Showing 93001 words to 96000 words out of 144575 words

Chapter 32 - GIDAN AUNTY BOOK 1 cmpt by Mss Lee

miss lee   

28 Jun 2024

32159

a jikinki, ina kukabar kanunfari!? Shima akwia abubuwa da mana da zakiyi wajan gyara jikin ki da abubuwa nagartattu basai kinje kin bata kanki ba ,please mata mu kula please yar kisisinar nan da rankwada da shagwaba a dungayi , dan honey =??, darling dinnan please , karki yarda waidan kina da  ya ya kice kin dena , da kun shiga daki maida kanki kamar yar baby=??, kar inji ana baban sani ko baban haruna, yan gidan aunty daku nake ,MAMAN SUDAIS kija musu kunne)sosai amzy ta cire kunya ta koyar da ita abubuwa da yawa, tsabar kunya kasa dago dakanta tahee tayi , ita kadai sai kuka take, amzy bata kulataba sai data bata kalubalan rayuwa, aure dan hakuri ne ,zomu zauna zo mu saba ba kullum ne ake kasancewa cikin farinciki ba. Ba ita ta kyaletaba sai wajan 2, bayan ta bata damar tayi sallah sannan aka kara sa mata wasu turarukan da zatayi Wanka dasu,TAHEE har yanxu bata dena kukan ba,tayi sallah tare da yin Wanka , wani Saban kukane ya kara zuwar mata , oummanta da taheer dinta duk sai da tayi musu addua sosai,uku daidai amzy tashigo dakin dauke da wata trolley me dan girma, wani brown din atanface me shegen kyau ba wani tarkacene a ciki ba simple dinki akayi amma sosai fadin yanda ya hadu bata lokaci ne, stone din jikin kayan sai faman walwali suke takalmi da da pose duk saida ta fito mata dashi da mayafinta, shiryawa tahee tayi cikin kayan bakaramun kyau sukai mata a jiki ba kamar a jikinta aka dinka su,sai da ta bari akai kiran sallar la asar sannan tayi mata simple makeup mata hanayina,  fatabarakallahu ahsanin khalikin, Allah yayi halitta awajan nan ,sai da na furta Masha Allah, Masha Allah , Masha Allah, Iya kyau da haduwa ta hadu, tayi kyaun da yafi Akirata da zinariya , daya tamkar dubu ko makiyi ya ganta sai ya kara kallanta balantana masoyinta,abun hannun da king yasa mata sai faman kyalkyali yake , stones din jikin kayan ma sai ya kara kawata kwalliyarta, daura mata dan kwalin amzy tayi amma ta boye mata gashin kanta sai wanda suka kwanta a gangan goshinta, farar kyakkyawar fuskarta sosai ya fito cikin daurin bakinta sai faman sheki yake, takalmin da amzy ta dakko mata me dan tsini ne kadan,hatta da bracelets din daka saka mata masu walwaline,sai pose din data mika mata tana yafa mata mayafi, ita kanta amzy tana shiryata tana sakin murmushi me kayatarwa tabbas kyan da ake cewa akwai kyau tabbas akwai kyaun ,waje ta samu ta zaunar da ita akan gadon ka fun ta fita daga dakin, Daidai inda ta zauna din taji dan tudu a wajan , tana dubawa wayarsa ta jiya ta gani a wajan da Sauri ta saka ta cikin pose din gudun kar wani ya shigo dakin,amzy ce ta dawo dauke da kayan daukar hoto sosai ta ke dauka tahee ,zaman da tayi akan gadon sai ya kara kayata wajan kasantuwar bedsheet din gadon me design din brown ne , suna cikin saukar hoton mahma ta shigo ita da small mom, gabaki d aya sakin baki sukai suna kallan ikon Allah,In banda tubarkalla Masha Allah babu abunda bakinsu ke furtawa, gabaki dayan su sun kasa kwakkwaran motsi, mahma ce tayi karfin furta  tubarkalla Masha Allah  a fili,  daughter wannan kyan naki ya wuce akira ki da kyakkyawa sai dai shugaban kyawawa , har na rasa tsakanin keda mijin naki wanene ya fi kyau, a maimakon su fito da amarya kamar yanda akace sai suka tsaya koda ta , gabaki dayan su photograper suka zama sai faman daukan ta hoto suke , saura kadan ta fashe da kuka, tun snap din da amzy tayi Mata tasaka a status dinta , cikin mintuna da basu fi goma ba sama da mutane dari sai da sukai mata magana harda Wanda basa kulata , HIS QUEEN shine kadai abunda ta rubuta a jiki amma zonaga comment, zata kara posting mahma ta hana ta sabida tasan in king yagani baruwanshi zaiyi maganintane, da sauri kuwa ta cire tana sakin dariya ko ba komai kusan mutane ashirin sun yi booking dinta acikin mintuna da be wuce goma ba, tabbas zuwan ta gidan alkairi ne,mikar da amarya suka tare da gyara mata mayafin kanta, abun hannunta ne ya sauka a kan hannun tahee , zaro idanuwa waje tayi tana sakin dariya  Diamond heart love  , ta furta kasan zuciyarta, iya hasashenta ta kasa hasasho a dadin kudin sa Sabida yanda yake walwali zai tabbatar maka da asalin zallan diamond akayi shi. Har za a sanar da fitowar amarya mahma ta hana acewarta angone zai fara ganin kwalliyar, gabaki d aya fita