Showing 48001 words to 51000 words out of 69829 words
Chapter 17 - KWANKWASON JIMINA BOOK 2 COMPLETE BOOK 2 hausa novel
cigaba da cewa da ita,
"Da farko ni marwaan sambaso lokacin dana fara ganin ku dinnan daya ke cewa kin tare masa wajen parking lot. Har ga Allah Anees ya bude baki zaice wnai abu nayi hanzarin cewa dashi ni nayi mata Ina nufin ke kenan. Sai yayi murmushi kawai, tun daga lokacin aboki na ya nuna yabar mun ke nasan halinsa komai da komai. Tun daga lokacin yake kokarin nesanta kansa daga gareki. Ni Kuma by Allah alokacin kawai irin nayi niyyar date and dump dinnan Kawai zanyi .saboda haka nakeyi by Allah player ne ni lokacin, Idan na samu kin karba soyayya ta sai na yaudareki nace bazan cigaba da alakan dake ba. Nayita cusa Kai na agare ki. Har kika amince, Shekarun baya Muna fteshers abokina ca sukeyi dani play boy.... Ko M-Con. Saboda dai iya tsara mata da yaudarar su. Tohm Amman bansan haka destiny na zai canzu akan ki ba. From playing/toying with your feelings sai na koma praying to have you as a wife. Allah ya kamani na kamu da madaukakiyar kaunar ki. Inason na mallakeki a matsayin matar aure, Amma kafin sannan ko zaki iya tunowa da abaya idan kunje wajen cin abinci ko in kinje aji ana kyamatarku suna bullying naku? By Allah Anees ne ya hanasu Nawraah. Ko kinsan cewa kyamatar ku da ake ana muku dariya da farko da kuka shigo da aka dena daga baya waye? Ba kowa bane fyace Anees shi ya hana adena muku. Da kudinsa da guminsa sanda kanwarki batada lafiya dinnan kunje asibitin cikin school ..Nawraah wallahi ba karya nake miki ko ince zan miki ba. Anees shine Wanda ya turomin sako yace gashi Kun kawo wata yana tunanin sister dinki ce karama, sannan shine Wanda ya biya likitoci da nurses din da suke a tsaye suka mata aiki da sauran abunda ya dace. Wallahi ba kwandalata aciki.... Nawraah Anees bai bar asibitin ba. Tun lokacin sai dai yaje gidah ya dawo ya zauna a waiting area da facemask yana ganin shige da ficewar ku. Dukkanin abincin da ake ta kawo muku na abinci da sauran needs tun sanda kuka kwanta zuwa sallamar ku dik shine..hospital bills Kai komai da komai Anees ne...."
Ya karasa magana yana tura mata wasu hotunan.. hotunan receipts na shedar biyar an saya abu da pos. Da wani littafi dake dauke da biro agegensa.
"Kingane wannan book din?"
Nawraah da gaba daya so take ya dena gaya mata maganganun haka ta samu ta kwanta. Tace dashi cike da kufulewa,
"Na abokin ka "
"Na Anees ne..tabbas. duk Wanda yake Alharamein university final year dinnan zai ce books din Anees ne. Sannan ba Wanda yasan ya cikinsa yake duk amincewar mu da shi kuwa .. Bai masan na sato masa ba acikin mota rannan. Amman akwai wani abu dayake Ko kina waje duk inda kika Saka yana biye dake. Zai faramiki zanen. Zanen fuskar ki da jikin ki. .... Duba ki gani hotunan dana dauka duka zanen ki yayi. Ki duba sauran hotunan Dana yi screenshot..tarin hotunan ki ne Nawraah tun ranar da kika fara sanya kafa a makarantar Alharamein. Anees bai tsayar da alkalaminsa ba..bansan yanada wannan talent din bama sai akan ki. Duk inda kike zai fara zana hotunan ki. Ya na lura dake sosai. Ko sanda kika kirani ban dauka ba last. Anees yakirani na dauka ranar ma na san yana bibiyar ki ne dan tsaro.. temaka dai Nawraah. Anees wallahi yana mutiar kaunar ki fiye da yadda bakina zai furta miki. Fiye da yadda hannu zai rubuta Miki . .dik yadda zan sarrafa ba zaki gane ba. Amman ki sani Anees abubukhar dollars yana kaunar ki sosai. Kaunar da zai fatan samun ki amatsayin matar sa. Amma guess what? Saboda loyalty da Kuma girmamaawa irin nasa. Ya kauda kansa yayi tamkar ba sonki yake ba. Kamar bashi ya fara ganin ki yaji yana sonki ba..ni nayi masa shigar sauri. Gashi bayason alakar zumuntakar tsakanin mu ta rage. Shi yasa ya hakura yabar mun ke. Tundaga ranar don ba zai iya tsayawa muna musaya