Showing 33001 words to 36000 words out of 103712 words

Chapter 12 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7862

mum din suna min ya jiki.
Don haka a dan wanan karnin tayi iya kokarinta kamar yadda mijinta ya umurci kowa da baison yaji ko ya gani a garesu kaina don hakane ashe suke kokarin nuna min kulawansu akaina lokacin.
Yayin da hjy mum ce da Dada suka zamo sanyin idanuwana a gidan saboda natsuwan da nake samu a wajen mum din tare da kulawa irin wanda mahaifiya zata ba yarta.
Don mum ko fita zatayi tare danine saidai idan ni naki fita amma kafanta kafana duk inda zata shiga islamiyan da take zuwa nan nima ta sakamu nida halima bata yarda ta kaimu wanda yaran gidan kezuwa jefi jefi ba sai sunga dama.
Cikin hakan zance Alhamdullahi don yanzu gaba daya na manta da zancen gida don nasan ba komawa a gareni na kuma ba kaina shawara gara na hakkura da ida Allah ya ajeni din inyi biyayya kamar yadda suke so a zauna lafiya.
Sati biyu da yin hakan daddy ya kaimu wata makarantar kudi don ba karamin fiti akayi da hjy malka ba data nuna bata son akaimu inda yaranta suke tunda tagane gasa hjy mum keson yi da ita wai yasa ta matsa mu dawo garin da zama .
Wanan yasa mum taba daddy shawara ya kaimu wani school shima na kudi don nasu baifi namu din ba duk bamu san anyi ba sai murnan hakan mukeyi mukan tunda ba abinda ya damemu sai kewan gida wanda yanzu mun rageshi koshi tunda ga Dada a tare damu.
Da mun dawo daga boko zancen islamiya ne don haka ko aikin gida yanzu bako yaushe muke yinsa ba sai weekend da muke gida zamu dan kamawa hjy mum din aikin gida din muyi.
Ga kuma kulawa ta musan man daga daddy da muke samu don zai kiramu har yayansa biyu da dai sun dan girmemuna ga shekaru yaji korafin mu zai zabi na zaba dake da muhinmanci yayi muna nikan kullun aka tambayeni zance hjy mum ta saya min ban karban kudin daddy din amma daya gane hakan halinane saiya ban kudin yace saiki kaiwa mum din naki ta kara tayi maki yar gidan mum.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[1/31, 08:06] Aishatu Aliyu Musa=??>?p?: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

1?? 2??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Shi baiwa ko daukaka wani abune dake zuwa daga Allah halittan bawane da aka haifeshi dashi hakan saidai mu yan adam bamu gane hakan.
Na fadi hakan ne duba ga yadda na koma cikin dan lokaci kadan dubaga yadda na saki komai na rugumi kaddara sai gashi cikin dan lokaci kadan rayuwata ta canza ga baki daya.
Zakice ni din ma haihuwa binnine ban taba zama kauye da muka baro nida iyayyena ba da farko to ba komai araina sai zalla kwakwan karatu both bokon dana mahamadiya dana sa a raina.
Bazance ban tunanen iyayyena ba wanan yana min makale a zuciyata dare da rana ina cikin kewansu koda yaushe suna a zuciyana saidai ban nuna damuwa akan hakan.
Wanda hakan yasa aka fita zancen nakoma ina bawa kowa mamaki daga karshema aka daina damuwa akan hakan dani tunda anga na sake a gidan.
Saboda hjy Malka yasa bana shiga part dinta don bata iya boye bakin cikinta akaina don ma tafi matsa min saboda ban bada kafa irin na Halimatu ba da har zasu dan bugi cikina suji halin da hjy mum ke ciki kan wani abinta.
Nima daga baya nagane cewa halimatu din nawa hjy mum din mu zagon kasa tana fadin zancen ta yana fita daga bakinta don da farko hannuka mai sanda mum kanyi muna takance amma kuke wurina bani kaunan abinda zai taba rayuwan ku.
Na dauka irin rikon da nake maku kuma zaku rikeni har zuciyar ku ba tare da munafuntata ba idan tayi wanan maganan nakan tsargu da ita nakanyi mamaki don me take yawan fada muna hakane.
Da hankali ya danzo min ya karu saina fahinci ida matsalan yake watau dai halimatuce ashe shakuwansu dasu mairo diyan hjy malka da biyu sukeyinsa don wani lokaci zaka sanesu a part din zaune ana yan dararaku a tsakaninsu.
