Showing 39001 words to 42000 words out of 69829 words
Chapter 14 - KWANKWASON JIMINA BOOK 2 COMPLETE BOOK 2 hausa novel
akan yadda zanbi shi mijin ita matar da kike fada aji matsalar sa abashi ko meyake so, su tattara su tafi. Ba shikenan ba?"
'Shikenan kuwa Alhaji. Ka gama magana"
"Ai sai dai idan ban zauna ba. Kudi ne fa yake komai yanzu. "
"Tabbas. Allah yabar mu cikin sa kuwa"
"Aamin dai."
"A kawo abinci?"
"Munci agidan Dr. Amma me akayi?"
"Stir fry rice ne. "
"Akwai ragowar cake dinnan me madara?"
"Tres leches?"
"Eh"
"Akwai"
"To akawo mun sai shayi. Shikenan "
"Tohm"
Shigaa tayi kitchen tana dokawa mai aikin su kira. Mai aikin tanata bacci sai dataje ta kwada mata dundu sannan ta tashi a firgice suka nufi kitchen din tace ta dora mata ruwan shayin Alhaji.
A tsaje a jikin kitchen cabinet ta jingina nan da nan ta hankadawa kawar tata kudin da receipt tana nanata mata da,
"Dan Allah kawata ki temaka a sake rike shi ya saki bakin bakin aljihunsa.. Duk da yanzu ma bakiga ba ca yai na tura ko nawa nakeso kinsan bayason fushi na. Zan kiraki da safe. Nagode "
Tana tura mata da sakon ta kashe data dinta gaba daya. Ta jera komai a tray ta Kai masa.
"Hajia an gama?"
Ai aikin ta tanbayeta tana sakin hamma
"Eh jeki"
Ta datse kofar kitchen din ta koma wajen mai gidan nata. Nan Suka shiga ci suna hirar su har dare yaja sosai tukun suka nufi makwancin su..
*DR. ABUBAKHAR DOLLARS DWELLING*
_ADVERT👇👇_
_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
_K'K'J_
_(M/W/S)_
_BOOK TWO_
_✍️:MX_
_30_
:::::::::
Bangaren sa ya wuce kai tsaye. Ya shige bandaki bakinsa dauke da addua..wanka yayi hadi da tsarki. Ya sauya kayan sa zuwa na bacci. Ya bi lungu da sako na jikinsa ya saka turaruka masu matukar dadi da sanyaya rai.
Wayoyin sa ya dauka da MacBook dinsa ya nufi bangaren mai dakin na sa. Bakinsa dauke da sallama ya shiga
Kamshin turaren wutar yanzu ba iri daya bane da kamshin wanda su kazo dazu sukaji. Lumshe idanu yayi ya bude. Kullu yaumin da irin kamshin turarukan da gidan nasu yakeyi.
Kwarai matuka mai dakinsa hajia Qibdiyya akwai tsafta da gyara. Dukkanin abubuwan da namiji zai samu daga mai dakinsa ta gari hakika hajia Qibdiyya ta wuce ta zarce ma.
Ya matsa inda kaskon wutan keci. Daya a local kasko na karfe daga can gefe. Dayan kuma electric burner ce ke konashi. Wani irin calming and soothing scent.
Ya matsa wajen electric burner din yana karanta sunan turaren daya gani ajikin kwalin turaren dake gefe. 'omani khajingru... By yerwa incense and more.
Ya sinsinar cikin kwalbar yana runtse idanun sa. Saboda kamshin daya gauraye shi. Mai matukar kwantar da zuciya da sakata cikin nutsuwa.
Ya karasa wajen dayan kaskon yana duba jikin kwalbar.."sandal twist".
"Nice" ya fada hankali yana ajiye kwalbar a gefe.
Dai dai lokacin da mai dakinsa hajia Qibdiyya ta sakko daga sama ta karasa parlorn kasan su.
Sanye take cikin wata riga ta bacci doguwa pink color. Ta dora wata rigar akai domin ta cikin me hannun vest ce ta saman kuma dogon hannu ne da ita
Karasawa yayi wajenta da sauri yana riko hannunta. Ya samu kansa da kai mata runguma yana shakar kamshin khumrahs din dake tashi daga jikinta. Ya dauki hannunta yana sinsinar sa shima. Wani kamshin oud kullaccam ne ke tashi daga jikin hannun ga kamshin khumrahs din data shafa.
