Showing 51001 words to 54000 words out of 69829 words

Chapter 18 - KWANKWASON JIMINA BOOK 2 COMPLETE BOOK 2 hausa novel

24 Aug 2024

8958

dake bandakin..

Baki daya duk ta zama wata iri lokaci daya ta futa hayyacin ta...idanuwanta sunyi luhu luhu saboda kukan data kwana tanayi...

Wanke fuskar ta tayi. Tayi brush ta futa daga cikin bandakin . Wayarta ce keta faman karar kida.

"N"
Shine sunan dake rubuce a matsayin wanda yakira din.

Katse wayar tayi tana sauke numfashi. Nan aka sake kira har su biyar. Ana shidan ta dauka tana sakin tsaki ta kara a kunnenta

"Ya akai?"

"Hajia Nusaiba ce fa ko lambata ce ta goge a wayar ki?"

"No nasan ke ce. "

"Daman mun shirya ne tun dazu. Ga su Nawraah ma duka a tare damu. Ku muke sauraro."

Dr bintu da gaba daya ahautsine take. Itama kanta balain dake gabanta yayi yawa, tace da ita,

"Nusaiba kawai kuyi hakuri ba abunda zan iya cewa akai."

"Bangane ba hajia. Bangane ba" nusaiba ta fada cike mamaki

"Àbun nufi shine tafiyar nan an soke ta.. Nagode" tana gama fada ta danna mata block

Kasa ta sauka gabanta na tsananta bugawaa..sai kwaraara addua take tana Allah yasa Alhaji maganganun da ya fada wasa yake ba waai na gaske ba.

Ta karasa fada tana sauka kasan. Ba kowaa yaran nata basa nan don haka tace kila bacci sukeyi basu tashi ba.

Parlorn jiya ta kwankwasa, ta dan sakaya hannunta ta murda handle tashiga ciki.

Yana zaune ya sauya kayann sa zuwa wasu fafare. Bai Saka hula ba..

Daga Kai yayi ya dubeta alokacin data yi sallama..ya amsa a hade yana kauda Kai,

"Alhaji" ta fada tana kokarin zama akusa dashi yayi saurin matsawa yana mata wani irin kallo.yana janye plate din gabansa

"Har an maka serving abinci kana ci Alhaji?"

"Of course gidan ki ne ko nawa? Zan jira kine kinje kina ta bacci?"

"Subhan'Allah" ta fada tana dafe kanta saboda tsananin sara mata da yakeyi.

"Daman ba mafarki nake ba Alhaji? Dama ba wasa kake ba Alhaji. Wai dagaske lamarin jiya ya faru Alhaji?"

Ta fada tana jujjuya kanta hawaye na zurara mata. Alhaji sambaso ya dubeta yana tabe baki

Katuwar mota ce ta shigo tana nishi. Alhaji sambaso ya mike da sauri yana ajiye cup din hannunsa akan tray.

Dr bintu itama ta mike tana bin bayansa ganin zai fita,

"Menene haka kike bibiye dani?"

"Lefi ne dan na bika? Beside mota ce tayi kara gatanan ta ta shigo zanga motar meye"

"To tunda ke kika aiko su ai se ki fita kuyi magana ko?"

Girgiza Kai tayi tana ja baya ganin yayi wajen kujera zai koma ya zauna,

"Kayi hakuri"

Ta fada tana komawa parlorn ta zauna. Ya saki tsaki yashiga dakinsa ya fita wajen.

Zungureriyar mota ce katuwa ta wani babban company dake kawo kayan gidah na gadaje da kujeru yan kasar waje.

Akwai wani sashen babba da har yafu Wanda suke ciki kyau acikin gidan yake shima yana facing Wanda suke ciki. Daga baya ya sayi kango ya shigo dashi gidan ya gina sabon an masa komai na wuta da ruwa a bandaki daman kayan gidan kujeru ne baa Saka ba da sauran su. A baya ta bashi shawarar ko idan marwaan yayi aure ya zauna anan . Idan yaso tunda fuska biyu ne gidan sai afutar masa da gate dinsa daban.