akan mace ba. Nasan halinsa zan shede shi..abubuwa da yawa dai Nawraah. Anees is your truest lover, He loves you beyond your wildest expectation.. Amma saboda son kai irin nawa, da selfish interest na kasa nuna masa nasan shine yake sonki tun fari, naki bashi kofa, Ina babba gaba da shi naki cin girman na bar masa, saboda gaskia sonki ya mun rikon karfi I can't do without you, ke ce bazan iya barwa Anees ba. Amman duk abunda na mallaka zan iya bashi... karki ga kaman na hakura da kene no, not a bit. duk da haka ban hakura dake ba fa..shi ya zabi ya bar sonki a ransa bazai gaya miki ba tunda mai hakuri ne.. So saboda hali na rayuwa. Dakuma dubada yadda muke cikin matsatsin abubuwan da suka gabato mu. Komai sai da albarkar iyaye..inshaa Allah ban cire ran auren ki ha Nawraah... Sai dai ko idan rai yayi halinsa. Shima ran idan yayi halin nasa a sannan ne to zan rokeki da Allah ko bayan rai na ban yadda ki aura kowa ba fyace Anees. Ke ko Allah yayi auren mu sai mutuwa ta riskeni. Dan Allah ki auri Anees shi kadai ne zai iya rikemun iyali na....... Ina nan Ina cigaba da shawo kan mahaifinw. Domin su maka kansu a kotu idan sun tabbatar da shedar su din basu aikata ba to sai su fuskanci wani abun ...
"Zain iya cigaba ko na barshi haka?" Marwaan ya rubutawa Nawraah bayan yayi vn..
"No " ta amsa masa da reply
Marwaan yaga sakon ta ya shigo ya sake danna speaker ya fara mata wani vn din .
"Ni dai Dan Allah ki yafemun, nasan ni mai laifi ne awajen ki. Amman ki sani wallahi Allah banda masaniyar abunda iyayena suka aikata akan iyayen ki. Ko faifon bidyon nan ni ne Sanda Muna ta video call da baban mu shine naga shi mutumin mahaifin ki kenan ya shigo haka suna yar tsama sai na danna recording na bidyon bayan naga abunda ya faru bancewa mahaifi na nagani ba nace nabar wajen yanzu na dawo wajen system din. Anan na fara bincike akan iyalin naga duk sun rasu sai babban dan su na samu aka samomin number sa na sayi sabon layi anan kasar wajen nayi registering number na tura masa bidiyon Ina tura masa na tabbatar ya karba kawai na yi de-actibating layin gaba daya. Bayan mun dawo Nigeria ne just recently bayan mun samu sabanin nan dake har kike fada shine nasan mahaifin ki ne, sannan yayan ki ne wannan dana turawa shima ya rasu. Dan Allah kiyi hakuri banda bakin da zan iya wanke Kai na awajen ki. Amman ki sani tabbas iyaye na ne su amma wallahi banda masaniyar abubuwa da suka aikata Nawraah.. duk wani lefi dana miki Dan Allah ki yafemun ki kuma dubi maganguna... Allah ya baki hakuri ya shiga cikin lamuran ki da yan uwan ki. Kuma inshaa Allah zan cigaba da fafutar nema muku hakkin ku da yardar Allah. Ina fatan Kuma nasara ce zata biyo ba. Love you die💜"
Ta gyara kwanciyar ta hawaye na zuba daga idanunta. Maganganun sun matukar sata razana, tu'ajjabi da kuma ban mamaki... Kawai ta Saka hannu ta katse vn bayan tayi forwarding dukkanin chats din nasu zuwa number ta. Ta yi blocking number tasa tayi deleting gaba daya..
A ranar dai bacci ya kauracewa idanun su har aka kirayi sallar asubah... Kowanne bangare na cikin wani hali marar misaltuwa musanman Nawraah jagora kasancewar ita din KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA....
_ADVERT👇👇_
_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
_K'K'J_
_(M/W/S)_
_BOOK TWO_
_✍️:MX_
_38_
:::::::::
*Tana* zaune a bakin gado tayi wanka ta sauya kaya zuwa na bacci. Ta daga kanta ta sauke akan katon agogon bangon dake wata kusurwa a dakin.
Lokaci yaja ainun mai gidan nata bai dawo ba bai Kuma dauki wayar da take ta kiransa ba. Bai Kuma kirata ba. Ta tuttura masa sako a text message data Whatsapp ba reply. Har ta mail ta tura masa ko zai duba nanma ba respond.
Jikinta ya shiga rawa. Ganin hakan bata taba faruwa ba. Bai taba Kai dare haka ba. Bai Kuma taba kin daukar wayarta ba ko yaga sakon ta yaki magana ba.
