Showing 84001 words to 87000 words out of 103712 words

Chapter 29 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7859

muna dacin hanci don a zauna dashi ko ?
Da yamma muna zaune ana hira gida ya cika saiga Dada ita ta saka min lale ta shammaceni banyi aune ba ta zuba min akafa har zuwa sawayena da hannayena tana guda.
Wani irin zabura nayi ina hawaye tare da furta ta faru ta kare ke nan na dai tabbata matar hafiz ke nan na fada a zuciyana na mike zuwa babdaki.
Kuka nayi sosai kafin nabawa kaina hakkuri na wanke nafito don kada mum ta gane cewa kuka naje nayi saboda nayi alkawarin ban sake yarda inyi kuka kuma kan auren.
Nan buki ya fara ga jama,a ko sai zuwa sukeyi daga garuruwa don su sheda kawai su nunawa iyayyena farin cikin ganin wanan lokacin kamar yadda yake a al,adance.
Kamar ko wani buki kuma ko wani gida aka hada bukin yayan daki biyu ake samun yan tsegumi da gulmace gulmace wanan ma namun hakan aka samu.
Hakan yafi faruwane kuma abangaren mummy din hakane ma a asirce mum taba da girki da za a dinga yo mata daga wani gida ana kawo mata nan gidan kawai saidai aga ana shigowa da manyan kuloli na abinci apart dinta.
Sai hakan kuma ya tsonewa mummy ido sai gasu har gaban Alh wai bata yarda da tsarin da mum ta dauko din ba nan daddy yake fadin baki yarda ba sai kije kiyi yadda tayi din mana kema.
Ni dai nasan Kubura bata tambayeni kudi wai zatayi girki ba haka kuma nima ban dauki kudi na taimaka mata tayi girkin nan ba ina duk abinda tayi tayine da sunan taimaka muna dai a cikin sha,anin nan .
Tunda dani dake keda bukin nan ba dole bane sai kubura tayi wani abin bajinta da har zai tsone maki ido idan kina da tunane mu tayi wa wanan karan ai a nan.
Duk da haka mummy bata fahinta ba don bata yarda ba kishi ya rufe mata idanu a lokacin sai cewa tayi dama ai bakinsu hadene gashi ita din dake cewa mum tana da rowa .
Itace irin halittan nan ne da komai sai sunci riba dashi kudin ba bata samu bane wajen miji bata dai iya fitarwa ne akashewa jama,a ta zata daddy zaicewa mum a hada a dinga kawowa ko wani part ga nata wautan.
Sai daren da za a daura aure hafiz din dasu yaya Addil daya shawo kansa suka iso garin cikin dare sosai bayan mum tayi ta korafin rashin zuwan nasu akan lokaci.
Tana cewa rashin zuwan matarsa da wuri yaci mata rai ace tana bukin kanwarsa amma ace wai ba matar Addil a wajen don tana yar rainin wayau.
Wanan yasa washegari da sukazo mum din taki tsayawa ta basu lokacinta tana nuna masu fushinta ga hakan da sukayi na basu kyauta mata ba son gaba su gyara.
Amma sai gashi itama Aishan wai tayi fushi don mum bata nuna tana da muhinmanci ba a wajen ta ga idon jama,a din haka ta sulale ta fice daga gidan ba tare da kowa ya sani ba.
Saida mum tace akirata tana kitchen shine ake fadin ai bata nan a zaton mun ta shiga wani part na gidan ne sai gashi ana fadin anga fita ai tabar gidan.
Ita kuma mum nata matsala ke nan daya fara bullo mata shine matar danta bata da mutunci balle kirki don sam bata da tarbiyan bin nagabanta uwar miji da take tankat uwarka ga me tunane amma ita ko gaban dan sai ta nemi ciwa nasa mutunci.
Don hakanema gaba daya gidan ba wani mai dogon shiri da ita baya ga gaisuwa da za a tsaya a danyi sama sama don gani take ta girmi wayewan kowa a gidan don haka babu sa,anta take daukankai
Sai dai ita a wajenta kuma gani takeyi kawai dai ba,a sontane don hakane bata nemi hanyan gyarawa ba sai iskanci da takeyiwa mutane tana kara bata kanta a zuciyan yan gidan mijin nata.
