Showing 18001 words to 21000 words out of 103712 words

Chapter 7 - DUBA MIN BAYA FAKON BIRI BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

7839

da kanta gefe daya nace a raina in ma bata hanani ba ni zan hana kaina ai bandai tsunka ba balle nawa ya sameni a wajen Dada.
Saiga hjyn da muke dakinta tayi sallama ta shigowa Dada da abinci har kasa takai ta gurfana tana fadin ga abinci hjy tace sannu yar albarka har kin hada girki.
Ta danyi murmushi tana fadin tare da yata mukayi hjy ashe yar nan ta iya aikine haka itafa ta tuka min tuwon nan kwasan ledane kawai na karba nayi don da alama bata iyasa ba.
Dada ta karbe da fadin saina kwano kwaso zube da muka iya mukan shita saba dashi a can ba ruwan mu da cin tuwo a leda kamar yarbawa donsu muka sani da da kwasan tuwon leda idan suna buki.
Sai gashi yanzu kuma yaran mu kun iya wanan tabi,an nasu har makun darasu hjy idan ka kwashe a ledan ne yafi kyau da kuma karko amma a kwano sai yayi saurin lakacewa yayi sanyi nan take kuma.
Ayyo haka zancen yaje ashe Dada ta fada tace ku kuka gane hakan mukan bamu sani ba shiko mukai taba mahaifanku kuma basu korafi.
Cigaban zamanine hakan hjy yanzu kan idan mace na wancan kwasan naku saima a dauketa kazama a nan jin hakan yasa na dan dago kai na kalleta kadan na sada kan nawa kasa.
Ta kallomu tace yan matan Dada ko a kawo maku naku nan da sauri nace gwaggo bari nazo na daukar muna na fada ina mikewa tsaye da sauri nabita na karbo muna abincin.
Wanda zamuci har mu rage sabanin wanda hjyn su Nafisa ta kawo muna shimkafa da wake da salat sama wanda dada bataci ba wanan din yanzu taci sosai har wanda muka raga tana fadin a je zatayi saura dashi da safe ta karya.
A nan part din kuwa taliya suka sulala shine abincin darensu wai tunda baba ba a bangaresu yake ba ranan shi zasuci su kwanta hakana.
Ranan sunsha tsina wajen Dada yafi cikon kwando don sai fadin take saboda lalaci ga abinci amma saboda kyiuya mace bata iya tsayawa ta girka don lalaci.
Karfe tara mukaiwa Dada sallama zamu kwanta take fadin har zaku barni jifa Dadan nan kamar bake bace kika ishemu da fada tun dazun yanzu kuma munce zamu kwanta kin koma fadin har zamu tafi.
Koda muka shigo part din yana rufe amma muna murdawa ya bude muka shiga ashe mai part din tana falo wajen maigidan a lokacin.
Sai muna batun mu kwantane mukaji muryanta tana fadin har kunshigo sannunku da dawowa nayi mamakin jin hakan a bakin babban mace kamarta saidai dana tuna hali kowa da nasane na kyale.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[1/21, 22:25] Aishatu Aliyu Musa=??>?p?: DUBA MIN BAYA FOKON ,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

7??

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Washegari ban ma san hjy din tana turaka ba nidai na tashi kamar jiya nakama gyaran waje har zuwa kitchen dinsu da yanzu nasan lungun da yake shine can karshen part din.
Sai kofa da zaka iya budewa kayi wasu aiyuka a baya wanda ba cikin part din yake ba shi bayane fili sai bakin famfo dake wajen da wasu abubuwa dai haka.
Ba inda bangyara ba a wajen komai tsab don na tari sa,an asuba babu jin zafin aiki saboda a kwai ni,ima a lokacin aiki yana da dadi.
Takwas da rabi har nagama wanka na saka yar dogon rigan atamfam rubata a jikina irin dinkin mu na yaku bayi da zai nuna nidin ba wata bace.
Ko dakin Dada ban shiga ba na nufi dakin Nafisa din kwankwasawa uku na samu ta bude har ina niyar komawa baya a lokacin ciki magagin barci ta taso tana fadin wai wayene haka dan Allah ?
A raina nace tirkashi tana bude kofan take fadin wai kece dama ai kofan ma ban rufe ba sabodake don shigowarki na barta bude.
Bayanta nabi take fadi kinga wanan kayan ta nuna min tarin kayan da aka jibge saman kujera tace wanan kada ki fara tabashi amma na cikin closet din nan don Allah gaba daya ki gyara min su ki hada ko wani da dan uwansa har gyalen ma.