Bankan tsaya kulasu zan shige wajen Dada mu dan jima muna hira wanda bai wuce hiran takuran da take ciki ba a nan din dkgidan rashin fita yadda takeyi a gida yanzun kuma bata samu sai abin yake damun ta sosai yanzu.
Yau ya kasance asabar don haka nakan dan zauna na wanke kayana tunda safe na hada hardana hjy Mum din idan sun bushe saina goge nakai mata daki yanzun ma haka nayi.
Nashiga da salamana tana zaune a bakin gado tayi tagumi da hannayenta biyu yadda ta amsa tun nan nagane a cikin damuwa take lokacin.
Kafin matace na bude durowa na saka na nufi wajen kai tsaye na bude na jera kayan har nagama zan fita batace dani komai ba hakan yasa na dan koma satan kallonta don na kara tabbatar da zargin da zuciyana ke mata.
Sam bani take kallo ba asalima a yanzu hawayene ke sauka a idanunta hakan yasa naja na tsaya cikin dan rudewa da nuna damuwa agareta.
Nake fadin Mum lafiya kuwa naganki hakan lokacin ta dago kai tana fadin ba komai mama jeki abinki kawai ganin hawaye a fuskan nata lokacin da take maganan yasa na tsaya a hankali na taka zuwa gareta ina fadin.
Mum ko mun maki laifine bamu sani ba na duka gabanta ina fadin hakan sai naji ta dan sauke ajiyan zuciya tace inma an min laifin bani tunanen dake ciki mama.
Nafi kyautata zaton halimace don a yanzu nasan halinku kaf nasan abinda kowan ku zai iya da wanda mutum ba zai iya yi ba a kullun burinki a zaman mu shine kiga farin cikina mama a gidan nan ni shedan hakanne akanki amma halimatu tana yarda ana hada kaida ita wajen cuta min ma,ana dai tana munafuntana a yanzu.
Don kusan ince banda siri a sashen nan da zanyi Halima bataje ta fadawa su hjy malka ba don na tabbatar bake bace ke fadin wanan.
Innalillahi amma halimatu bata da kirki ashe sakariyace haka ban sani ba har wani dadi taji a wajensu da taje tana sakin maganan mu a can ?
Rashin wayaune don sun fita dubara ashe har kayana take dauka ban sani ba take kai masu sugani amma Mum ba za,a kyaleta ba gaskiya na fada ina kallonta.
Kaita girgiza min tana fadin bazanso nayi sanadin zaman ta gidan nan ba insha Allahu halinta dai zai baiyanata illa iyaka yanzu tunda mun ganeta saidai mu dauki mataki a kanta ki kara kula sosai ga duk wani motsi nata a gidan nan.
Na amsa da to bata fada min me halimatu din tayi mata ba a lokacin nima kuma ban tambayeta ba na fice a dakin ina mamaki hali irin na halimatu din na munafunci.
Tun wanan abin ban kara yarda da halimatu ba dama ba wani lakkane da ita ba ko kan ta tashi nayi duk wani aikin da zanyi na taimakawa Mum din kafin mu tafi school.
Hakan ko a jikin halimatu din sai Dada ce bama tayi magana ganin rashin jittuwan mu a tare yanzu ba kamar da can ba da komai a tare mukeyinsa .
Yanzu har yakai ta daina kwana part din Mum din ta koma can wajen su mairo tana kwana dasu haka kuma tana jidan yan kayanta tana mayarwa can.
Sai a karshe ta dainama shigowa wurin hjy mum din gaba daya abu dayane shine tare muke zuwa makaranta da ita wanan kan munayi har yanzu don ba yadda za,ayi mota daya muke shiga dukkan mu mu hudu a fara saukesu sai a kaimu namu school din wanan dokana daga wajen daddy.
Ranan da yamma daddy ya shigo part din Mum a falo ya sameta zaune tana kallon wani shiri na girke girke jin sallamansa ta dago tana fadin Alh an dawo ?
Yace na dawo yana kaiwa zaune yake fadin hakan ta gaisashi da yamma ya dan amsa a gajiye kafin ya fara raba ido yana fadin a,a ya banga yaranki ba ?
Yace wai su mamana yace su mana don ya saba tambaya idan ya shigo tace yanzun nan ta daga zuwa kitchen wai yau tuwon take muna sai gani na fado falon ina tambayanta kayan yaji.