Bude baki tayi cike da mamaki gabanta nata bugawa. Zuciyar ta na hasaso mata tabbas suprise (bazata) ne yake son ya Mata bayasan tasan komai akai shysa ya fara acting dinnan.

Ta tabbata sabon gidanda ke cikin nasu da akayin shine Wanda zasu koma ciki kafin su tafi.

Wani murmushi ya kufce mata. Tana sake leka windown tana hango maaikatan nata shiga da kayan cikin gidan wasu Kuma tun da suka shiga basu fita ba da alama jere su suke

Bakinta ya sake hangamewa da farin ciki lokacin data hango wata motar ta sake shiga duake da kwalaye na kayan kitchen kuloli ne da sauran su komai da komai dai na alfarma.

Ta murmusa komai ta haye sama tana jin zuciyarta na mata dadi. Bandaki ta shige ta fyallo wanka ta sauya kaya zuwa wani hadadden lace ta zuba sarka da dankune harda su jambaki ta zurara da hoda. Ta feshe jikinta da turaruka masu matukar kamshi da kwantar zuciya.

Ta gama shiryawa ne. Lily ta kwankwasa kofar ta shiga ta shirya tsaf zata futa,

"Maa"

"Naam Ina zuwa?"

"Salon"

"Okay tohm sai kin dawo"

"Baba ya fita?"

"A'a na dai hawo sama wanka"

"Okay"

Fita lily tayi ta tsaya da mahaifin nata Alhaji sambaso suka gaysa tace salon zata ya bata kudi. Ransa a murtuke ya dakko dubu daya ya mika mata,

"Baaba dubu daya fa ka miko mun"

"Eh abunda zan iya bayarwa kenan. Idan bazaki karba ba kawo"

Bakin lily a bude ta kasa cewa komai. Ga maaikata nata shige da kawo cikin sabon sashen da akai.

"Banaso" ta fada tana mika msa kudin

Ya karba ya cusa a aljihu. Takaici yasa ta kasa cewa komai ta shige mota ta tasheta ta fita.

***

Marwaan da ciwon Kan da yake yaki tafiya. Wanka yayi. Abincin da aka Kai masa yaci ya sauya kayan sa zuwa kanana riga da wando na English.

Fita yayi tsakar gidan na su don hayaniya dayake ji anata magana. Manyan motoci ya gani sunata sauke kaya suna shigarwa sabon sashen.

Ganin mahaifin sa yasa ya karasa wajen sa ya tsugunna,

"Baba Ina kwana..?"

"Lafiya"

"An tashi lafiya?"

"Lafiya"

"Baka tafi aiki ba kenan. Inata sauri"

"Dama tafi zaka ganni ne yan zu a haka?"

Marwaan ya girgiza kansa yace,

"A'a baba. Allah yabaka hakuri"

Ya juya ya shige cikin gidan sashen mahaifiyar su Dr bintu. A tunanin sa har yanzu mahaifin nasa bai daina fushin dashi bane shysa.

Yana shiga parlorn Dr birtu na sakkowa. Ya gayshe ta amsa tana murmushi,

"Ka gayda baban ku?"

"Eh"

"Ya kukai bai gaya maka can gidan gyaran me ake ba?"

"Bai fada ba. Kinsan fushi yake da ni"

"Ni dinma. Amma nafi kyautata tunanin can gidan da ake jere zamu koma kasan da an barshi akan idan kayi aure a futar maka da gate ka zauna aciki"

'oh ai ni banason zama agidah ma. Nafison wata area ko wani garin ko kasar"

"To ai gashinan nanma Allah ya dubi zuciyar ka. Mu zamu koma, don kada nayi fada nasan shine da kansa yasa aka sayo komai aka jeren Kai Alhaji"

"Okay bai gaya miki ba?"