Don ko hakan datayi ba wanda baiji wanan labarin ba kowa na tir da halinta a cikin taron nace kinga bone kowa ya zageki Allah yasa mu gane gaskiya mu gyara ba sai ana son mu zamu kyautatawa uwar miji da yan uwan miji ba halinmu zai muna alkalanci a gid??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ajen auren mu mata.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[2/29, 06:30] Maman K: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

2?? 7??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.


Rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya to Allah ya gyara kamar kullum wanan uwar diyar batai kunya ba kamar yadda kow keyin abinsa cikin rufin asiri haka Allah ya rufa wanan asirin don an daura aure kamar yadda kowani aure aka saba daurashi lafiya an kuma samu jama,an da suka sheda hakan bila,adadin wajen taron.
Karfe hudu bayan daurin aure masu waliman da hjy mum ta kira sukazo suka cika unguwa da lasifika suka hau sharfi akan aure da biyayya ga iyayye suna kuma kwatance da irin kokarin daddy wajen tada zumunci da zamanin nan yake neman gagara a tsakanin yan uwa ko makwabta.
Anyi an watse lafiya an raba gifts wani mai hoton amare mu uku wani kuma hotona da ya hafiz ne a manne duk wanan kokarin mum ne datayi na aurar da yarta.
Sai washegari za,a tafi da mairo da Asiya garuruwan mazansu saini dake gari da za,a aje gaba da unguwarmuce za,a akai ranan.
Duk dako angon ya fada masu cewa komawa zaiyi washegari don matsa mashi da daddy yayine ya dauko pass yazo halartan bukin ba don wani abu ba can.
Duk da jin kalaminsa hakan baisa daddy ya girgiza ba ga abinda yayi niyar yi haka mahaifina ni dai sai ince tu ranan da yazo wajen mum sukayi magana ban kara ganinsa ba duk ko da kaini gidansu da mum tasa akayi ana gobe za a daura muna aure a can na wuni cikin yan uwana tare dasu.
Sai yamma akaje aka daukoni amma banga baba ba ko a idona haka mahaifiyata akwai damuwa sosai a fuskanta amma saboda kawaici irin nasu batace dani uffan ba har lokacin dana barsu din.
Ana gama walima muna zaune saiga Dada ta shigo part din mum tana fadin ina amaryan hafiz din ina jin hakan na bata rai take na hade fuskana .
Take fadin ki taso iyayyenki na jiranki waje iya abinda ta fada min ke nan dole na tashi nabi bayan ta bayan na nemo mum na fada mata.
Mukaje da Samira don tare muke sai dawowa samira tayi ita kadai tana fada masu cewa su daddy sun wuce dani ai sun tafi su kaini gidan mijina.
Nan take gida ya rude da mamaki mum kasa hakkuri tayi daidai motar su ya tsaya saiga kiranta tana tambaya hankali tashe da Alh wai kunje kai mama dakinta yace gamu har mun iso gidan ai ya kashe waya.
Su daddy Enugu suna gaba su biyu daddy kano yana rike dani har zuwa cikin gidan yana saman bakinshi da nema muna kariya daga sheda da sauran abin ki ga musulmi.
Gabana yayi wani irin faduwa a daidai lokacin da muryan hafiz ya daki kunnena ashe yana gidan yana sana,arshi kiran da daddy yayi mai yasashi tashi ya feshe gidan da air fresher gidan ya dauki kamshi lokaci guda.
Nasiha sukai muna sosai saidai na daddyn mu nasihan shi kamar wanka da jurwaye yayi muna don nasihace ta gugar zana garemu daga shi har ni kan zaman takewa.
Har kofa ya rakasu bai dawo ba saida yaga motarsu ya daga daga wajen ya juyo zuwa ciki ina nan rakube a inda daddy ya barni zaune sai tsukinshi naji hakan ya sanar dani shigowanshi daga rakiyan da yai masu din.
Banza ukuba yanzu kika shigesa duk wanan barnan miyau bakin da daddy keyi akanki zai kare bani ba don ki sani daga yau kin shiga tashin hankalin rayuwa ke nan a rayuwanki zakice nace.
Tunda har kukai sanadin mai dani bazawari bazanyi ni kadai ba koda ace maza suna zawarci saidai muyishi tare dake saina bar maki mugun tabon da gobe ko ance maku ga kwadayi dake da iyayyen ki makwadaita zakuce yana wari.