Ganin daddy din yasa naja nayi turus tare da dan gaidashi cikin daburcewa daganinsa din ya amsa min cikin irin fara,an nan nasa yana tambayana karatu.
Kafin yace ina yar uwar takine saina kalli mum din tace wai halima yau ne ta koma part din hjy malka ai can take zama yanzu daga ni sai mama a nan.
Yaushe akai haka ya tambaya cikin son jin ba,asin dalilin komawarta can din mum tace can din taga yafi mata sauki ai da nan da can duk dayane.
Dole dai nasan akwai wani abinda ya faru har tabar nan din amma aini wajenki na barta donke nabawa amnansu tun farko .
Murmushi Mum tayi kafin tace can din yafi mata dadi tunda kaga ta koma can da zama kabarta kawai nima hakan yafi min sauki data zauna nan hankalinta ya kasu gida biyu.
To shike nan amma zanyi binkice in gano inda matsalan ya fara don banson mutum mai baki biyu Mum tace Allah ya bada sa,a ya mike ya fice bai sake wani magana ba kuma.
Lokacin Mum din ke fadin ai gara ka bincika din kaji koka gane gaskiya ba zan taba zama da ita ba kuma tunda ta zama munafuka mai baki biyu karamar yarinya da ita har tasan tayi munafunci irin haka inaga ta kara girma kuma.
Nikan aina gama zama da wanan yarinyar a rayuwata.
Tsam na juya zuwa kitchen da tausayin gwaggon namu a raina nina fara fadawa Dada abinda halimatu din tayi tace haba naso gane hakan amma koni nan sai ayi sati saidai inji muryan halimatu a sashen nan amma badai ta shigo inda nake ba .
Bakomai bane Dada harkan wayewan nan nasu ne da kwadayin dan kayan dasuke kashewa su mika mata ya rudeta Dada tace ku kyaleta har yaushe ne muna nan zaki jita dasu indai yaran nan ne masu halin uwarsu.
Kudai Dada in zance ya tashi uwayen mu daine masu halin banza ba,ataba cewa uban mu saidai uwa na fada ina dariya tace rabu da nono dakike gani nono shine babban alkalin da a duniyan nan.
Indai ka tsotsa to sai kayi wanan halin kai,ko don shi ake son uwa da hali nagari mai kyau don zurian da zata haifa gaba suma suyi koyi da halinta nagari a duniya.
Haka abubuwan gidan suke tafiya da dadi ba dadi son babu yadda za,ayi ace an zauna a cikin dadin rai ko yaushe abu dayane dai dake sa ban damu ba don sakewa da hjy mum din ya taimaka min sosai zaki samemu a tare ko wani lokaci ba zaki dauka cewa ba ita bace ta haifeni don sai ince yanzuma da nake ni kasai din nan a wajenta nafi farkon zuwan mu jin dadi.
Don ina samu kula na musanman daga wajen yayanta maza sun daukeni tankar kanwa a garesu wani lokaci suvtsawata min wani lokacin kuma idan kin samemu a tare muna hira dukan mu a falo har mum idan suna gari saiki zata dai uwarmu daya dasu dama.
Saboda natsuwa na fara hango matsala a tsakanin halima dasu Mairo bandai gaskanta ba don haka ban fadawa kowa ba nabar zancen a cikina.
Ganin yanayin da muka fito gida ranan har aka saukemu halimatun batayi magana ba yasa na dake nima ban tambayeta ba duk dako idonta ya nuna tayi kuka a ranan sosai saboda yadda idanuwanta sukai hulu,hulu dasu alaman kuka tasha a lokacin.
Ban damu da zuwa da kudi school ba amma duk da hakan sai mum ta matsa na dan riko kudi don wani lalura amma abinci kan mai kyau har saina koma dashi gida don kadan zanci in rufe inkoma gida dashi .
Wata rana kuma inba wa yanda ke bukata don a waje ko yayane saika samu wanda kafi koka darashi sukan zo takanasa su tambayeni abincin na basu.
Duk da zuwa yanzu kusan yan ajinmu sun gama sanin cewa rikona ake gidan daddy ba shine mahaifina ba kamar yadda suke zato don halima ta gama fada masu cewa rikona akeyi a gidan ai.
Kwatsan saiga halima tazo during breakfast tana fadin don Allah zeey kokin raga abinci ki taimaka min inci tun jiya da rana rabona da banci komai banci ba.