sukai akabar small mom gudun kar Wanda ya shigo dakin, mahma kuwa kai tsaye part din king ta nufa, bin falon na shigayi da kallo dan gabaki d aya an canza komai na cikin falon komai nacikin falon sabone, kallan sha aban dake cikin shigar manyan kaya fara kaldasu tayi, yana ina  ta furta , fusgar da iskar bakinsa yayi mahma tun dazu nake kiransa amma yaki jina yayi wuce warsa sama wai bacci zaiyi , mahma batace komai ba sai wayar ta da ta dauka cikin dan baci bacin rai take kokarin dialing din number din sa, wani irin sahirtaccen kamshin turaransane ya daki hancinta, da sauri ta daga idanuwanta tana binsa da kallo, gabaki dayansu daga ita har sha aban sakin baki sukai suna binsa da kallon kurulla, yayi bala in kyaun da baki bazai iya kiyas ta kyan da yayi ba, sanye yake cikin wasu hadaddan ubansun shadda, light brown meshegen kyau da tsada kallo daya zaka mata kasan ba karamun kudi aka kashe mata ba, dinkin zamani ne ajikin rigar hatta babbar rigar dake jikinsa, kafarsa sanye take cikin wani half qucci dark brown kafarsa fara suwal sosai ta bayyana a cikin takalmin, fararan hannunsa ma sanye yake cikin diamond wuce me shegen tsada da zoben sa , dayan hannun kuma wasu siraran abun hannun diamond a jiki, dayan kusan kullum yana hannunsa Wanda ya fi kyallin cikine kawai yafi daukar idona, fuskarshi babu ko digon murmushi kawai amma ba kadan ta fito da zallan kyansa na larabawa ba, pink lips dinsa sosai ya turo ga gashinn idanuwansa da suka kara fito da fararan idanuwansa,hatta gashin kansa gyaran da ya sha nadaban ne sabida yanda hular kansa ta fito da adon gashinsa, a hankali yake taka stairs din sai ji yayi ana snapping dinsa , dago idan da zaiyi ba sha aban kadai ba hatta mahma snapping dinsa take, tunda aka haifeshi zata iya rantsewa bata taba ganin kyawun da ta hango awajan saba kamar yau, dukda kasancewar sa kyakkyawa ne shi na karshen karshen, dan hararan sha aban yayi yana kara tsuke fuskarsa kafun ya kalli mahma dake faman sakin murmushi son na kasa ganewa da kai da ita wanene yafi wani haduwa,kamar hadin baki ,Anya bazan fara kishi ba  ta karasa cikin Zolaya, dan kauna kansa yayi batare da yace komai ba, wani shegiyar dariyar iskanci sha aban ya saka da har saida mahma da kai masa duka, hanyar fita king ya nufa kallansa mahma tayi ina zuwa,batare da ya kalleta ba ya furta  office , da sauri ta kallesa  office, wasa kake ko , dan wallahi yau duk wani miskilancin ka bazan dauka ba , yanxu maza ka wuce kai muke jira ka fito da amarya, nan da mintuna biyar nakeso a fito da ita inva haka ba ran kowa sai ya baci ta karasa da nuna sha aban  Kai ma wuce ka tafi wajan taron  da sauri kuwa ya wuce yana dariyar dramarta da king, ganin tana kokarin juyawa yasashi riko hannunta, harara ta sakar masa zata wuce ya rungumeta  am sorry, I will do everything to make you happy wani murmushi ne ya subuce mata raba jikin ta tayi da nasa tana shafa gefan fuskarsa  please kazo in not less than 5 minutes dan Allah  lumshe mata ido yayi alamar toh, ta gane me yake nufi shiyasa ta juya ta far part din, amaimakon ya biyo bayansu sai ya shiga wani dakin da tahee ta taba zama dashima komai na ciki sai da aka canza masa, dan wani bottom ya danna da komai ganin ka bazaka san dashi ba, yana dannawa kuma wardrobe din wajan ta rabe biyu yana shiga ya kulle taci , ta wajan kuma wai ta dawo yanda take kamar babu wani makamancin abu a wajan, tafiya yayi me dan tazara kadan kafun ya iso wasu kofofi a wajn, kofar biyun karshe ya nufa, yana bude kofar abun mamaki sai gashi a part din dada, a bun frame din dake wajan ya taba take awajan kofar ta kulle ya dawo ainahin jikin bangon,yana dan jin hayaniyar mutanan gidan kadan kadan, dan tafiya yayi kadan batare da kowa ya gansa ba , kofar dakin da take ya kalla kusan second biyu kafun ya murda ya shiga dakin da sallama, sallamar sa daddadan kamshin sane ya ziyarceta da sauri ta daga manyan idanuwanta, take a wajan ya sauka cikin nasa idanuwan dake binta da wani irin kallon dashi kadai yasan ma anarsu, yanda ya jingida da jikin bangon dakin ta kalla , itama a wannan karan ta kasa dauke kallanta daga garesa, cikin takun kasaita ya nufota da tun lokacin da ta kallesa bugawa zuciyarta ya tsananta, gefen inda take ya zauna tare da dora kanta akan kafadunsa cikin rada rada ya furta fatabarakallahu ahsanin khalikin ,daga nan be kara cewa komai ba sai sauraran zuciyoyin su da suke yi na tsawan mintuna biyar