"Bai fada ba.kila kayan sawarmuma Kai mana zeyi can din. Hahah ya hutassheni ma ai. Allah na tuba ba hanawa zanyi ba. Tunda dai ni zan zauna aciki da iyalina"

Marwaan yayi murmushi kawai kansan a kasa,

"Kaci abinci?"

"Eh"

"Toh mashaa Allah"

Suna dai ta zaune suna hira jefi jefi. Har maaikatan suka kammala jera kaya aka wanke gidah aka tsaftace koina. Maaikatan suka tafi da motocin su.

Alhaji sambaso ma ya fita... Bai dawo ba har bayan wajen biyu na dar, ranar ma a dakinsa na kasa ya kwana bai bari sun hadu da Dr bintu ba ma ya sake fita

Akan kawo manyan talabijin kayan kallo da sauran su aka jera. Dr bintu dai nata murna tana hasaso yadda zatai recording ta turawa kawayen ta an gyara mata gida sabo.

Bayan anyi ishai abadan. Sai ga motoci har da jiniyar yan sanda sun shigo gidan. Ta daga labule tana lekawa. Ganin Mata na fitowa daga cikin moticin

Ta dafe kirji tana ware idanu tace,

"Alhaji daurawa marwaan aure yayi batare da masaniyar sa ba"

Sauka kasan tayi da sauri jikinta na rawa. Lily dake parlor tabi bayanta

Ai kafin su fita ma. Tuni matan sun shiga cikin parlorn suna sallama.

Suka koma ciki ta tsaya a tsaye ta kasa zaune,

Gaysheta sukayi ta amsa tana duban su da kallon karin bayani.

"Yar uwar ki ce muka kawo"

"Yar uwa wata iri Kuma?"

"Abokiyar zaman ki"

Dariya ta fashe da ita tana tafa hannuwa,

"Abokiyar zama wace iri? Oh ko makociya ce aka kawo mu gaysa?"

"Abokiyar ki zaman ki dai a matsayin na uwargidah, Kuma yaya awajenta yanzu. Mukace bari mu fara kawota ku gaysa ki sa mata albarka"

"Bayan Allah batan hanya ko ince gidah kukai banan bane gaskia. Ko gidan su izzu ne nan naga ana biki kaman" lily ta fada tana duban mahaifiyarta ta

"Nan ne dai.. Ba nanne gidan Alhaji yusufa sambaso ba?"

"Eh" lily ya amsa

"Marwaan aka daurawa aure?" Dr bintu ta fada tana kokarin bude lafffayar amaryar

"Waye haka?.oh ko dan sa? A'ah! shi kansan dai arzikin ya fada. Mai gidan naki ne dai ya karo aure. "

Hannun Dr bintu na na rawa ta yaye fuskar laffayar amaryar..

Wa zata gani? Kubra kawarta kuma aminiyar ta datasan kowane sirrinta ce sanye cikin laffayar ta saddaa kanta. Kamshi sai tashi yake daga jikinta. Kanta an yarfa mata kananun kitso ya fito ta gaba.. Yayinda hannunta da kafafuwanta sun sha lalle maroon da black

"Kubrahhhhh?"

Dr bintu ta fada a razane. Ta sulale ta sume a wajen.... Tana bude idanu ta ganta a asibiti marwaan da lily akanta......

Ta Kalli gefe an rubuta a bango 'Emergency unit... Amenity annex'


...

https://t.me/BlumCryptoBot/app?startapp=ref_7XYZOnMEWU

Kuzo ta fashe da mu a Blum🥳🥳🥳 ga link nan. Allah yasa my dace Amin
.








ATUWAA🧕

_K'K'J_
_(M/W/S)_


_BOOK TWO_


_✍️:MX_


_40_


:::::::::




"Maa kin farfado? Alhamdulillah" marwaan ya fada yana murmushi

"Maa" lily ta rungumeta cike da jin dadin itama

Dr bintu ta daga hannu dakyar tana duban roban ruwa da yake shiga jikinta ana mata kari.

