwance.
Jiki ba kwari na karba tare da tunanen zancen mum ko yaushe tana min fadan karna yarda taji ance wani yasani wani aiki a bangaren samarin gidan inba haka ba raina zai baci.
Don shi duk zama a gidan dasu ban taba taka kafana ni kadai a part dinsu ba sai gashi yau mummy din ta aikeni kuma banda halin cewa banzuwa ta tuztuzgi ubana ba wani aiki bane wajenta .
Dole na karba na kama hanya taimakona guda ranan da muka shiga gaidashi wai yayi accident dasu anty Nafisa nasan dakin shi don haka na nufi wajen kai tsaye da kayan abincin.
Gabana sai faduwa yake daga kofa na tsaya ina kwada sallama shiru hakan yasa na kwankwasa tare da murda kofan lokaci guda ina sallama.
Yana zaune dagashi sai gajeren wando ya mike kafa daya ga sigari yana busa ga kwalban giya ya rike da hannu daya idanuwansa da suka kada sukayi jajir ya dago yana fadin.
"Ke ubanwa yace ki shigo min daki haka kai tsaye ashe baki da hankali dama haka ban sani ba ubanwa ya aikoki min daki ma ya fada yana kakafeni da idanuwansa.
Cikin dan rudewa ina i,iniya nace dama hjy mummy ce tace na kawo maka abincinka don Allah kayi hakkuri shout up my friend don kina doluwa shine zaki shigo min ba tare da nabaki izinin shigo min ke dabban inane wai ?
Ga abincin na aje a gabansa don kiris ya rage in fara amai saboda warin giya da taba daya game dakin wanda ko a hanya naji warin taba damuna yakeyi sai kaina ya daure balle wanan dakin daya dauki warin abubuwan lokaci guda haka.
Da sauri nadago na juya don in fice daga dakin naji yace cikin tsawa ina zaki haka dakata kiji wallahi duk naji wanan zancen a bakin wani gidan nan saina kusa kasheki da duka ba kuma abinda za,ayi tunda bakinki mai gulma yaja maki.
Duk da tsoronsa da nakeji haka bai hani fadin ni ina ruwa da zanje in fadawa wani wanan tsakaninka da ubangijinkane ai na fada ciki ciki a zatona ba zaiji me nace ba amma sai naji yace.
Kika ce me ashe baki da kunyane haka zan tatakaki wurin nan yanzu idan kika kara magana ya dan yunkura kamar zai mike na kwaso da gudu zuwa waje ina haki daidai fita dan corridor su mukaci karo da ya Addel dake shigo.
Cikin mamaki da al,ajabi yake kallona kafin yace ke zeey meya kawoki part din nan ina dan waiwaye nace ba hjy mommy bane taban abinci wai in kawowa wanan yayan shine don nashiga na sameshi yana shan taba yace wai inna fadawa wani saiya halakani.
Kallon kofan ya Hafiz din ya danyi kafin yace kinga tafi ina zuwa kar kuma aji wanan zancen a bakinki kindai san halinsu daga yau kuma kowa ya aikoki nan part din kece na hanaki shigowa ko mum ta hanaki na gyada mai kai ina wucewa da sauri ina dan waigowa kada ya biyoni a baya ya shakeni kamar yadda yace tunda na fadawa ya Addel din.
Ban koma part din nasu ba don tsoron da naji kada ta kara turoni kai masa abu don haka na wuce kai tsaye wajen mu mum tana daki lokacin tana barci don haka na shige dakina na kwanta sai tunane nakeyi a raina.
Wai ashe haka dama warin giya yake dama ashe ko dadi baida kuma mutane ke sha bayan Allah ya haramta shanshi me suke ganewa a cikin wanan abin mai wari ?
Ya Addel dayake shigo dakin anty don su gaisa yaga baby yaji anty Nafisa na fadin wai ba muryan Zeey naji ba ina ta tsayene kuma tana tambayan tsohuwar da suke dakin tare don mummy bata yarda kowa ya zauna mata da ita ba ita da kanta ta samo mai zama da yar nata.
Shiya bata amsa da fadin itace yanzu na hadu da ita wai mummy ta bata abinci takaiwa Hafiz daki shine ya korota ta fito da gudu har tana karo dani.
Akan me zata aiketa dakinsa kuma shi baya zuwa ya dauki abincinsa da kansa mummy fake kara bata Hafiz yake iskanci dayaga dama abincin ma ba zai iya zuwa ya dauka ba sai ankai masa.
Haka kawai ajawa yarinya zagi ko duka ga banza haka su mairo suka dauko iskancin nan don sunga tana min abubuwa sukaso su mayar da ita boyansu saida na hana.
Baiyi magana akan zancen ba illa cewa dayayi da ita ya kuka kwana tace sorry ance jiya daka iso ka shigo munyi barci yau da safe ake fada min kazo jiya mun kwanta ya hanya ?
Yace Alhamdullahi ashe an sauka barka da arziki Allah ubangiji ya raya muna yasa dadin musulmine ya tayar muna dashi ta farkin addinin musulunci ba kunya ta amsa da Amin woo bros.
Allah ya nuna muna auren ku kuma matanku su haihu haka ayi dozin dozin yace haba sai kace za,akai kurmi indai andan samu sai a huta zaifi suka kwashe da dariya.
Tace ai haihuwan baida wuya saidai zullumi yace ai ashe me sauki kika samu har kike fadan haka tace gaskiya ka bari abin ba dadi ai nida zainab mukasha tumulun mu dakin nan har na haihu dagani sai ita.
Kai wace zainab din ya tambaya cikin mamaki karara a fuskanshi tace zeey dai tamu zainab din mum aika bari wallahi shiyasa nake son yarinyar nan har cikin raina tanada hakkuri da sanin ya kamata.
Yace amma dai kunyi kasada zainab ce zaki tsaya ta karbi haihuwanki kema Nafisa nan ji nayi da kike fada min kamar ba gwareki a ginan nan wallahi don haushi.
Ta kwashe da dariya suka dauko zancen mahaifin yaro tsohon mijinta nan ta bata rai tana fadawa dan uwanta damuwanta na rashin zuwanshi yaga babyn kuma bai aiko kowa ba.
Hakkuri yake bata yace kiyi hakkuri wata rana ai zai nemesa balle ma dole yazo don daddy ba zai kyaleshi ba ai kodon aiwa yaron nan gata koni aka barni dashi zanyi maganinsane ai balle su daddy balle gasu baba garba akusa da daddy Enugu nasan dole zasu dauki mataki kafin suna yazo ai.
Shigowan mummy ya katse su kamar kullun in suna magana tashigo sai ya fice don baison wani abu ya hadashi da ita bayan gaisuwa tun lokacin da tayi mai tonon sililin a tsakar gida yana karami ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login