itama tana lafe kwance kan kafadunsa, knocking kofar akai saudaya kafun suji saukar muryar Mahma zaku iya fitowa yanxu tana kammala zancanta , suka farajin takun takalmin ta alamar ta bar wajan, kusan mintuna biyu kafun ya mike tare da ita a cikinsa yana nufar kofar fita da ita da sauri ta kwace jikinta tana zaro masa ido , idanun cike da kalla harda dan turo karamin bakinta,kallan bakin yayi kafin ya kalleta  bakin nan da kike yawan turo Munsu xanyi maganinki and in baki dena ba yanxu ba gobe ba zan karbesu kamar yanda kika so ai damugun sauri ta mayar da lips dinta tana sunkuyar da kanta, be kara bata damar magana ba ya janyota ajikinsa tare da tura dakin, sai da ya kara janyo gelenta kadan ya tabbatar ya rufe mata ciki kafun su karaso kofar da kowa ke zaune anzuba mata ido ana jiran fitowarsu, gefensu wasu matane guda hudu ko wanne da damin fulawa a hannunsa,suna jin alamun taba kofa aka kashe gabaki daya light din wajan sai ta wajan kofa da aka bari masu walwali,ana bude kofar zo kuga yadda zuciyoyin mutane ya dunga tsunkewa take a wajan aka fara musu watsin flowers masu kyau kafun wutar wajan ta dawo gabaki d aya , gabaki d aya mutanan wajan zuba musu ido sukai ga wata irin dum waka dake tashi kadan dan ,kowa ya rasa abun cewa basma da ke kokarin dago kai sai gashi tayi saurin maida kanta , amrah ma bakadan ba tayi nadamar zuwa wajan har idanuwanta suka sauka akansa, yanda ya rike ta sai ka dauka wayanda suka dade da shiga gogin soyayya bakaramun matching sukai ba , me daukar hoto sai faman taukansu yake , yanda take faman kashe idone alamun hasken ya mata yawa be san lokacin daya kwantar da Kanta kan kirjinsa ba ,gabaki d aya mutanan falon kara sakin baki sukai suna kallan ikon Allah , Kai tsaye wajan dada suka nufa , tana ganinsu ta saki kuka me taba rai oh ni yasu , Allah nagode maka adduar tsawan ran da nadungayi yau ta cika burina ya cika naganin Auran tahanuni, tunda Allah ya dauke ran mahmuda, Allah ka basu zaman lapiya me dorewa ta karasa zancanta tana goge hawayanta, wani dan madaidaicin box dada ta dakko tare da daurawa tahee a tafukan hannunta wannan kyauta ce na baki sabida yanda kike sani farin ciki tahura ta karki ji komai duk lokacin da ya bata miki rai ki sanar dani zanyi maganinsa kuka tahee ta fashe dashi me rasa zuciya ko magana ta kasa yi,a hankali sautin kukanta ke tashi kadan kadan, daga wajan dada wajan ummey aka nufa dake share hawayan farinciki yau Allah ya nuna mata bikin d anta da take mararin gani har cikin zuciyarta , itama nasihar tayi musu kafun ta bawa tahee kyautar diamonds set tundaga kan sarka , dan kunne , zobe da abun hannu bayanshi kuma ta bata kyautar manyan Lamborghini sababbin yayi gudu biyu ,guda gabaki d aya aka saka afalon dukda dayawa mutanan wajan ba haka suka soba , da aka zo kan ammey kuwa kuka ta fashe dashi daya taba ran kowa ga tahee da take kuka kasa kasa itama , da kyar aka samu tayi shiru itama nasiha tayi musu kafun tayi musu kyautar diamond itama da babban mall dinta dake Lagos, kowa yaji dadin yanda ta hadasu musamman yanda ta raini king amatsayin d anta tun yana karami,gabaki d aya iyayan falon kowa kyautar da daga gold sai kyautar motoci da company da take samu , wannan abu shi ya kara bakatawa amrah da basma rai kowa yana ganin da ace babu tahee da shine zai samu wannan kyautar. Part din abeey aka suka nufa mahma na take musu baya, yanda ya gansu ba karamun farinciki yasa shiba daya kasa boyuwa akan fuskarsa, shima sosai yayi musu nasiha ne ratsa jiki akan zaman aure, yana kammala yi musu kuma ya basu kyaututttuka masu girman gaske , d aya daga cikin jirgin NAHYAN sukutum ya mallakawa tahee,wani saban kuka tahee tasaka masu, kama hannunta mahma tayi batare da ta bari tace komai ba ta nufa da ita dakin da su ummey suke ciki daga ummey sea small mom, anyi anyi da ammey tazo taki zuwa acewarta sune iyayanta ai, sosai suka zaunar da ita sukai mata nasiha me ratsa jijiyoyin jiki da tsoka ko wannansu saida ya rungumeta tare da lallashinta kafun abar mahma ita kadai sai amzy da aka kara kira , wani wanka suka sata ta sake yi kafun su shirya ta cikin Wani Dan ubansun lace meshegen kyau red colour , shigarta ta ynxu harta taka wanda aka yi mata dazu kyau da haduwa, wani abu amzy ta bata Tasha kafun akara kyarata, suna kama gyarata kuwa aka dakko wata lapaya red itama aka nada mata a jiki( oh oh oh ni miss lee, ni kaina saida kyawun ta ya tafi dani).