Hawaye suka shiga wanke mata fuska. Tana kokarin tashi daga kwancen da take ta kasa ..

"Karki tashi maa.. ki dakata tukun"

"Meya faru da ni....duk mafarki nake ko?.

Marwaan ya girgiza kansa yana duban lily yace,

"Ba mafarki bane maa. Amma dai dagaske bakida lafiya doguwar suma kikai.Alhamdulillah Kuma kin farfado"

"Yanzu yusuf yayi aure? Yusuf ya auri kubrah? Kubrah fa aminiyata innalillahi Wa inna ilaihi rajiun"

Lily zubar da hawaye takeyi takasa cewa komai sai marwaan ne mai samun kwarin gwiwar amsa mata.

"Kiyi hakuri maa kinga bakida lafiya kinji? Karki saka hakan a ranki. "

Dr bintu ta barke da hawaye sosai harda shessheka tamkar karamar yarinya

"Yanzu Ina yusuf din?"

Marwaan ya sosa keyarsa yana datse harshe bai ce komai ba

"Ba kuce komai ba yana Ina yusuf din?"

"Maa yana gidah"

"Bai zo ba?"

Suka gyada mata Kai a tare. Wasu siraraan hawaye ne suka zurara daga idanunta. Ta Saka hannu ta share hawayen tana mayar da kanta gefe tace,

"Waya kawo ni asibitin?"

"Ni da lily"

"Lalle.... Humm yusuf kenan. Kubrah Allah ya Saka mun"

"Ma wannan dai aunty kubrah din?"

"Itadai"

"Subhan'Allah"

"Auren cin amana..kema maa kin yarda da mutane. Matar nan komai tasani . Ashe Ashe" lily ta fada tana gyara zamanta akan kujera dake kallon gadon marasa lafiyar da Dr bintu ke Kai. Yayinda marwan ke a tsaye.

"Rashin sani mana, kubrah taci amanata. Yusuf yaci amanata. Allah kana gani" cewar dr bintu

Haka dai sukayita bata hakuri ... Ruwan da aka sanyaa mata ya kare. Aka mata allurori suka Kuma bata magunguna.

Gidah marwan ya mayar da su. Suka taimakawa mahaifiyar tasu suka shigar da ita sashen ta. Kasancewar dare ne.

Wanka tayi kawai ta kwanta akan gado tanata juyi. Hawaye nata zuba daga idanunta. Ta dakko wayarta tana duban chatting dinsu da kawartata da tazama kishiyarta wato hajia kubraa. Duk matsalolin Mai gidan nata take gaya Mata da yadda zaa shawo kansa awajen bokan su ya sake barke Mata bakin aljihu...

Mikewa tayi dakyar ta leka window ta saman ta hango dayan gidan da kubran take da Alhaji Sambaso. Ko'ina yayi dau da hasken shima. Idanunta ta runtse alokacin data ga an saki labulen dakin datake hango window.

"Shikenan yusuf zai kwana da wadda bani ba? Kubra aminiyata zata kwana daki daya da miji na uban yaya na? Innalillahi Wa inna ilajir rajiun"

Ranar dai haka tayita zulumi tana koke koke tana surutai. Bacci barawo ne ya sacheta

Haka yaran nata ma lamarin ya dame su sosai musanman marwaan da dama yana dauke da tarin damuwa kala kala....


*******


Ganin shiru shiru har dare yaja ainun ba wata tsayayyiyar magana yasa bappah Auwalu dake zaune akan kujera ya dubi nusaiba tana kusa dashi duk tayi tsuru tsuru,

"Nusaiba.. tun dazu ta bakin ki muke jira fa fisabillahi"

"Tace mu saurara."

