Showing 96001 words to 99000 words out of 103712 words

Chapter 33 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7846

hakki.
Tare da godewa Allah daya ban ikon fadin hakan koba komai yadai ji zafin zancen ai tunda ya taso hakan a kaina bada dan giya daga zuwanka sai masifan tsiya haka ?
Wanan abin dame yai kama dama ashe haka matan yan giya suke famane da tarun hakkuri da takaicin rashin zaman lafiya indai hakane gaskiya daddy ya cutawa rayuwana da aura min dansa Hafiz da yayi.
Baby kina ina ne mummy gani nan hanyar gidan hafiz daga nan zan wuce office ta fada bata tanka mata ba ta kashe wayan nata tana jan tsuki a daidai lokacin da mai gadi ya bude mata get din gidan ta tura hancin motanta ciki ke nan.
Don hankalinta bai kwanta ba ga wayan da taji mahaifiyarsu nayi da dan uwannata daya kira uwar yana masifa sai ya halaka yarinyar nan ko ya bar mata shedan da ba zata taba mantawa dsshi ba har abada.
Tun a waya ta fara surfa masa zagi ya kashe wayan haka ta kwana da zancen a ranta ta tashi dashi hakan yasata sammakon fitowa daga gida ta nufo gidan hafiz din tun misalin karfe shidda da wani abu na safe shinr uwar ta kirata ganin tayi sammakon fita haka.
Tayi mamaki data samu kofan gidan a bude hakan ya nuna a budema gidan ya kwana ke nan ba,a rufe ba har gari ya waye haka kofan yana bude kai tasa ta shiga ko ina shiru a gidan .
Hakan ya bata daman fara kiran sunan kanin nata daga inda take tsaye din ga kayan ruwan daya watsar wanda na kawo masa da tiren da cup har goran ruwan duk a watse cikin falon.
Sai guntayen taban daya zuka ya warwatsar a kasa da kwalban yar mitsitsiyar giya duk a falon watse jin bai amsa ba yasa ta nufi kofana tana nocking tare da kiran sunana a lokacin.
Can nake jin muryanta sama sama a inda nake zaune wajen dana idar da sallah ina addua tare da tunanen makoma a yau tunda yace sai ya halakani idan ya kamani kuma dan giyane ba hankali garesa ba zai iya hakan dayace yasa na kasa fitowa daga dakin.
A hankali na bude dakin tana tsaye a kofan ta bini da kallo tare da fadim bai maki komai ba dai ko na girgiza kai a cikin takaici ina bata hanya don ta karaso dakin tace ki biyoni falo.
Iya abinda ta fada ke nan ta juya zuwa falo din nabi bayanta din muna isa yana isowa wajen yake fadin zanyi maganin kine yar iska mara mutunci.
Hafiz har a gabana kake gwada rashin mutuncin naka kome ka zauna kema samu waje ki zauna ta fada in a serious voice ga kowan mu kusa da ita na zauna a darare don kada ya taso yai min dukan dayace a banza.
Dan shiru tayi kafin ta dago tace dani yau baki zuwa school ne da har yanzu kina daki da sauri na dan kalli inda yake zaune din ba tare da nayi magana ba sai cewa yayi wata tsiya takeyi a schoolbdin koda taje tace ban tambayeka ba malam kafin kace min komai ka kwashe wanan kayan kazantan naka daga nan kafin mummy ko daddy su iso gidan nan.
Tunda kai baka da hankali ka rasa inda zakayi shaye shayen ka sai tsakiyar falon matarka don hauka hafiz kako san alhakin hakan ba zai barka ba hafiz wanan wani irin cin fuskane haka wai ?
Anya hafiz kana tunanen gaba kuwa kashe mummy kakeson yi da bakin cikin ka kome an maka auren nan na gida don ka natsu ka dawo hankalinka amma ba a huta ba duniyace fa hafiz tsawo da fadi gareta hafiz.
Komai shakiyancin mutum ba zai iya ganin iyakarta ba saidai taga nasa hafiz sai yaushe ne zaka natsu kaiwa kanka fada akan irin halaiyan nan mm akane hafiz ?
Yanzu ka duba don Allah wani mai mutuncine zai shigo gidan nan haka ya kalleka da daraja ko ita din tayi daraja a idon mutane an samu gidan ku a haka ?
