Showing 75001 words to 78000 words out of 103712 words

Chapter 26 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7850

asirce daddy don a manna masani suci arzikin Dad din na karasa ina wani irin kuka hannu ta dora akai tana fadin nashiga uku ashe hafiz katon wawane ban sani ba.
Baba Garba din zai kullawa wanan sherin mutumin da kowa yasan irin kauna da amincin dake tsakaninsu da daddy zai tsaya kan shirme yana masa wanan sherin haka ?
Au kema kinji ko kinji abinda Hafiz ya aikata ke nan duk da kema naga laifinki ai tunda kinsan basu shiri me saisa ki kirasa masa ita don Allah.
Wallahi hjy mum na zata alheri ya kawosa wurinta bansan dan iska sheri yazo yayi ba na dauka abin arziki ne wanan babban maganan daga ina yafito masa haka kuma ?
Atoh kila abinda yaji ana fada ke nan shima ya fadi in bashi ba yaya Garba sa,ansane da zai jefa masa wanan kalamin kamar ubansu daya fa da Alh.
Duk da ran anty Nafisa din ya baci da kalaman mum amma haka ta daure tana bada hakkuri ga mum din wai kada zancen yakai ga daddy don laifinta Dad zai gani.
Tace nafisa ke nan wanan abin kema kinsan ba abin a kyale bane tunda har yakai ga dora hannunsa akanta tun yanzu ga kuma cin zarafi ai dole aiwa zancen tufka tun yanzu.
Ni har naje na fadawa hjy tun dazun ai don tayiwa Alh magana idan ya dawo don dole dai su sani wanan abin gara abarshi tun rayuka baikai ga baci ba gaskiya.
Ayi abu don zumunci ya kara a tsakani azo kuma ana da ansani a tsakani ai kinga gara a bari haka zaifiwa kowa sauki tun yanzu.
Kai hjy mum kema kinyi saurin fadawa Dada ai da ki bari in dawo mu samu dan iska muyi masa tas amma duk da hakan bai baci ba ai don zaifi gaskiya a tsawata masa doni dan iska ya tashi jawa magana ai a wajen aiki.
Da hukumar makaranta sun sani wallahi wanan abin zai iyasa su bani quiry ko kuma su koreni ma don hakan dokane a garemu mai tsanani.
Ta kalloni tana fadin kiyi hakkuri don Allah zeey in Allah yaso za,a tsawata masa ya daina ta daga tana fadin bari naje mum kada suga na dade ban dawo ba azata har yanzu ina can.
Daddy kan jin abin yayi kamar al,amara ya dade zaune shiru bai iya magana ba sai bayan tsawon wani lokaci yace me yaron nan yake nufi ne wai ?
Ke nan ya nuna ni ban isa dashi ba ke nan da zance dashi ga abinda nake so har ya tsaya yana jayayya akai haka shike nan yaje ga duniyan nan ai fadi gareta tunda yana da wani uban dayafini.
Yaro in maka gata in hadaka da yarinya ta kwarai kace min ba haka ba shike nan tunda ban isa dashi ba ai koda yake nafi ganin laifin Nafisa ai a zancen nan.
A,a Alh kada kaga laifin nafisa don Allah ita meye nata a cikin zancen nan don Allah na tabbatar Nafisa dai ba zata turashi yaje yayi abin nan da yayi ba maganar gaskiya.
In kasan halin mutum ko bayansa ka fadi gaskiya akansa babu ruwanta cikin zancen nan yaje da sunan hirane yayi hakan ita kuma tayi fada sosai ga yadda yayi din .
Ai gashi ga duniya tun haka uafi masa din aurene dai ba fashi nayi niya sai anyusa kuma ko zai mutune ranan daddy din ya fada rai bace.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[2/26, 07:16] Maman K: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

2?? 5??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,

Rayuwan haka yake tafiyawa bawa da kalubali iri iri wani tun yana karami zai fara fuskantar kalubalin rayuwa wani ko sai ya zama magidancin kansa zai fara karo da hakan.
Nikan kusan sai ince tun ina karama din na fara fuskantar hakan na baro kauye cikin kunci da matsi mun dawo katsina wanda zuwa kano ya zamo min babban kaddaran rayuwa a yanzu.
Don ko yanzu na fahinci shirin buki haikan hjy mum dina keyi don ko duk wani abu daya kamata ace uwa ta tanada nakai yarta aure da zatayi amfani dashi gidan miji hjy mum tana tanadar min shi daidai gwargwadon halinta zakice itace ta haifeni da cikinta abinda take min.