Cikin tsoro nace subbahanallah garin ya keko halima zaki hora kanki da yunwa haka alhalin ba abinci kika rasa ba don Allah batace dani komai ta karba ta zauna a seat dina tana ci saida ta gama dashi.
Gashi ranan doya da kwaine da soyayyen nama mukayi breakfast dashi don mu biyune kadaica part din dagani sai Mum kowani sati kuma ana kawo masu kayan abinci a raba a gidan.
Don haka gaskiya zance Alhamdullahi gaskiya do banda kunci rayuwa ko kadan abu daine wanda ba,a rasa ba tsakani idan ance mutum bai haifeka ba dole sai kaga ta wani fannin bai kyautama ba a ganin ka shiko yana maka iya bajintarshine.
Kodana dawo sayo muna drinks kallon kulan data aje gefe nayi ina fadin bakiji dadin abincin bane halan don harda girki kiri kiri tace min part din hjy malka sunfimu abincin zamani mai dadi ita hjy mum kullun sai abinci iri daya takewa mutane .
Wanan yasa nakai ga tambayata hakan ta dan sake murmushi afuskanta na mika mata goran cock da ruwa dake hannuna ta karba da sauri ta bude ta kwankwada sai gyatsa har abin ya bani dariya.
Kusan kwanaki muna hakan kuma Allah bai ban ikon tambayata ba ina dai saka abinci mai yawa wanda zamuje muci tare da halima duk mum bata sanda hakan saini da kaina wajen sabarin bakina na tonawa kaina asiri.
Nace ai yanzu da halimatu muke cin abinci shiyasa nake cinyewa ban dawowa dashi gida kuma don kullun kamar da yunwa take kwana wani lokacin kafin ma a tashi break take soma satan cin abincin.
Wace halimatu dai badai ta gidan nan ba sai datayi min wanan tambayan nagane katobaran danayi din wajen fallasa kaina a sanyayye nace itafa Mum.
Ya akayi ta zauna cin abincin da baida dadi nace nima ban sani ba kullun dai tana zuwa kamar mai yunwa a haukace wani lokaci ma saina bar mata abincin taci ita kadai.
Amma ko yar nan bata da kunya tunda har ta iya zama taci abincin mu nace mum baki ganta bane halan kwana biyu duk ta fita hayacinta fa ta rame ta lalace yan kwanakin nan.
To Allah ya sauwaka saiki kara yawan abincin yadda zai dinga isarku kada ki takurawa kanki kumake nidai bani hora mutum da abinci dama ita tagujemu ai.
Abinda ban yarda shine tace zata dawo part din nan kuma da zama yanzu in yarda gaskiya wanan ban dauka amma don abinci ki dinga zubawa da ita kuci kullun.
Irin wanan halaiyan na hjy mum yasa nake kara ganin mutuncinta a idanuna don macece wance tasan kanta da darajan duk wani mahalukin dan adamba duniya.
Don hakane na canza muna kulan abinci ko ya akayi yaran suka gane suka fadawa uwarsu zamu tafi da safen Friday sai ganin hjy mummy nayi tsaye bakin mota har na karaso ina gaida ita bata karba min ba.
Sai cewa da tayi ke wanan meye kika dauko haka na dan daburce ina kallon bayana don ban taba zaton dani take ba a lokacin sai cewa tayi dake nake na dan kalli hannuna dake rike da ledan da na riko na kayan abincin nace wanan abincinane a cikinsa.
Dakata kiji don nasan ku da gadon munafunci kamar tsiya inke da uwar rikonkoki kuka daurewa halimatu a gidan nan wallahi sai ranku ya baci ai ita hjy kuburan tasan halina idan ke baki sani ba.
La,ila ina ruwana da halima da zaki kirani da munafuka na fada a dan hasale don nasaba data taba a lokacin tace mun gada gunwa ke nan iyayyen mu take nufi wai wazan baka so a jikinka kamu na zagin koko.
Amma yarinta da tashen balaga bai bari na tuna hakan ba lokacin sai wanan amsan dana bata nima bansan zai fito min ba sai naji tace ke nikike son mayawa da magana ki kama kanki kafin bakin nan naki yaja maki matsala a gidan nan wallahi.
Mota nayi kokarin shiga ina gunguni ciki ciki ina fadin ni ina ruwana da zabcen ku nidai nasan ba munafuka nake ba wallahi.
A,a mommy na fada maki kibar yarinyar nan don yanzu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login