Saidai ita matarka da yanzu ya zamo mata dole dole kuma tayi hakkuri dakai tunda kaddaran aure ya hada duk shaye shayen baban boy bai taba yinsa gabana ba asalima bansan yanayi ba sai bayan rabuwan mu nake jin hakan amma waya sani kaga koni matarsa bansan da yanayi ba sai a bakin abokin iskancin nasa yanzu nake ji.
Ki bar hadani da wanan kucakar yarinyar da sunan matana a gidan nan wanan fitsarariyar kucakan zaki kira da matana ?
Au matar waye a yanzu in ba naka ba kana da sauran ja ke nan ashe har yanzu baka fahinci manufar daddy na hadaka aure da yar uwarka ba to bari in warware maka idan zaka fahinta.
Jiya daka dawo a mayenka ka fada min idan wata kake aure ba ita ba idan iyayyenta basu ji wanan haukan dakai mata ba jiyan nan amma ita gata ta shige daki tana hadiyan bakin cikinka.
Yadda kake ganin an manna maka ita itama din hakan take gani tsaban biyayya ga iyayyene kawai kaganta a nan din zaune dakai wani kallo ya watsa min daga inda yake zaune din.
Tace kwarai kuwa don a rufawa juna asiri daddy ya baka wace yake ganin zata iya hakkuri dakai a cikin dangin ko dangin aiba kowane zai iya yin hakan ba.
Enough don Allah kina fadin haka saita dauka ita din wata tsiyace ai nifa ban kaunar yarinyar nan a rayuwata don ku sani.
Anji a yanzu baka kaunarta itama bata kaunar ka ai amma yadda tayi hakkuri ta zauna kaima ka danne duk abinda kakeji game da ita a zuciyar ka yanzu ku zauna lafiya kada kuba iyayyen mu kunya.
Keda kike ta zncen iyayye su zo su zauna da ita mana kosu ba wani a cikin dangi tunda bani kadai bane namiji ai ko it mum bata da diyan da zata hadata dasu sai ni ?
Hafiz ta fada da karfi tare da mikewa tsaye tana fadin ka iya bakinka kada kazo ka fadi abinda zai zamo maka dana sani a gaba.
Bani dana sanin komai ko agaban akan wanan mai zubin wawayen zan dawo ina dana sani kome nazone ayita ta kare a daina damuna da zancen wanan yarinyar ana katse min aiyukana dake gabana.
Au haka kace ba zaka saduda ba ke nan ta kalloni tace ki tashi kije ki shirya ki wuce school kada ki makara wanan bai san ida ke masa ciwo ba tukun shima ya mike yana fadin idan taje ta tsaya can kada ta dawo gidan nan .
Ni dai nashige ina fadin dayafi nono fari a zauciyana a gurguje na shirya na fito na samesu yabini da mugun harara yana jan tsuki ta mike tana fadin mu zamu tafi kaiwa kanka tunane akan hakan.
Ban tunanen komai wallahi indai akan wanan yarinyar ne ta gama zama a gidan nan tace muje kyale mahaukaci idanta dawo ka koreta ina shike nan dai ?
Motan ta bude muka shiga muka barta ciki har lokacin fada take kwasa dashi tana fadin banda haukan giya a aura maka mace kamar wanan ka tsaya kana bura uba da hauka wai kaiga dan iska ?
Baki dai tsaya ya dakeki ba ko ta juyo tana tambayana hakan da kyat na sauke numshi na girgiza kai tare da furta a,a gareta ina hawaye .
Kiyi hakkuri don Allah haka yake tun farko da bakin zuciyan nan nasa na banza balle ya fada harkan drugs yanzu shine iskancin nasa ya karu haka.
Zancen yakeyi a yanzu baisan babban kuskuren da zai tabka ba a nan idan ya sake aka raba aurensa dake ba baki nayi masa ba wallahi sai yayi kuka da hawayensa ba yana muzantaki a yanzu ba nan gaba zai raina kansane a kan hakan.
Ina dai baki fadawa kowa wanan zancen ba zeey don fadan zancen nan zaizo ya shafi kowankune don mutuwan aure baida dadi wallahi ko wani irin aurene kuwa saiya tabawa mutum zuciyansa.
Kiyi hakkuri duk wanan haukan shirme yakeyi duk ranan da kuka zama daya dole ya sauko daga duk tsiyar da yakeji avyanzu balle komr hafiz yayi baya sa laifin hakan saboda yana da daurin gindi.