Duban tarin kayan nayi a raina nace tirkashi wanan duk kayan mutum gudane haka yaushe har mutum zai tsaya sakasu don Allah wanan irin abu haka ?
Wasu manyan ghana most go ta jefo min guda ukku tana fadin ki jera minsu a cikin nan amma don Allah na less daban buje da riga daban sai na zannuwan suma daban.
Na,amsa da to saidana dan nisa na fara yin yadda tace takoma ta nade a cikin bargo nan dai naci gaba da aikina abu wasa wasa har yakai ta tashi tana kallona daidai nagama jera zannuwa din zan fara na less ina dagowa naji taja tsuki daga bayana.
Hakan yasa na dan juyo tace kin ganene dinga nuna min akwai wa yanda zan cire dama kin hada wanan dinne nace ehh to ki fara wanan haka dole ta mike tare muka hada kayan da ita don nikan yafi karfi na.
Saukin abin takance dani ai wanan zai maki ko idan nace ehh sai ta nuna min gefe daya na aje da haka har muka karasa da kyat komai nata da takeso saida muka hada a dakin nan tsab mukayi packed dinsu a waje daya tasa na daure wanda ta bani cikin wani zanin gado gefe daya.
Ashe gwaggona ta taso taga har tayi aiki bataji durina ba ga alaman nayi aiki kuma don ta samu komai tsab a kitchen din ma na gyaroshi tsab har yakai taje daki bata ganni ba yasa taje dakin Dada nan ma banciki.
Saida ta kawowa Dada abin kari take tambayana don halimatu tana bandaki bata samu tambayanta ba Dada ta tsoratata da cewa bakiga Abulle ba tun safe ?
Ina ta shiga ni safiya a garin nan kuma sai gashi wai ana nemana halimatu tace ba tana wajen antyn nan ba ke Dada kin mantane da tace yau da safe zasuyi aiki dakinta hakan yasa Dada ta samemu dakin tana masifa.
Lokacin ma mun gama ina gyara kulle abinda ta ban tace don Allah Dada ki rage wanan fadan yarinyar nan ta gaji da yawa wallahi tun safe muke abu daya da ita ni nama gode maki wallahi dakikazo da ita ai da bansan yadda zanyi ba.
Ehh kyace hakaman tunda ga jaka na kawo maku ko to bari kiji bata karawa kowa wanan aikin wahalan kinji ke kuma na fada masu.
Haka na kinkimo kayan data bani din muka fito da Dada lokacin Dada tace wanan fa badai wanki bane kuma tace aiki tambayeta na juyo cikin muryan nan nawa nace Dada bani tayi fa.
Owoo yanzu naji batu ashe kinsan ya kamata na dauka halin banzan dai zaki gwadawa yar mutane kuma tunda ba sanin ya kamata kukayi ba ku.
Ke dai akeji yanzu ta fada tashige bandaki ta turo kofan da karfi zamu shige wurin Dada day??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????an ta fito tana yauki tacewa dada din duk kin hanamu barcin safe yau wajen masifan ki .
Saida ta juyo ta kalleta tace saiki kira ubanki ya koreni gidansa tunda na hannaku barcin hasara barcin safe tana fadin hakan muka shige daki.
Zance zuwan Dada gidan gaskiyane kamar ya takurawa yan gidan gaskiya don yadda take basu amsa gatsal zaka gane babu shirin arziki a tsakaninsu da ita.
Zakace ba irace kakarsu data haifi mahaifinsu bama don bata raga masu ko kadan da sunyi mata take basu amsa take a wajen kusan haka halinta yake ko banza saidai nasu din yayi yawane nagani.
Nikan dana rugumo kayan zan nufi masaukin mu dashi muka hade da gwaggon mu cewa tayi dani bayan nagaisheta wanan kayan na meye kuma ?
Cikin dukar dakai nace wanan antyn da zatayi aurene taban su ta mede baki tana fadin nasan tarkacen tsunmakarane ko ke me zakiyi dasu kuma bandai tanka ba na shige dakin dasu na zauna ina dan dubawa daya bayan daya .
Ni dai ani kan kayan sunyi min gaskiya ba laifi ina na taba saka less me kyau irin haka aina samu na shiga buki na fada a raina.
Wanda naga bani so suna ajewa halimatu don nasan zatayi korafi ban bata komai daga ciki ba kala ukku nacirewa halimatu din na kwashi wanda na zaba har na halimatu buuu nakaiwa gwaggon namu ta gani.