Duk da zaman namu Allah baiyishi da dogon tsayi ba amma haka bai hana taimin komai na sakayya a gareni ba takance nidin yartace ta cikinta don ko dan uwanta ya haifa matani.
Nidai ina kallonta don duk gayyan kayan nan basu burgeni kosu ban sha,awa kawai dai ido na saka zuciya tab da tunanen me zaije ya dawo min.
Karatuna kawai nasawa gaba wanda hakan ke dan sake min zuciya duk da banda kawa da zan nuna ince ga aminiyata yau acikin kano.
Bawai kuma ban samu bane a,a bandai ba hakan muhinmanci bane a rayuwata don akwai mutum uku da mukai karatu tare a secondary da yanzu course din mu daya don suma pepper su yayi kyau sosai an kaisu uni.
Dan dama su wani lokaci zaki ganmu tare muna hira ko muna dan tatauna abinda ya shafi karatun mu na yanzun don sanin da sukai min mai fasaha tun a secondary a sanadinsu sunana ya fara dan dagawa a class din.
Gashi har Saturday nakan shiga school around twelve mu dawo four na yamma don hakane na zama busy sosai a wanyanzun din ban kuma fadawa kowa zancen aurena ba.
Wani lokacin nikanyi mamakin rashin fara karatun su Mairo amma nakan bar zancen da cewa watakila dai don result din su baiyi kyau bane daddy din yaki kaisu ko kuma ni na samu daurin gindine a wajen dan uwana daya tsaya min har yaga na samu na fara karatun a yanzu kar a tauye min rayuwa gaba daya.
Ranan na dawo school din rana na samu part din mu cike da matan gidan ina shigowa da sallamana Anty Nafisa dake duke ta baza zannuwa tana kallo ta dago tana kwala guda tare da fadin kunga amare fa.
Yan gatan daddy aini wallahi daddy ya nuna min banbanci irin wanan lefe haka gaskiya yaran nan kun taki sa,an daddy ba kadan ba gabana yayi wani irin mumunan faduwa lokaci guda na dan daga kai na kalli kayan sau daya na shige daki.
Zaune nakai don gaba daya wani irin duhu nake gani lokaci guda saida mm a dade zaune a wajen kafin na rage jin muryoyinsu a falon da alaman sun fita kenan part din.
Hakan yasa na daure na mike lokaci guda na fara rage kayan jikina motsin mutum ya shigone yasa na dan juyo inga maishi Antu ce dai still ta shigo dakin nawa.
Haba sis kayan lefe ba abin wasa bane balle ku da daddy ya kashewa wa yan nan makudan kudin wajen hada wanan lefen komai iri daya daddy ya saka maku saidai ya banbanta kala don kowa da kalan nasa haka kuma,,,,,
Sai naji tayi shiru don fahintar da tayi ba ita nake sauraroba a lokacin tace gaskiya banso ki da haka ba zeey zaki biyewa Hafiz ne ku sabawa daddy ga baki daya ku ?
Bayan duk kokarin nan da daddy keyi akanki kada ki bari shedan ya rudeki har a gane hakan akanki bayan kowa na yabon yadda kikayi biyayya ga iyayyen mu din yanzu kuma ki bata rawanki da tsale.
Gaskiya kada ki yarda wanan labarin ya kai ga daddy din yadda yake fama yaba hankalinki a wajen kowa ko mairo fa Auwal yazo daga bauchi sun shirya yanzu duk ta rage wanan iskancin data dauko yi kinsan guy din hadadene ga kuma ilimi.
Asiya daice da take bin zancen mummy wai ba zata katsina ta zauna ba har yanzu nake dan ganin kanta yana hayaki itama dai din ta rage ba kamar farko ba don na zauna dasu nayi masu nasiha sosai.
Kuma na lurar dasu gatane fa daddy yayi maku zeey ke mace ce zeey duk wani iskancin Hafiz na dan lokacin nan ne kina shiga gidan na tabbatar da zaku shiya dashi.
Abu dayane zuwa biyu shine nasan Hafiz dan karyane na gasken gaske don haka sai kin zage sosai kin koyi kwaliya girki don kamar Addil yake shima su biyu keda rayuwan tsada da jin kyama a gidan nan bako ina suke shiga ba ba kuma ko wani abinci suke ci ba haka kasafai.