Both mummy da daddy suna da hannu cikin lalacewan hafiz
Don sun gwada masa gata fiye da tsamani yanzune daddy yake son nuna masa matsayinsa na uba agaresa an riga da an makara ga hakan ko .
Nidai ban ma jin wasu zancen nata saboda hawayen dake zuba min duk da na dan makara ranan bata yarda na wuce class ba saida taga dan natsuwa yazo min ta rakoni har bakin ajin don ta daukar min excuse ga malamin dake ciki lokacin kada ya hanani shiga.
Ranan haka na wuni a cikon bacin rai sai faman sake sake nakeyu a zuciyana kan yadda zamu kwashe dashi idan na koma din tunda ya furta kada in dawo masa gida a lokacin.
Kamar yadda mukazo tare itace tazo ta daukeni don komawa gidan sai naji dan sanyin hakan datayi min sai dai koda muka isa gidan arufe muka samu gidan da katin kwado ya saka ta baya.
A gabana ta kira mum tana fada mata abindake faruwa mummy din tace wai hafiz yana da hankali kuwa ko sai na bata mai rai akan zancen nan ne wai ?
Kafin tace yanzu ina mama din tace gamu tare da ita gaban gidan tsaye sai mummy din tace ku dan jira yanzun zan kirasa ya bude maku.
Amma anty dakin bari na koma gida kawai zaifi don karki tafi yazo yai min wani wullakancin daya wananbdin kuma tunda yace ba bar mai gidansa.
Ki koma ina zeey baki yarda da zancena ba ke nan komawan ki gida ai shine babban illa kuma kikoma kice masu me tunda ba sakinki yayi ba balle kije da tushe.
Gun baba zan tafi ba gidan daddy zan koma ba na bat??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a amsa da hakan sai naga ta dago ta kalleni kafin ta girgiza kai tace shi baba garba din shine baisan tashin hankali ba ko ?
Ai kina zuwa gida zance ya baci harma in ba ai hankali ba sai zumuncin su ya baci da daddy kan hakan don wanan ba karamin zance ba.
Jan bakina nayi ban kara magana ba saboda tunane sa bakin ciki dake cina lokaci guda nine yau namiji kewa koran kare haka kuma ina lake saboda iyayye.
Baifi rabin awa daya ba sai gashi da mota fuuu ya shigo saida maigadi ya kauce mai da sauri kadaya take shi muna kallonsa ya fito yana busan iska cikin tafiyan kasaita.
Yazo dakey din baiyi maganan komai ba ya bude gidan zai juya ya tafine naji tace dashi abinda kayi ka kyauta ke nan hafiz kai me kake son ka zamane wai ?


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[3/7, 10:17] Aishatu Aliyu Musa=??>?p?: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

3?? 1??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Tare muka shiga ciki da ita bata zauna ba sai bin ko ina da kallo dayi nagidan ga falon sai warin taba sigari da wani tsami da nake zaton na giyane .
Daki na juya zan shiga don ban iya jure jimirin wanan takaicin a idona da hancina naji muryanta tana fadin hakkuri zakiyi zeey ki fito ki gyara wajen nan don dan iskan baisan inda kansa ke masa ciwo ba har yanzu shi.
Dole ke zaki zage ki gyara gidanki kada wani bakon kunya yakai ga shigo maki gida na hankan ga kinga akwai nauyi da kunya sosai don wanda bai sani bama sai ya sani yanzu ga halin da mijinki yake ciki ai.
Cikin kuka na juyo ina fadin anty bazan iya wanan abin ba gaskiya kuyi masa magana idan zaisha ya tsaya waje don Allah yasha abarsa warin abin nan yana sa kaina juyawa sosai wallahi.
Nasani zeey ko baki fada ba nasan hakan tare da ita muka tsaya muka gyaro ko ina tana fada min muddin yana gari kada in sake inyi wasa da saka kamshi ako ina a gidan.
Bata bar gidan ba saida nayi muna girki mukaci tare ga mahaifiyarsu nata kiranta a lokacin don kira yakai ukku tana fadin tana gidan har yanzu muna gab da kammala cin abincin ya shigo.
Ban dago kai nako kalleshi ba yana fadin wai ke har yanzu dama kina gidan nan tace to ina zani hafiz kana son kajawa mutane wani tashin hankali kuma inya kama in kwana a nan yau har kwana zanyi gidan nan ai.