Ya kai hancinsa kan gashinta dake tashin kamshin scented hair cream na man shafawa a gashi na kamfanin turaren yerwa incense and more man kitso me kamshi da hair spray me kamshi shima.
Baki daya kai baya wari ko tsami dinnan na lokacin zafi da saka masa ruwa na tsarki da sauran su. Duk hajia Qibdiyya ta shafa ta kuma fesa na fesawa.
Ya samu kansa da Kai hancinsa kan kafadar ta yana sinsinar kafadar kan rigar ta dake tashin kamshin tiraren wuta na kaya data turara na kamfanin tiraren yerwa incense and more.
"Mariya....Tahhhhhhh" ya karasa fadan sunan yana jan taahh din cikin wata siga
"Naam baban su, sannu da zuwa"
Murmushi yayi ya kamo hannunta suka zauna akan kujera yan duban ta sosai yace,
"Allah ya miki albarka . Hakika banda bakin godia agare ki Mariya. Nayi saa nayi dace da samun mata tagari uwar ya'yana ..har gaban abadan bazan daina yiwa Allah godia ba bi saga wannan babbar kyauta da yayi mun na auren mace saliha, Mumina, Mai ibadah, Mai tausayi, Mai tarbiyya, Mai Kamala, Mai kyau, wadda ta iya girki da daukar wanka Kuma ma'abociyar turare. Mariya komai kin hada a mace. Gaskia na yi babbar sa'ar samun ki uwar 'ya'yana"
Murmushi ta saki tattausa tana girgiza kanta hadi da kamo hannunsa tana matsawa da duban cikin idanunsa ta dan langabar da Kai tana turo baki gaba cikin kissa da shagwaba tamkar wata yarinya tache,
"Baban su... Kullum cikin sawa kaina kato yake kake. Hakika Kai din end of discussion ne. As-sadeeq dina daya tamkar da dubu. Ina son ka Ina kaunar ka har karshen numfashi na ba zan dai na rokon Allah ya yaye maka dukkanin damuwar ka ba ya cika maka burikan ka. Ya biya maka dukkanin abunda kake muradin samu. As-sadeeq Kai ne kaahada komai. Duk inda namijin kwarai yake ka ka kai. Ka zarce Kai ka Kuma fin kaiwa As-sadeeq. Hakika Kai din adali ne, gwarzo maabocin addini da kamshi, kyakkyawa Mai kyawun zuciya. Dawisu sarkin ado. Ina gwanin wasu? ga nawa. As-sadeeq hakika na yi mugun sa'a da kansan cewar ni matata agare ka. Domin samun miji Kuma uba nagari ga yayan sa kamar Kai wallah sai an tona. Kai din ka wuce duk inda kake tunani. Kai din kayi gaba sai dai sauran su biyo baya. Mutinci, dattako, Kamala, Ibadah, hakuri, temako, walwala, gayu, kamshi, tsafta... The list goes on and on and on As-sadeeq na. Sakii linzamin ka mai nasara as-sadeeq. Allah ya iya maka ya dafa maka. Kayi musu nisa ya zasuyi da Kai? Wallahi dole su hakuraa. Shi zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzu ana shaho wabillah sai yayi. Shelele na. Habibi da'iman kenan. Na kalle ka nace Alhamdulillah. Na sake kallon ka nace mashaa Allah. Na sake duban ka nace Subhan'Allah Allahu yayi halitta. Duk dan Adam tara yake bai cika goma ba As-sadeeq dina. Kai Kam ka cika taran ka cif cif ba ragi. Allah ya saka maka da mafifin alkhairin sa. Me zaa fara wanka ko abinci ko shayi ko tausa. Me kake so?uhm?" Ta karasa fada tana narka masa manyan idanunta akansa.
Dr abubuakhar dollars yayi murmushi yana matseta a jikinsa hadi da kwantar da kanta akan kafadarsa. Hannunsa daya yana shafa gefen fuskar ta yace,
"Na ma rasa bakin magana . Mariri na rasa ma mezan ce miki. Kin gama karar mun da man Kai na da zan kwarara milk godia .hakika bakina yayi nauyi. Kalamai sunyi karancin magana. Idanuwa na miki kallon kauna da fatan alkhairi. Gabban jiki na maraba da kansancewa a tare da ke. Zuciya na zillon samuwarki acikin ta. Allah ya biyaki da gidan aljannah . .... Ai ina dawowa na wuce bangarena. Nayi wanka. Na kure gayu na shafa turare. Ina zuwa kamar ko da yaushe. Kin sake cinye wankan daren yau . Daga shigar ki zuwa kamshin dake tashi daga fatar jikin ki zuwa gashin ki da kayan ki. Da gidan bakj daya da ke kamshin turaruuka na wuta masu ratsa zuciya da sanyata nutsuwa. Allah ya biyaki Qibdiyya ta .."