Sai cewa tayi suna da dan dama dama ai kin gode nidai naja bakina nayi shiru inda naga suna saka kaya a drower dakin nabude nasakasu har yar jakkar kayana na warewa halimatun nata.
Data shigo na bata takoyi murnan hakan lokacin dana bata din don ta nuna farin cikinta sosai nan muka wuni muna taya mai shiyan girki har yamma muka shiga wajen Dada.
Tana zaune saman carpet data idar da shaf,i da wutir din ranan muka shigo ta dago kai ta kallemu gaida ita na farayi da Dada mun wuni lafiya ?
Ta amsa cikin dadin rai tana fadin ai nake tambayan ku dazun uwarku take fadin kuna can kuna tayata aikine kun karasa ko na amsa da ehh Dada halimatu wuri ta samu tahaye gado ta kwanta.
Ke kam anyi mashiririciyar yarinya duk wahalan ki kin kai na yar uwarkine da suka mayar kamar boyarsu ni inkin debe Kubura sai ince duk ta bar masu ko kawarda kara a gidan nan.
A,a Dada aiko aikin ta yaja muna alheri gashi har nima da ban masu komai ba nakai ga kala ukku masu kyau da tsada kaya masu kyau ta samo muna fa da batayi ba ina zama zai samo muna wanan alherin kuma ?
Ke arr ja,iri dayi banzane ke kiyi mana ko duniya da kayan cikinta zasu bata ba kumce ba na hana wanan bakin aikin da batazo wazaiyi masu shi ?
Dada ki bar halimatu kara zugaki fa takeyi tace aina fahinta basu dai son suga bakin mutum yayi shiru ke dai yar albarka mikon min tuwo naci tun dazun nake son in bude naga me suka kawo min koda yake kuburace a kitchen din banda matsala yau da bakin cimarsu.
Mata ki zauna kiyi girkin kwarai ba zata tsaya ba yau ko wuni gidan nan marka batayi ba inama har yanzun bata dawo ba wai suna wajen hada kaya can gidan da za akai yarta.
Banda lalacewan zamani ina uwa ina zuwa kallon jerem yarta kuma kisan zamani yaci baya a yanzu kunya ya fita idon mutane ni wanan abin kunya ina zan iyashi don Allah ?
Da dane ai tana gida ta saka yarta gaba tana kara mata huduba kan zaman aure amma kaiya haka zata dunkulata ta kaita solai solai kamar rukumi da kaya sai karyan arziki kawai ina aure zaiyi karko a yanzu don Allah.
Toke Dada mu ina ruwan mu da wanan zancen ki samesu mana ki fada masu kinzo nan kin tasamu gaba kina zuga fada kamar mu zamu hanata hakan.
Ban iya fadan ne kome ta fada a hasale wanda hakan yasa na tsoma masu baki nace a,a Dada don Allah dai kyale halimatu ba komai ne zakiga sunayi kice sai kin maganta ba don Allah ki kyalesu kila haka al,adan garin yake.
Tace kuma fa yar nan shiyasa nake sonki dan halin manya iyakata ko idon don kinji dazun mara kunyar yar nan ta fara zancen nazo ina takurawa rayuwansu ai.
Ki kyalesu Dada a rabu lafiya tunda haka suke abinsu kinga sai a zauna lafiya inma tayi maganan bari zasuyi halan wahal da kanta kawai zatayi.
Waini kike fadawa hakan to kaf dunsu gidan suyi kadan duk iya shegensu kyalesu nakeyi bani hauhuwan da wata tazo daga baya ta nuna min iko a kansa.
Mikewa nayi na dauko kayan abincin na dire a gabanta ina budewa kamshin man shanu ya bure dakin lokaci guda jin hakan yasa ta kallo miyan tana kura mai idanu.
Tuwon shimkafene miyar kuka da tantakwashi yaji kayan yaji gwanin ban sha,awa sai kamshi ke tashi na kara jawo plate gabanta ina fadin Dada biyo za a bude maki ?
Fara bude min gudan ta fada tana shafa wai addua a jikinta bayan ta gama yanka masifa yanzu na ba gaira ba dalili kan abinda bai shafota ba a daidai lokacin kuma wanan hjy ta shigo dakin.
Tan fadin hjy kin ganmu sai yanzu yau tun safe dana fita ban samu kaina ba mutanene yanzu basu sa gaskiya ko kadan mun bashi kudin kayan nan da dadewa sai jiya da mukaje kwasa yake son ya kawo muna wani zance kuma.