Dariya ya kwashe dashi yana fadin zakiko hadu da daddy yau ajiku don yanzu nasan ya dawo gida by this hours bai kai dare a wajeshi ashe kasan da hakan kai ina kafito yanzu ?
Cikin gari mana ya fada yana zama kusa da ita yace naga mum da boy ai gidan hjy Binta na fito wurin salis acan nagasu zasu shiga islamiya,Ooh abokin tabaran ka ko ta fada tana hararansa.
Kajiki da shirme salis din ne abokin tabarana kawai sako naje in karbo a wajensa wai meyasa kuke zargin salis ne haka sosai lokacin na mike ina fadin.
Anty zanshiga ciki idan zaki tafi kiyi min magana na fada ina tattara kayan da mukaci abinci da ita a wajen ta dago ta dubeni tana fadin me kuma zakiyi a daki mu muna nan falo zaune ?
Akwai assignment din da nake son dubawa na mrs buhari data bamu gobe take son assignment din nata kuma shi zan duba na fada tace dani to sai nashigo kinsan mrs buhari kuwa kuna kuka da ita department din nan don yar kaifice ita.
Nasa kai na nufi cikin dakin ba tare dako juyowa ba zan shiga ke nan naji muryanshi yana fadin ba zaki ban abunci ba ke nan saina rokeki ko ?
Kunga irin abinda nakewa ke nan mutum ya shigo gida mace tayi maka kimkam kamar icce wai kuce dole sai na zauna da wanan gaskiya nidai ancuceni wallahi.
Ta bangarena tsaye nayi na kasa motsawa a wajen na kasa motsawa saboda banyi tsamanin zai bukaci girkina ba kodon yaji zanyi karatune yasa yake son making dina busy oho ?
Muryan antyne ke fadin jeki zubo masa ina dama kin aje masa ai dauko masa ki kawo masa na shige kitchen din na tsaya na hada kamar yadda muke hadawa daddy nasa abincin.
Da ace zaman lafiya mukeyi da ba wanda yaikaishi samun gata a waje don nidin training din mum ce banda matsala a wajen aiki don na iya komai na aikin gida tun ina gidan mu kuwa.
Na dauko abincin zuwa falo a gabansa na dire kayan abincin na juya na dauko ruwa na aje ina jira inji cin mutunci da diban albarkan da zaiyi min a lokacin har na gama na kwanta banji hargowansa ba ma,ana baiyi wani cin mutunci ba.
Anty tayi masa kur da ido tana kallonsa ko zaici abincin dayasa nakawo masa din ga mamakinta bayan tafiyana sai taga ya bude kulan abin ya kurawa tuwon semo din ido na dan lokaci.
Ko harda abincin nata ba zaka iya ci bane naga ka kurawa abincin idanu kamar mai tunane ya dago yana sauke ajiyan zuciya yace to ya na iya naga kun hada min kai akan yarinyar nan har daddy na batun yi min baki akanta.
Da murmushi ta sake tare da jin tausayin kanin nata ya kamata a lokacin hakan kuma ya kara tabbatar mata cewa ya fara saukowa daga abinda yakeji akansa kan auren.
Yunkurawa tayi daga inda take zaune zuwa kusa dashi da kyau ta zauna tana fuskantarshi tace hafiz ina son muyi magana dakai na fahinta kadai san banda kowa duniyan nan bayan ku don haka kamar yadda ba zaka yarda a cuceni ba nima hakan ba zan yarda a cutama ba kasani.
Hannu ya tsoma cikin ruwan dana aje mai don ya daureye hannun nasa ya soma daureyesu yace ina jinki ai ta kallesa lokacin da ya yanko abincin yana kaiwa bakinsa ta dan murmusa taci gaba da fadin.
Ka fada min meye BC damuwanka akan yarinyar nan ko kuma auren ne baka so ga baki daya ka kasa tsayawa kayiwa mutane bayanin komai har yanzu.
Don girman Allah ka fada min koma meye kada kace zaka boye min damuwan ka a yanzu don Allah kaga sai mu san meye mafita ga auren nan ?
Abincinsa yake ci hankali kwance ya mata bayanin daba zai iya tsayawa yaiwa kowa shiba bayan ita da Addil yanzu ko ko yasha giyar wake ba zai samu Addil da zancen nan ba ai.
Anty ta kura masa ido tana kallon yadda yake cin abincin kuma yana fadin zancen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login