Duk ta samu sosai tanata kawo abubuwa da dama..Allah yasa ba wani abun ne ya faru dashi ba. Don tabbas duk yadda akai yana cikin wani hadarin ne kilan..tanata kamo addu'oi abakinta tana rokon Allah yasa lafiya yake..Allah ya Kuma kareshi a duk inda yake
Karar horn dinsa taji ya gama parking . Tana tsaye agaban window dinta na dakinta a sama tana lekawa gabanta na dukan uku uku..ganinsa tayi ya fito daga cikin motar ya jingina ajikin ta yana waya yana murmushi..
Tashiga sake sake a ranta. Ko wani abun ya sakeyi ne yake farin ciki? Ta tuno ai nusaiba ta turo mata sako zasu bar burnin naduka din sun amince. Da yayi wani abun da nusaiban zata fada.
Don haka murmushin wani abun ne na daban kenan? Ko visa dinsu ta fito? Ko wasu abubuwan ne na kadara ya sake mallaka? Saboda duk da dare ne amma dubada manyan futulin wutan da suke wajen sun haska ko Ina tamkar rana kana iya hango fuskar sa tar yana ta murmushi yana dariya. Zaka gane yana cikin madaukakin farin ciki marar misaltuwa.. Kawai dai baa jin me yake cewa saboda akwai tazara sosai a tsakani.
Don haka ta koma ta zauna a bakin gado tana jiran shigar sa. Ya jima kafin ya kare wayar ya shiga cikin gidan . Kai tsaye ya nufi dakinsa ya watsa ruwa ya kwanta..
Shiru shiru Dr bintu bataji ya shigo ba. Ta leka taga ya gama wayar
"News ko ball yanzu haka ya tsaya kalla Alhaji da daren nan" ta girgiza Kai ta sauka kasan tana rausaya..
Shiru taji ba alamar karar kayan kallo ..ta shiga babban parlorn da yake a matsayin nasa nanma ba karar tv.
Bandakunan palukan ta kwankwasaa duk baya ciki.
"Ko wani abun zai dauka a dakinsa?" Ta fada ahankali tanayin hanyar dakin nasa.
Ganin abubuwan takardu kawai da sauran documents muhimmai yake a dakin nasa. Baya kwana a dakin a nata suke kwana..
.
Ta kwankwasa kofar dakin tamurda handle din ta jiyotaa datse.
"Alhaji" ta kwankwasa kofar tana kiran sunansa
Shiru bai amsa ba. Yana kwance akan gadonsa yana danna wayar sa.
Ta sake kwankwasawa da karfi tana cigaba da Kiran sunan nasa. Mikewa yayi daga kwanciyar da yake harda sakin siririn tsaki ya saka hannunsa akan mukullin ya bude..
Baki a wangame ta dube shi. Har yayi wanka ya Saka kayan bacci. Ga Kuma wayar sa ta datake ta faman Kiran nasa rike a hannun sa yana dannawa,
"Ya akai?" Ya ce da ita yana kauda Kai
"Ya akai? Ya akai ka fa kace mun yusuf" Dr bintu ta tanbaye shi cike da mamaki dauke a fuskar ta.
"Idan ba komai zan rufe kofa"
Bankada kofar tayi ta shiga cikin dakin tana daddaga fullallaka da bude drawer ko zataga wani abun na daban ko takardu da sauran su.
"Yusuf lafiyar ka kuwa yau? Kasan me kake cewa? Anya daren nan ba zazzabin ne ya tashi ba? Tun dazu daka fita kace kana zuwa zaka dawo baka dawo ba sai yanzu ba dadewa shine ka shigo dakin ka kayi kwanciyar ka kabar ni can hotiho, inata sake saken abubuwa na dauka ma ba lafiya ba, wani abun ya faru dakai don baka taba haka ba..
Alhaji sambaso ya yamutsa fuska yana zura wayarsa agaban aljihun rigar kayan baccin dake jikinsa yace,
"Bintu ba nasan hayaniya kingane? So bacci nake ji ki fita zan rufe kofa"
"Bazan fita ba. Yau ni kake cewa haka yusuf? Ba inda zani. Sai ka gaya mun inda kaje da wa kuka hadu. Me kake shiryawa. Sannan dawa ka tsaya kana waya ajikin motar ka bayan ka dawo. ? Sannan meya hanaka tahowa dakin mu kamar ko da yaushe zaka zo nan dakin da anfi shekara nawa ba a kwana acikin sa. Har kana cewa in fita maka zaka rufe kofa yusuf ni kake gayawawa haka?"
"Ba zaki fita ba?"