Ke dasu sai kunce,,,,,,
Knocking din kofan gidan da akeyi ya hanashi karasa abinda zai fada yaja wani ubab tsuki yana fadin kawai kawai mutum yana zaman zamansa a dauko masa masifa a sarkafa mashi a habasa shakat da rayuwansa wanan wani irin masifane wai a hana mutum hutawahasale.
Yana bude kofan a hasale anty Nafisace ke fadin dama nasan kana ciki tunda naga ba,a bude da wuri ba ko har ka fara shan angoncinne kai ni basu Dada waje su shigo don Allah ka wani rdakin kofa kamar baka son mu shigo yan kawo amaryane sukazo.
Ido ya waro waje yana fadin wace amaryan ke nan kuma ya tambaya cikin mamaki.
Dada tace naka mana ko an kawo maka itace dama tana zolayanshi ido ya waro waje yana kallon kofan dakin daya barni a zaune cikin razana .
Gudan da yajine ya kara firgitashi yana fadin wai da gaske Nafisa ita wacan na zaune a dakin fa ita din wacece Dada ta amsa data karfece wanan kuma amaryan danko muka kawo maka yana bin samira dake rufe da kallon mamaki.
Kaje dakinka don Allah kada mata su sameka wajen nan su dauka koka fara bita zauzaune tun yanzu nafisa ta rada masa a kunnensa.
Wani haushi da takaici ya kara rufesa wajen wai ana nufin mata biyu daddy ya aura masa lokaci guda koko dayan daya saninece data zamo mashi alkakai a yanzu ?
Nan yaji tururuwan jama,a suna shigowa da guda da ihu abinda yayi hating duk mata sun ruda gidan ga koke koken yaransu yana tashi duk da ya rufe dakin amma yana iya jiyo muryansu a nan din.
Sai bayan wani lokaci ya daina jin muryoyinsu tare da jin tashin motocinsu suna barin gidan duk da hakan bai fito ba sai sha daya da wani abu yazo ya rufe gidan ga baki daya yana jan tsoki.
Yar gatan amarya yar lele itace angonne ke zuwa sayen bakinta don nikan bayan wucewan yan uwa mikewa nayi na nufi kofa na saka key na dawo na rage kayan jikina na shiga bandakin na dan watsa ruwa tare da dauro alwala.
Na dade zaune ina addua kafin na mike na hau gadon saboda zuwa lokacin zuciyana ya dake ya bushe ina jin kaina kamar bani bace kamar ban iya kai safe lokacin.
Allah da ikonsa ina gama addua na kwanta bansan lokacin da barci ya daukeni ba sai falkowa nayi na ganni kwance cikin hasake sai kuma lokacin na tuna da inda nake kwance din.
Zabura nayi ina salati nakai duba ga kofa na tuna nayi masa key kafin in kwanta na samu na mike da kyar na koma bandakin na sake dauro alwala nazo na sake tayar da sallah.
Hannu sama ina kuka nake rokon Allah daya hausheni kan duk wani mugun nufin da hafiz kedashi a kaina na zama matanshi danayi yanzu din.
In nayi adda in tsaya inyi kuka in kara kuma daga hannu ina rokon Allah in kuma koma tunanen duniya a haka wani barcin yayi gaba dani ba tare dana sani har gari ya waye sosai kafin na zabura na mike ina sallati na sake shigewa bandakin na dauro alwala.
Haka na koma kamar zautata a ranan ni kadai a daki gashi ba motsinkowa a gidan koshi azzalumin banji motsinsa ba na kuma kasa bude dakina ina jin tsoro don bansan da wace zaizo min ba lokacin kuma .
Ga ba waya a hannuna wayata na dakin mum saman akwati na aje lokacin da zan saka abayan zuwa wajen walima tun lokacin ban kara bita kanta ba wayan samirace a hannuna kuma karama ita nake ta jagula tunda nazo.
Sai wajajen karfe daya naji anata dukan kofa hakan yasa na daure na bude wata gwaggon mune yar mum ce ita take fadin tun dazun ake zuwa ana fadin kofa a rufe.
Uwarki nacan ta rude dole ta taso damu muzo mu dubaki ko wani abune ya sameki gashi yanzun muke jin wai mijin naki ya koma tunda safe inda yake aikinsa.
Wani dadi naji duk da ban cikin yanayi mai dadi a lokacin amma jin hakan yasa zuciyana sanyi lokaci guda nace Allah sarki mum nasan ta damu sosai ga wayana na barshi a dakinta tun jiya din.