"Tun dazu kika cewa tace mu saurara tun safe. Haba Dan Allah. Menene matsayar gwara mu saki "

Nusaiba ta latsa wayar hannunta ganin yadda lokaci yaja ainun ta nunfasa tace,

"Auwalu tafiyar nan Ina tunanin ba yanzu bane sai nan gaba"

Bangane ba"

"Eh yadda na fada dai hakan take. "

'meye manufar hakan. Meyasa sai gaba wani abun ne?"

"Haka dai tacemun...don haka sai mu mayar da kayayyakin mu ma'ajiya. Su Kuma baqi su koma inda suka fito"

Nawraah tayi murmushi Jin karashen zancen nusaiba. Sarai tana sane da su take. Don haka tace,

"Aunty muma dama ba zama zamuyi ba. Yanzu tunda dare bai ja ba zamu koma namu gidan"

Nusaiba ta kece da dariya tana tafa hannuwa,

"Naku gidan? Sannu masu gidah kice dai gidan marayun da kike a tsakure. Amman gidah ai gashinan ya tashi daga naku mallakin na wasu ne"

"Nusaiba meye haka. Zan mugun saba maki. Ai dama tun baa je ko'ina ba halayen naki basu sauya ba? Yaran nan yaushe rabon da ki gansu? Yaushe kika taba takawa kika je inda suke. Nan gidan mahaifin suke? Uba nake awajen su. Amma saboda kwakwazo da kiyayyar da kike musu da tsangwama da kyara shysa ko suzo su wuni basayi.kiji tsoron Allah nusaiba. Wallahi"

Nawraah tayi murmushi. Hannunta rike dana Amnah tana lankwasa yan yatsun . Yayinda ashfeef na daga gefe a zaune shima.

Tache,

"Bappah kayi hakuri . Tabbas munyi kuskure da bama zuwa mu ziyarci ka da yan uwa kasancewar ka mahaifinmu. Domin Kai ma uba ne. Ko da abbiey yana nan. Da Kai da yaran ka ba abunda kuka mana na nuna rashin son zaman mu a tare ko hana abinci da sauran su. Duk kunyi bakin kokarin ku. Musanman bappa da kake yawan zuwa kana ganin mu a gidan marayun . Mungode sosai bappah, Yaya Ahmadu Ma idan yaso wajen hamma ashfeef Muna zuwa mu gaysa. ..."

"Idan Kun fita, ku turo kofar sauro wallahi"

Nawraah da nusaiba ta kaita makura duk hakurin da takeda shi . Yau dai tace bara ta mayar mata,

"Aunty kenan..wallahil Azim koroko kike kina kuka jina jina mu dawo nan gidan wallahi ba zamu dawo ba. Ai nan ba gidah bane. Gidah shine inda ake samun nutsuwa da kwanciyar hankali , ahada karfi da karfe atare.. Gidah shine Wanda ba zaa hanaka abinci ba, ba zaa maka wulakanci ba... Gidah shine inda zaka huta. Cikin yanayin da kake a lullube na bakin ciki da damuwa sai an yaye maka shi,gidah rufin asiri ne . Gidah marayu gidan mu ne, lamba daya kuwa, domin sunfi wadanda muka hadu dasu ta zumunta, Sannan alummar da ke cikinsa da yardar Allah Allah zai amince mana da su baki daya. ..wannan har gidah ne da kike tunkaho da shi?"

Sai ga nusaiba ta daka tsallen albarka,

"Okay Auwalu kana jinta ko?.to gashinan tana rena maka gidan..ah lalle wuyan ki yayi karfi.wato yan kujerun nan namu da katifu da sauran kayan kitchen a takaice wannan kango ne, ah lalle. Wuyan ki ya isa yanka. "