Kinga nan ma sai kin kula haka kuma nasan hafiz da son jiki da son jan girma kuma kamar yadda kika sani kowa kuma yasani kinga ke nan a nan sai kin hada da hakkuri.
Hakkuri kuma bana wasa ba don nasan kinsan komai basai na fada maki hafiz yana shaye shaye ba duk da mummy tana ganin ba wanda ya sani a gidan nan nasan kin sani a ranan da mummy ta aikeki kai masa abinci part dinsu kuma munyi zancen dashi.
Don haka kinga nan ma akwai matsala na zauna nayi tunane da hikima daddy yayi wanan hadin naku keda shi zeey don ke din ta gidace zaki iya rufawa dan uwanki asiri ba kamar wata bare ba ta waje da zata iya tona mashi asiri ga abinda yakeyi din.
Zuwa lokacin na kasa boye hawayen da nake faman riko a idona kuka sosai nakeyi a dakin naji ta dafani tana fadin wallahi zeey da hikima sosai cikin wanan auren Daddy bai hadaku ba saida yayi nazarin hakan ya hada kowa da daidai da ita.
Kada kiyiwa daddy mumunan zato a wanan hadin naku kice ya manna masa dansa dangiya alhalin su yayansa ya zaba masu masu kirki .
Ba haka abin yake ba zeey wallahi na fahinci daddy a yanzu duk wanan hadin da daddy yayi yayisane akan hikima da basira ko wanen ku ya hadashi da wanda yasan zai gyara rayuwansa amma ba kowa zai fahinci hakan ba sai nan gaba.
Idan kun daure gaba dayan ku zakuji dadin auren nan naku jin meta fada yasa na dago kai na kalleta tace Yes iam telling you zakice na fada wata rana insha Allahu.
Hannunta ta dauka ta dagwara a nawa tace ki jajirce sosai zeey ki zamo jaruma a gidanki zainab ki mayar da mijinki abin alfaharinki abin kuma so ga kowa daya gansa.
Kuka sosai nake har ban iya gane mum na dakin ba saida naji tace kukan na meye haka don kawai kijawa kanki ciwo duk abinda Nafisa ta fada gaskiya ta fada maki.
Don ba karya acijin zancenta nima abinda na hango Alh yayi ke nan kikaga ina faman baki hakkuri da kike dauka duk bamu son kine wanan shine gata da kaunan da zamu iya nuna maki ai mama.
Itama mum dafani tayi acikin sanyin jiki tace mama kiyi hakkuri ki daina kukan nan don Allah ki yarda da hukuncin da Allah ya kaddara a gareki.
Ki yawaita kiran Allah ya sasauta maki abinda kikeji a zuciyarki insha Allahu abin zaizo maki da sauki ta hanyar da baki tsamani ba da yardan ubangiji.
Tana kaiwa nan ta juya ta fita zuciya ba dadi agareta ta barni da Anty Nafisa din dake fadin haba sis ki kwantar da hankalinki mana ki dauki shawaran da muke baki nasan kowaye hafiz idan kikabi sharan mu zakiyi maganinsa hafiz zai dawo a hannunkine wallahi.
Haka kuma sai kin daure da mummy don rayuwan Hafiz gaba daya bisa tsarin mummy yake don hafiz ko wanka yayi saiya kira mummy wani lokaci yana tambayanta kayan da zai sauya saboda sagarta data koya mai wai so.
Don haka ki dauri kibi shawaran nan namu insha Allahu zakice nace dake ni zan koma don in gyara wancan kayan nasu mairo dake part din mu don nasan mummy ba zata tabasu ba idan bani naje na kawar ba a yanzu don Allah ki natsu kamar yadda hjy mum ta fada maki.
Daga haka kuma tafice daga dakin ta barni a wajen saida na dan dauki lokaci kafin in mike nashiga bandaki na fito don la,asar ya shigr ko ana batun magariba ba daman ayi nafila a lokacin yasa na wanko fuskana na fito abinci na sama mum ta kawo min har daki na zauna naci kadan don kada tace banci ba na kwashi kayan zuwa kitchen.
A dakin kwananta ta jera akwatinan auren nawa da daddy ya gabatar masu a matsayin lefen mu wai ashe duk da fitinan mummy bayan Dad ya kirasu saida ta saka matar daddy enugu ta bude ko wani tagani ta kana tace a musaya a dauki wanda daddy yace shine nawa shi kuma ya fito yace bata isa ba kowa da sunansa yasaya mai ya kuma saka komai iri daya aciki don yasan kalan da kowan mu ke so ai.