Murmushi hajja Qibdiyya tayi tana girgiza kai hadi da dan daga kanta ta saka kan kafadarsa tana duban sa tace,
"Kafi kyawu kyau As-sadeeq. Sai walwali kake tamkar wata daren goma sha tara. Idanuwa na futar da hasken nutsuwa da comfort din kasance wa atare da kai.. Sannu nawan. To ya aikin?. Afuwan.. barka da dare muradin rai na. Fatan ka dawo lafiya. Ayi tausa?"
Ta karasa fada tana kokarin janyo kafarsa. Dr abubuakhar yayi hanzarin riko hannunta yana girgiza kai,
"A koshe nake mariyata. Allah tun abincin dazu bakiji ciki na ba. Ba abunda nake so yanzu sai dai mu kasance a haka muna masu cigaba da hirar mu har ya zuwa sanda zamu kwanta"
.
"As-sadeeq dina kenan. A dai yi hakuri ka asha tea din da dan sauran light food haka ba nauyi kaji?"
"Duk abunda kikace ai hakan za'ai mar'atussaliha"
Hajia Qibdiyya tayi murmushi. Ta mike ta na sumbatar tafin hannunsa. Ta shiga kitchen. Cikin kankanin lokaci ta jere dukkanin abunda zasu bukata akan wani kyakkyawan yadi da amfanin sa aci abinci akai Kawai..
Nan ta jere komai ba akan dinning ba. Ta riko hannuwan sa suka koma can suka zauna. Ta shiga zuba masa komai ta wanke hannunta tana bashi komai a baki. Ya bude baki yana karba suna ci suna murmushi .
Yadda suke zuba kaunar junansu suna bawa soyayya hakkin ta Kai kashe wasu sabbin ma'aurata ne da basu aurar baa.
Bayan sun gama cine. Ta tabbatar ya samu nutsuwa sosai ta fara bashu labarin komai da komai tun daga kan fara aikin Hindu da dukkanin abunda ya faru ya zuwa rasuwar su da komawar yaranta biyu zuwa gidan marayu.
Tiryan tiryan har ya zuwa sanda ta fara sanar masa kadarorinsa da sunayen wadanda sukayi muguntar da makircin.
Ta cigaba da sanar masa komai, Zusa sanda take sanar masa wadanda sukayi muguntar da zagon kasa aka raba shi da kadararorin sa.
Hakika yayi mamaki matuka har yake sanar mata da ma ya fara karkatar da hankalin sa akan Alhaji sambaso amininsa dubada yadda yake bibiyar lamarin da alamun ayar tambaya....
_KWANKWASON JIMINA_
_(MAI WUYAR SHAFAWA)_
_31_
Daga bakin kasuwa ya ke tafiya sambal daga titin zuwa layin gidan sa. Gaban wani shago kadan da ake sayar da kayan dinki ake Kuma dinki ya tsaya yana zaro yan chanjin kudin da ya samu na lodin mota.
Dari hudu da cassa'in ne. Ya kirga su yana zare dari biyu da cassa'in din kai ya mayar da dari biyu sauran cikin aljihun gaban rigar sa.
Sanye yake cikin riga yar shara gabanta anyi aljihu sai hula samfarin tashi ka fiya naci
Yaci saa kuwa wajen mai awarar ba layi. Ana bawa wani yaro ya mika mata kudin hannun sa . Ta sadda kanta kasa tana duban sa tace,
"Ina wuni babaa?"
"Lafiya kalau diyar albarka. "
"Ta nawa zaa bayar ko ta du?"
"Eh ta duka"
Ta zuba masa awarar ta Kara masa wata akai ta daure yaji tana barbada masa kabeji.
Shiru yayi kansa akan awarar dake soyiwa acikin mai. Kwakwalwar sa ta shiga tariyo masa alokacin malama Hindu mai dakin kaninsa malam junaidu.