"Tabbas nan ba gidah bane anty. Ai kaje gidan da ake maraba da Kai shine gidah Koda kuwa ba shida komai na more rayuwa, ko da kuwa kullum dusa ake ciki, Amman zaa tarbe ka da so da kauna, nanne gidah . Ba karamin abubuwa ne ke sanyawa hakan ba. Gidan da zaka je a karbe ka hannu biyu..na ciki da suka rigaka shiga su karbe ka kamar dan uwan su. A tare an zama daya. Ga wajen kwana ishasshe. Ga hadi da kayan kallo ga abuncii har sai mun ture kullu yaumin. Abubuwa dayawa dai wannan gidan ya zamar mana Kuma mun samu hanyar arziki sosai acikin sa. Bamu kadai ba harda wasu.. Alhamdulillahi. Nan Kam anty ba gidah bane. Gidan ba aso kazo. Gidan da aka baka daki daya da tumaki da akurkiin kaji. Gidan da inde baka nemo ba ka kawo ba zakaci abinci ba, gidan da ruwan sha ma saii ka roka. Wanka kuwa sai dai kayi a awaje. Kai wasu abubuwan ma ba zasu fadu ba. Amman tabbas fita zamuyi mu mu tafi gidan mu. Inda ake son mu da kaunar mu ana farin ciki kasancewa damu. Har gaban abadan bazan dai na fariin ciki ba akan kasancewar mu ni da yan uwana acikin gidan marayun. Saboda gidan marayun ya zamar mana riga da zani harda danwali, Gidan marayu ba yunwa. Ciwon Kai kake sai an baka magani kasha. A Kuma kula da Kai. Duk abunda muke so bamu rasa ba banda na iyaye. Ku. Bayaga haka Alhamdulillah mun samu sauyin rayuwa bayan rasuwar mahaifan mu kala kala. Wanda ya zamar mana tarihi Mai dauke da mamaki. Bakomai bane fyacr cikinsa shine mutanen da basa yi dakai sai da ran mahaifan ka. Hahahaha duk anyi walkiya mun gansu Kuma da saura. Suma Allah bazai bar su ba. Akwai Wanda ma daman kaman jiran yake iyayen mu su rasu saboda mu shiga ha'ula'in rayuwa.... Sai yanzu na tabbatar Dan uwa ba wai shine jinin ka da kuka hada jinin zumunta ba, Dan uwa shine Wanda zai daukeka ya rikeka tamkar Kai din jinin sa ne, Baku hada komai dashi ha. Amman har yafi Dan uwan ka na jini zumunta.

To ki cigaba da shararawa a gidan ki. Mu ba zama zamuyi miki agidah ba. Mun daina zama inuwa daya da makiyan mu. Gidah dai naki ne sai yadda kikai da shi. Ko akukurkin kaji da kika bamu a baya muka zauna, kada ki manta mu ma mahaifin mu ne ya baki. Sannan abubuwa nawa suka miki na rufin asiri aunty...?"

"Auwalu kana ji kayi shiru ko?"

Bappah Auwalu ya tafa hannuwan sa yana kauda Kai yace,

"Me zance mata?. Yo ai duk abubuwan da ta fada babu na karya aciki nusaiba. Sannan da fari ke kika dakko zancen ma. Na meye naki kina babba zaki fada musu haka? Wani lokacin mantawa kike ne yayan yan uwan na ne?.sannan ko mantawa kike gidan nan dai nawa ne ba naki ba. Amman idanun ki sun rufe sai magana kike, Wallahi summa tallahi kece kika bangaro nusaiba.... Tun suna kankana kike zubar fada agaban su, taci ta cikata yau ta amayar, A wannan daren zasu fita su koma ?.kamar wadda batada Yaya ba kisan ciwon kan Yaya ba. Ko da yake naki gasunan a kusa suyi fitsari su kwanta yan gidah ne. "

"Yo Allah na tuba daman ai haka nasan zaka fada Auwalu. Ai yayan da basalefi ne shafaffu damai. Baka goyan bayan kowa inde akan sune. "

Nawraah har ta Kai bakin kofa sai ta juya idanuwanta na hawaye tache,

"Anty kenan. Wallahi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login