"Bazan fita ba"
"Okay zauna ni bari na bar miki dakin" ya futa daga ciki ya barta a tsaye
Cike da mamaki tabu bayan sa da kallo. Har ya koma dayan parlorn akan kujera ya kuna ac ya kwanta yana juya mata baya
"Yusuf, Idan wasa kake mun dan Allah dan Allah ka dena bakaji zuciyata ba. Gaskia banason irin wannan wasan banaso Allah . Wasa da halayyar da bata ka ba ba saboda Allah. Ni kawai ka fito ka gaya mun menene farin cikin nima na samu nutsuwa amma wannan wasan naka ya yi yawa haka. Dan Allah kaga dare ne Dan Allah. Dama inason nace maka ma nusaiba matar bappan su Nawraah dinnan tace mijin ya amince zasu bar naduka. Ta turomin sako ta text message. Kaga yakamata zuwa da safe ko cikin daren nannma ka gama yanke abubuwan da za'a basu idan ma ta bank ne ai ta bude banki sai a tura mata su tattara su tafi. Inata kira baka dauka a awaya. Na tutturo maka messages nanma ba reply sannan na maka mail ma shima shiru bakace komai ba. Na shiga dimuwa sosai Alhaji. Dan Allah bar wasan nan haka bakaji zuciyata yadda take duka ba wallahi. Kaji? Kaji yusuf dina..?" Ta karasa fada tana kokarin zama a bayansa ta saka hannu tana riko kafadar sa.
Alhaji sambaso ya kafa ya shureta. Sai ga Dr bintu a a kasan kujera dabas a carpet tayi zaman dabaro saboda shurewar buguwar da yayi mata.
"Alhaji wasan har dana shudewa yau?"
Wata wulakantacciyar harara ya bita da ita yana yamutsa fuska. Ya daga yatsa daya ya mata nuni da shi,
"Na gaya miki banason takura, bacci zanyi, zaki wanii zauna a bayana kina kokarin riko kafada ta. Akan wani dalilin? Tashi ki bani waje"
Mamaki ne ya cikata ganin yadda yake magana furucin da lafuzan da suke fita daga labban bakinsa sam ba yadda ya saba magana bane. Bai ma taba mata irin wannan magangunnan ba haka. Tabbas ba wasa a fuskar sa domin a daure take gamau.
"Alhaji"
"Dan Allah dan Allah meye? Kinada takura wallahi "
"an Allah idan akan kiraye Kirsten dana maka ne nonstop da turo Sako kayo hakuri. Ba snaj abun bane kauna ce tasa Wani damuwa... Daman so nake naji ko lafiya ne? Na Kuma sheda maka da sakon amincewar su Nusaiba barin naduka baki daya harda su Nawraah"
"To meye hadina da su? Na fasa bayarwa su zauna kar su tashi."
"No Alhaji nasan ba wani hadinmu dasu, Amma kasan ai dasu Nawraah zasu tafi baki daya. Kuma kai kace a bata offer dinnan da mai gidan yaki karba kwata kwata baka nata tunanin abunda zaka bashi ba ma ya amince? to gashi dai ya amince tace zasu tafi. Kadarar ko kudin dakace zaa basu. Nake tuni nace ko yanzu da daddaren amata transfer ko zuwa da safe ko ya kagani?"
Wani irin dogon tsaki yaja da har sa Dr bintu ta daga Kai tana duban window ta dauka siren ne na yan sanda ko motar kwana kwana .
Sake sakin wani yayi yana nuna mata kofa, cike da fada yace
"Wake miki wasa? Tashi ki fita. Bakida aiki sai maganar kudi kudi kudi kudi kudi dai. To wallahi ki bude kunnuwan ki ji kwandala bazan sake baki ba. Karki bari na sake maimaita miki"
Baki bude Dr bintu take dubansa tace,
"Yusuf... Yusuf Kai ne haka? Yusuf yau ni kake gayawa wadannan maganganun? Kasan me kake cewa kuwa?"
"Kwandala bazan bayar ba. Su zauna ko su tafi su ta shafa ba abunda ya dame ni. Tashi ki bani waje. Tashi!"ya karasa fada a tsawance, ya jawo kafadarta ya futar da ita wajen kofa ya rufe kofar da mukulli...
Mamaki ya gauraye ta. Da baya baya ta jingina da kujerar dayan parlorn ta yi zaman yan bori..hawaye suka shiga wanke mata fuska..
Baki daya ta kasa cewa komai..sai datayi kukanta mai isar ta sosai sannan ta koma sama ta dau wayar ta ta kira kawarta hajia kubra ta gaya mata dukkanin abubuwan da suka faru.
Batayi bacci ba har aka kira sallar fajr tayi sallah har wayewar gari. Sai kuka kawai da take tayi duniya ta mata zafi baki daya...
_ADVERT👇👇_
_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
_K'K'J_
_(M/W/S)_
_BOOK TWO_
_✍️:MX_
_39_
:::::::::
*Bayan wayewar gari* mikewa Dr bintu tayi ta shige bandaki tana duban fuskar ta a mudubin