Tunda ta fara awarar sayarwar har Allah ya karni ranta bata taba karbar kudin awarar su ba. Sannan bata taba fashi ba kullum ne sai ta aika musu da awarar fal da yaji da su timatir da albasa da kabeji.
Idanuwansa ne suka kawo ruwa yayi hanzarin janye su kar su zubo masa.
"Gashi baba" Mai awarar ta sake fada a karo na biyu tana mika masa bakar ledar awarar.
Karba yayi ya mata godia yayi gaba. Ya nufi kwar gidan nasu. Gidan farko kamar koda yaushe sai ya tsaya yatuno shekarun baya alokacin da ran dan uwan nasa.
Samun waje yayi daga can gefe yana duban gidan. Maaikata magina nata Kai da kawowa ana gyaran gidan fadadashi akeyi sosai. Wanda gidan ya koma hannunsa ne ya ke masa na zamani daman gashi gidan fuska biyu ne
Ya tuno sanda motar data kawosu ta saukesu a kofar gidan nasu alokacin da suka dawo garin naduka da zama.
Tariyo komai ya shiga yi yana gani a idanuwan sa. Sanda suka fito daga mota. Junaidu shi yayi masa komai na wayarin wuta da ruwa da sauran kayayyakin gidah alokacin da zasu dawo..
"Innalillahi Wa inna ilaihi rajiun" ya ambata yana goge hawayen da suka zuba masa. Ya girgiza Kai ya mike cikin nasa gidan yana sake maimaita,
"Allah ya jikan ku da rahama junaidu da Hindu da Ashir. Allah ya raya abunda kuka bari ya musu albarka ya daukaka su..Allah ya shiga lamuran su ya musu arziki. Nayi kewar ka junaidu nayi kewa ka nayi kewar dan uwa na gari , aminina, abokin shawarata, bango majinginata junaidu, Subhan'Allah. Gata ya kare Allah ka iya mana. Hindu Allah ya rahamshe ki kema..ubangiji ya dubi bayan ki. Hakika kedin gwarzuwa Kuma kanwata ta gari Kuma mata ga kanina ce.. Hindu Allah ya dubi alkhairan da kika yi ya jikan ki da rahama. Allahu Akbar" ya karasa fada yana dage hanunsa a bango
Ya sanya kasan rigar sa yar shara yana jan majinar data taho masa. Sakamakon mura da lokaci daya ta sarke shi saboda hawayen da yakeyi,
"Ashir... Innalillahi Wa inna ilaihi rajiun. Allahu akbar.. Ya Allah kai kasan munufar hakan. Rabbi ka iya mana, rabbi wadannan bayi naka da ka amshi ransu rabbi yasa suna aljannar ka madaukakiya. Allah ka gafarta musu ka enta su. Allahu akbar. Ashir.. Allah ya jikanka da rahama. Yaron nan Mai zuciya da hakuri da ladabi da kawaici. Yaron nan Ashir ba abunda zance sai fatan Allah yasa kana aljanna, ka dakko halayyar mahaifin ka. Da zuciyar mutuntaka ta mahaifiyar ka. Yaro Mai nutsuwa da son zumunci da yan uwan sa innalillahi Wa inna ilaihi rajiun Allah kafimu sanin abunda yasa ka dauke gatan mu duka. Rabbi ka maye mana zukatan mu dake rauni ka yafe mana muma. Allah mun tuba" ya karasa fada yana kwankwasa kofar shiga gidan nasa daya gani a rufe.
Nusaiba na zaune a kujera tayi zuru ta mike kafa.jiran shigowar sa take don haka da sauri ta mike ta sanya hannu ta bude kofar.
Yana dubanta ya kauda kansa. Ya shjga ciki bakinsa dauke da sallama,
"Wa alaykm Salam" ta amsa shi tana zama akan kujera..
"Layla..Ahmadu"
"Naam.bappah" Layla ta amsa shi daga daki
Ta fito da sauri hannunta rike da maficii tana fiffita,
"Bappah sannu da zuwa"
"Yauwa sannu Layla. Ina Ahmad?"