Gwaggo Rahinatu tace ai mun gani tun jiyan ta dauka ta boye maki shine ga abinci can a falo tace zuwa yamma zata lekoki ta ganki ai yanzu ma munzo duba ko lafiyane anata zuwa kofanki yana rufe.
Basu tsaya suke fada min ai an wuce da amare tun safe yanzu ai kila sunkai don gobe zasu dawo masu kai amaren nikan duk sama sama nake jinsu.
Saida suka wuce naga abincin ganin kayan abincin yasa nagane daga hjy mum suka fito ba part din mummy da yanzu ita keda alhakin ban abunci don ina karkashin danta da zama yanzu.
Sai lokacin na samu daga kai na kalli tsarin gidan gidane mai kyau nagani na fada don ba inda wanan gidan yake da maraina gaskiya a wajena nikan.
Abincin na bude na dan tsankwara nace bakina ba dadi don haka banci wani abin kirki ba na aje cokalin na zauna nan ina tubane hakan yafi mun na fada a raina.
Da zaman dan cin mutuncin da baisan daraja iyayyenmu ai gara yayi gaba hankalina yafi kwanciya da hakan da zamansa don bansan iya abinda zai iya min ba idan yana nan.
Allahne ya karbi addua na dana kwanayi a dakin ya iza min shi gaba na fada a zuciya shigowan su Samira ya kara dauke min hankali nan suke min hiran abubuwan daya faru bayan bari na gida din.
A bakinsu nake jin wai yace next week zai dawo ba dadewa zaiyi ba dama bai samu hutu ba yadai zone kawai ayi buki dashi ya koma.
Ni dai ban tsuka ba shigowan su mum dina ya dauke min hankali saidai mum din a yarda na ganta ranan duk ta zabge tarame kamar wace tayi ciwo a dare daya.
Abubuwa sin ma rayuwanta yawa don bata saba hakan ba sai gashi da zaizo mata yazo mata da tashin hankali kowa najin abinda ke damunsa har daddy uban gaiyan.
Sunyi min nasiha sosai wanda duk cikin nasihan hakkuri da biyayyan aure shine kan gaba duk wani kalami na kowa da zai fada shine inyi hakkuri wata rana sai labari insha Allahu.
Ta ban wayana tare da fadin duk da nasan baki da kawayen banza amma zan kara ja maki kunne don Allah ki kula akwai hakkin aure akanki yanzu mamana kada ki yarda ki canza rayuwan ki nan gaba don Allah.
Da kuka muka rabu yan uwa suna bata hakkuri take fada min su samira zasu kwana tare dani in Dada ta dawo kai amarya daga bauchi zatazo ta zauna dani a gidan.
Muka rabu cikin rashin dadin rai ranan tare dasu samira muka kwana wanda tun karfe takwas da wani abu na kwanta barci saboda barcin gajiya dake idona.
Washegari bamu jira an kawo muna breakfast daga gida ba mu muka girka abinda mukeso tunda akwai komai da aka kawo min nagara na dauka ya Addil zasu ratso kafin su tafi .
Sai gashi samira na fada min ai sun wuce tun safe yazo ya sallami mum cewa yana da aiki zai koma a raina nace kowani al,lazi da nasa amanun shi kuma yaya matarsace nasa matsalan rayuwan.
Don nasan itace zata matsa mashi su koma a ranan bawai son ransa bane zaisa ya koma dama shi ya Nasir bai samu zuwa ba yana wajen course din aikin daya samu na world bank.
Ranan ma dasu Samira din muka wuni muka kwana gashi washegri zasuyi sammako su koma don su Dada sai dare sosai suka dawo kuma bata da lafiya koda suka iso.
Haka washegari tunda safe aka turo su samira suka fit suka barni ni kadai a gidan kamar manya sai gidan ya dan fara ban tsoro ganin ni kadaice a ciki.
Sai maigadi dake can ta wajen gidan yana aikin gadinsa ba ruwana dashi kuma haka na kwana don mum data kirani tana sheda min Dada jiki yaki har ssibiti aka kaita da sunyi shawara a turo min halimatu ko ya nagani nace su barta zan iya kwana ai saboda karfin hali.
Tun daga wanan rana na kama kwana ni daya a gidan tsoron haka kuma ya fice min a raina zansha barcina da safe tunda muna hutun boko a lokacin.
Saina gaji zan tashi indanyi abinda zanci daga nan kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login