A bangaran king kuwa Suna fita abeey ya rungumeshi , yana sauke a jiyar zuciya ba  addua ta daya kullum naga auranka tun bayan rasuwar Mohammad, amma Allah baiyi ba sai yanxu , na rokeka ba danni badan na isa da kai ba , ka kula da maraicin yarinyar nan , tana bukatar kulawa ta musamman ko dan irin kaddarar rayuwar da ta fuskanci kanta a ciki, idan kamun hakan ka gama yi mun komai arayuwata, Allah yayi maka albarka yanda ka faranta mun Allah ya baka masu faranta maka kaima  , lumshe idanuwansa king yayi yanajin kalaman mahaifinsa har cikin zuciyarsa,har yanxu yana tuna kalaman nan akhie , idan Allah yasa ban ga auranka ba inaso ka zama da happiness man , ranar auranka,duk matar da aka zaba maka ka karbeta hannu biyu kasota kamar yanda kake san mu , kara lumshe idanuwansa yayi tuno Wannan kalaman daka wajan mutumin da har yau bazai taba mantawa dashi ba, besan lokacin da bakinsa ya furta  I promise you , I will always be what you wanted me to be , kara rungumeshi abeey yayi tsam a jikinsa kafun ya raba jikinsu, dan Allah abeey king yayi  abeey ni baka bani kyautar jirgin ba  ai , dan bugunshi abeey yayi  Wanda kake dasu ya isheka, maza tashi kabar mun daki , wani gajeran murmushi king ya saki da ya fito da zallan kyawun da Allah yayi masa ,ban taba ganin wanda ko be yi murmushi ba yana kyau balantana ya gwada koda motsa lips dinsa ne, sallama yayi wa abeey kafun ya bar part din, koda suka hadu da sha aban sai faman tsiya yake masa, saida ya dawo masa asalin king dinsa kafin ya kyalesa.