Sannu da zuwa mama na fada tare da gaida ita ta da mika hannu tana fadin yauwa yan matan hjy kuna nan kuna fama da rigiman tsohuwa ko ?
Ta kalli abuncin tana fadin yauwa ankawo maki abinci ko dama na damu wallahi na barku tun safe to ai dadin mutum biyu din ke nan a gida in guda bata nan daya na nan sai kiga gida ya rayu yadda akeso.
Jin hakan batace komai ba sai cewa da tayi ke Nafisa yau tana ta yabon ki kin mata aiki sosai kun shirya kayata nikan ina naga lokacin wanan yanzu.
Muryan babane shima ya shigo dakin nan muka zube muna gaidashi din har halima dake saman gadon ta sauko yake fadin ashe kina nan kina cin abinci yanzu nake maganan ki shigowa na kenan daga kasuwa.
An dawo lafiya ko Allah yayi albarka abinda ake nema Allah ya baku ya amsa da amin lokacin hjy ta juya tabar dakin ya kai zaune gefen gado ganin hakan yasa da sauri namike zan fice daga dakin.
Muryanshi naji yana dakatar dani ta hanyar fadin dawo ki zauna abinki ina kuma zaki mamana ba a binci zakuci bane ?
Dada tace wanan nawane nasu nacan gun uwarsu ai aini kubura ta kyauta min datayi min tuwon nan amma wanan hanjin da matarka ta dinga tura min kwana biyu ai saiya kaini asibiti ba shiri.
Kallon juna mukayi da halima muna kumshe dariyan mu ya dade a dakin yanawa mahaifiyarshi bayani kan bukin anan muke jin cewa ai mai mata zata aura ashe .
Da sauri Dada din tace aikaji ita kuma gun mai mata ta kare sunki auren hadi da zuria suka gada tun iyayye da kakani a nan kuma yanzu ta fada.
Aina fada mata tun farko daga ita harshi babangida din tunda sunki hadin da mukai masu yanzu banda korafi daga baya sai Dada din tace Allah dai ya gyara kundai bi ra,ayin diyanku kada ransu ya baci a nan .
Amma banzaci hakan ba gareku don ban taba tunanen wanan zamanin zaizo ya sameni da raina ba Allah ya gyara yace ya dan dukar dakai.
Muma dakin shiru mukayi kamar ruwa yaci kafin Dada tace dashi jeka huta da iyalin ka Allah ya bamu alheri ya mike da kyar da alaman wanan maganan ya dan tabashi lokacin.
Yana fita nace ci abincin Dada kar yayi sanyi tace to yar nan ke dai ta jawo abincin ta faraci halimace son jan magana ta sauko daga saman gadon zuwa kwabon abincin Dada ta tsami nama daya ta mike da sauri tana dariya.
Dada din tace ja,ira baki jin bakina tunda mai kaunata ta hanani yawan magana nace haka shine daidai ai Dada dinga sawa kowa ido wata rana zasu tunaki.
Ashe gaskiyane wasu yaran zuciyan manya ake dora masu ashekarun nan naki kike wanan maganan tankar yar shekara hamsin gareni Abbulle gaskiya ba karamin tarbiya da hangen nesa iyayyanki suka baku ba .
Da duk uwan zamaninan zasu diga lurar da diyansu alkibilan alheri da har yanzu duniya tana kwance tana barci yadda aka santa a baya amma kayya a yanzu mun aro wani akida mun yafawa kan mu na bata da sunan boko.
Naman ta dauko ta miko min na girgiza kai ina fadin a,a muma ansaka muna munci Dada wanan rabonkine ai wanda naci ma gashi ya lake min a hakori yana damuna yanzu.
Yarinya mai dabara karna matsa maki ki karba kikace hakan sai na dukar da kai ina dariya adaidai lokacin wanan karamar tasu data dan girme muna tashigo dakin babu ko sallama da waya makale a kunnenta tana fadin gani dakin ai nashigo.
Duk muka bita da kallo cikin mamaki wanan shigowan nata haka babu ko sallama itako sai cewa da tayi ehh gata zaune ai OK sai kawai ta miko min wayan dake hannuta din.
Ban karba ba sai dago kai da nayi na kalleta a cikin mamaki kafin na mika hannu na karbi wayan daga hannunta bayan tace a cikin tsawa ki karba mana sisterce ke son magana dake.
Na karba na kara a kunne na naji tana fadin sister ki shiga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login