"Ya fita tun dazu"
"Ungo rike nan awara ce. Ayi hakuri abunda aka samu baki daya dari hudu ne da cassa'in. Na saya awara gatanan ta dari biyu da cassa'in. Gaa dari biyun nan asayo wani abun ayi Kari da safe. Allah yabamu saa"
"Sannu da kokari bappah. Mama ya zamuyi da rabin? Bappah zakaci amma ko"
"A'ah a koshe nake Layla. Mun Sha fura wani bawan Allah ya saya mana "
"Banda tsabagaen gulmar dan ubanki a Ina awarar dari biyu da cassa'in zata ishemu? Mu da ku? Ku kanku ba isar ku zatai ba. Ko ke kadai kika dage tsaf zaki cinyeta. Har nawa take awarar? Tashi kiban waje" nusaiba ta fada tana dankarawa Layla harara.
Da Sauri laylan ta mike da awarar a hannu tana duban cikin ledar awarar tace,
"Ai kuwa da yawa Allah. Kamar tafi ta kudin"
"Eh tasa gyara kamar. Ai tanada kirki yarinyar"
"Ohh ummalo ce ko?"
"Wacece haka?"
"Bappah ba me awarar wajen shagon masu dinki kake nufi na?"
"Eh ita fa"
Layla tayi murmushi tana cusa awara daya a bakinta tace,
"Haka take tayita karawa yafi na kudin mutun."
"Ita Kuma haka take?. Allah Saka mata da alkhairi. Allah ya raya su idan da rabo sai ayi aure ma"
"Amin. Amman fa yaya Ahmad take so" Layla ta fada tana daria ta cigaba dacewa,
"Tayita kunyaa idan ta ganshi. Shine yayanta Gali abokin su ya Ahmad ne shine yake ce masa sokuwar kanwar nan tasu nan duniya shi take so "
Nusaiba ta juya a chake tana janyo tsaki hadi da dankarawa Layla harara a kufule tache,
"Narantse da Allah. Zan Kai miki bugun mahangurba. Sai zuba kike kaman bakin naki ba linzami wacece ummalo? Me awarar? Kike maganar ta da Ahmad. To bude kunnunki kiji...
Dai dai lokacin Ahmad yayi sallama ya shiga parlorn na su Nusaiba na na sallamar sa ta juyar da saitin yatsan da take karkadawa Layla ta mayar dashi kan fuskar Ahmad tace
"Soyayya kake da me awara? Ai Kai har nan har ka Kai minzalin tsayawa da mace Kuna hira ko?idanma zakai budurawar to kaje gidan maiko maiko inda zaka samu ka dandali arziki. Wallahi inde Ina raye. Ku bude kunnuwan ku kuji ba zaku auro yara Tsantson talaka ba. Mai za ai da auren jeka na yi ka. Auren zaman yaran da ka haifa kawai auren kaddara. Auren Allah wadai. Kullum kaine fararo fararo kana yar murya a sanmaka abinci. Ba zeyiwuu ba. Kuce zakuyi irin auren da nayi auren da har yanzu ina dana sanin kasancewar yinsa. To ba zakuyi irin sa ba. Ga damuwa ga yunwa. Da karancin shekarun ka ka koma babba saboda wahala. Ina bazaiyiwu ba. ..kuna ganin matsatsin da muke ciki suturar kirki banda ita. Lahai lahai iska zata dauke mu saboda yunwa. Daga yau karka sake kar na sake naji Kai ko musayar kallo kaayi da me awarar nan sai ranka ya baci. Haka zalika kema shashasha. Kinje makarantar yara masu da hali amman kin ki samo Wanda zaki aura kema auren gatan nan da aketayi kiyi mumaa mu huta. Kwata kwata ba kida saurayi. Amman tunda haka kika tsara shikenan. "
Ta dinga kwafa tana jefa musu harara. Ta dankarwa Ahmad ta juya ta narkawa Layla. Ahmad da baki daya ya kasa gane kan inda zancen ya dosa. Kawai ya sake gaisheda bappan su yana basu hakuri kafin ya mike ya fita daga cikin gidan nasu
Layla ma daki ta shige. Hawaye daya na bin daya. Tarasa wane irin hali ne da mahaifiyar su. Sam kullum ne sai ta saukewa bappam su bubun tijara ba bataa jin dadi. Gashi wani lokacin ma har makota sukan shiga rabiyar fadan su.
Tana danna awarar a baka tana hawaye ahakaa ta karasa cinyewa ta korada ruwa ta goge fuskar ta kwanta.
Nusaiba bayan yaran sun