Nan kuma ta kwashi fushi ta hau bakinta daddy din yace idan son kai nayi kece dai naiwa son kai din don matar dankice na cikinki zata daura kayan don haka ake nayiwa son kai din ke nan .
Wani kallo tayiwa daddy kafin tace matar danka dai amma ba dana ba in gaskiyane ita mama din abin kwaraice ka hadata da Nasir ko Addil mana amma ba jini naba.
Tunda kasan ko a rarihi ba aure tsakanin zauren gidan mu da nasu ke nan ashe ba aure a tsakanina dake ko ?
Tunda hakane tayi shiru ta juya ta bar wurin rai bace yace sakaran banza zan koya maki hankali a gidan nan tunda ke kulun yarinya kike zama baki girma kafin ki tauna zance.
Dada da abin duniya ya dama a lokacin kallon hanyar da hjy malkan tabi tayi tana dadin wai ko anya kan marka daya kuwa kodai marka ta tabune ba,asani ba ?
Lafiyanta kalau tsaban iskancine da rashin sanin ciwon kai data iya take nunawa wanda bai gama sanin halinta ba a yanzu wai ita marahankali.
Bayan kamar kwana biyar ya Addil ya shigo garin sai washegarin asabar ya shigo gidan muna zaune falo don ranan ba zamuje karatu ba kowa na gida saboda dan tafiyan da mai course din yayi muka huta gida a ranan.
Yana saye a cikin wani yadi fari daya kara masa kyau sai wata yar hulan maza dagani mai tsadane mai kalan dan ruwan toka akansa duk da akwai rama a jikinsa hakan bai hanashi yin kwarjini ba a idanuwan mutane.
Part din Dada ya fara shiga dana daddy Enugu ya gaidasu suna tambayarshi matarshi Aisha duk da tare suka shigo kanon amma saiya saya yace tana lafiya kawai ba ambata tare suke ba don gudun korafi a wajensu.
Ya gama dasu har part din mummy kafin yashigo nasu part din ya samemu zaune da mum din a falo muna kallo mum kuma na waya da mai kayan kamshi da tayi Oder a kawo mata wata yar maiduguri.
Lah ya Addil ashe kazone na fada cikin yar fara,ata ina kokarin dagawa inda nake zaune yace amarya gaki duk kin rame mana ko duk rakin auren ne haka kika fada tun yanzu ?
Fuska na dan bata tare da fadin haba dai ya Addil har dakai kuma kaine fa share hawayena kullun inawa ya Nasir gorin hakan don yaji haushi .
Zance kuma a gaskiya karo na farko ke nan duk zamana gidan da wani kalman wasa ko zolaya ya taba shiga tsakanina da yaya din don baya magana balle inga fuskan tsayawa wani wasa dashi can yadda mukeyi da ya Nasi da sai mum ta koresa wani lokaci .
Mun din ta gama wayan ta dago tana fadin ashe kun samu shigowa yace ehh aina fada maki zanzo kafin buki na ganku ya sauko saman kujeran ya tsuguna yana gaida ita a cikin ladabi ta karba masa ni dai hakan na ban sha,awa wallahi.
Ruwa da abinsha na karaso masa dashi har na dire a gabansa yace nagode mum yarki ta rame da yawa wallahi ko tayi ciwone wai don raman nan yayi mata yawa gaskiya.
Aiba ita daya ta rame ba har kai don haka ashe aure ramar da mutane yakeyi ke nan ba kiba ba kana zancen mama kai kaga yadda ka rame din kuwa ?
Halan ko abinci bata baka balle wajen kwana kai ya kamata aiwa wanan tambayan a yanzu ba mama da har yanzu tana dakin uwarta bako .
Meke sakaka wanan rama haka har ya ja maka dushewa hasken ka ya dushe sosai a yanzu mai sunan malam ta kirasa da sunan da akasarin yan family suke kirashi dashi din don sunan kakansa malam Ali da yaci .
Dan shafo kai yayi zuwa fuska yana murmushi yace mum don daidai kin dade baki gani bane kike ganin na rame amma ai jikina nan da haskena kuwa.
Allah yaya ka rame ka fada sosai kayi baki ka rage tsayina ya dago ya harareni nayi saurin nokewa a bayan mum yace kika karajin ana min magana kin sani ai zan fasa shegen bakin nan naki a wajan nan.
Ba zaka dukar min diya ba son gaskiya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login