('('('('

Karfe 8:20 pm mahma da small mom suka dauki tahee zuwa dakinta na aure bayan nasihohin da jan hankalin da akai mata,kasa mikewa tahee tayi daga zaunan da take sai faman kukar da take Durza da ya haifar mata da zazzabi, mikar da ita small mom tayi kafun su nufi motar da aka bude musu, ba ayarda kowa ya bisuba,suna zuwa Daidai part din akasa tahee ta fitowa da kafar dama bakin ta dauke da bismilla,har suka shigo part din komai sai sun sa tayi bismilla cike da addua suka shiga part din, basu tsaya a falo ba suka hau step da ita, wani door suka bude Babban falo ne meshegen kyau a wajan, shima basu tsaya a wajan ba kai tsaye daya daga cikin bedrooms din aka kaita, ba bata lokaci su mahma suka sata yin wani saban wanka, tare da shirya ta, saida suka zo tafiya ne tasakar musu wani saban kukan , jikinta sai faman rawa yake sabida zazzabin da ya kamata,da kyar suka samu sukayi mata dabara suka gudu. Ganin saura ita kai yasa ta kara fashewa da wani saban kukan.

Kallan yanda take faman kuka yayi kafun ya karaso cikin dakin bakinsa dauke da sallama , kan gadon ya karasa tare da dagowa, jin an dagata yasa tayi saurin bude idanuwanta , kallan Wanda ya dagatan tayi kafun ta kara sunkuyar da kan nata tana fashewa da wani saban kukan, rungumeta yayi a jikinsa yana sauraran yanda take kukan,bayanta ya dan shafa kafun ya furta  it s ok don t cry , a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login