Showing 1 words to 3000 words out of 81012 words

Chapter 1 - KALBIM HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

16 Sep 2025

174

??ࡱ?>?? r ????????????? ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????o 0

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?Fs WordDocument????1?0Table????????`Data
???????????????????? P???KSKS?1??h???????rr????????? ??::::::::<$??Q*r??::????:{??{:?:{?::?? ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJTA`????TDefault Paragraph FontOJPJQJ^Jfi`????f Table Normal :V ?4?
l4?a? OJPJQJ^J(k`????(No List ?h$rC8V?_Z~??t?????Z?L? ? ?7^O]tg??N?Ƣv???.???6*^?j?*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
#Zafafabiyar


1
Bismillahir Rahmanirraheem

Ina rokon ALLAH Subhanahu wata'ala yanda zan fara littafin nan lafiya cikin aminci da yardarsa ya bani ikon kammalawa cikin kwanciyar hankali da nishadi tareda dacewa lfy Ni da yan uwana gabaki dayanmu.AMIN.

Dan Allah ku kasance masu uzuri idan an samu kuskure ko mantuwa da makamantansu,Thank you.


********
ZADEENs HEALTH CEN/SPEACIALIST,
WEDNESDAY 1:40Am
Tin kafin isowan motocinsu da suka tinakaro babbar gate din asibitin securities na asibitin suka taso kusan a tare suna wangale musu gate din cikin sauri sbd irin gudun da motocin Ahalin ZADEEN's din suka tinkaro dashi wanda duk wani ma'aikacinsu yasan idan ciwon motacin suka tinkaro asibitin to Hasken idaniyar ahalin ce ba lafiya wadda kullum take cikin ciwo.

Sauran securities din da basu qaraso bude kofar gate din ba kaf dinsu fitowa sukai suka tsatsaya a gate suna bin motocin guda uku da kallan girmamawa duk da tsakar dare ne tareda fatan Allah ya bata lafiya.

Motocin na gama shigewa aka rufe gate din tareda taresa sbd babu wanda yake shiga ta wannan gate din a qaidarsa sai masu asibitin wanda kusan koyaushe suna hanyar zuwanta.

Kafin suyi parking likitoci uku da nurses biyu suka fito ta private kofar da zata kaika kai tsaye zuwa Vip room din dayake sama gaba daya.

A tare duka kofofin motocin suka bude kusan a tare duka suke fitowa babu wanda baa cikin kayan baccinsa yake ba sai DZAD(Dad Zad) wanda shine asalin Zadeens din a yanzu da babu kakansu kuma shine mahaifin marar lafiyar tasu sanye yake da jallabiya da qatuwar rigar sanyi ash sai hula sbd idan ciwon 'yar dayake gani a matsayin tasa bugawar zuciyar ya tashi saukowa yakeyi gaba daya daga billionaire din da ganinsa ma yake wuya ya koma kaman asalin uban da bayada komai agajin gaske yake nema a gurin Allah.

Gadon da aka tura ta dashi ne komai nata a rufe ko fuskanta baa gani sbd kwata kwata basa bari ana ganinta sosai sai iya likitocin dake kulawa da ita sa ciwonta ne kadai suka san kamanninta sbd tsaro da tsananin rashin wasa da duk abinda ya shafeta.

Suna wucewa ciki sauran familys din suka musu baya babu wanda zuciyarsa bata harbawa da damuwa,

A daidai irin wannan yanayin ne ko lokacin idan suna cikinsa babu abinda bazasu iya kawarwa ba dan biyan buqatansu dan kuwa mantawa suke da komai da kowa sbd JANNAH.

Securities din ZADEEN's dinne da suka iso asibitin ba tareda kayan securities dinsu a jiki ba sbd basa son asan akwai wani me mahimmanci a asibitin suka zagaye private kofar har ciki batareda alamar da zata nuna securities ne su ba.

A sama kuwa suna isa aka shige da ita inda iya doctors dinne zasu shiga familyn kuwa a nan wani wadataccen palon jira dayake a tsare suka zazzauna cikin yanayi mara dadi wasunsu kuma a tsaye suna kaida kawo cikin rashin sauti ko kadan sbd rashin dadin zuciya.


Mimi data fisu karfin zuciya akan lamarin Jannah din koyaushe itace ta dago idanuwanta da sukai laushi ta kalli Dzad wanda shima juyowa yayi ya kalleta da idanuwansa da sukai jajir kafin ya sauke ajiyar zuciya ahankali yana hade hannuwansa biyu sbd sanyin dayake ratsasa ko zai rage masa wanda kai tsaye zuciyarsa yake jin kaman yana zuwa zai masa illa sbd a wannan lokacin komai zai iya zama ajalinsa dan komai nasa yana gab da mutuwa idan har wani abu ya samu Jannah.

Hannu Mimi ta miqa duka biyu ta dora akan nasa hannuwan tana rufe masa su tareda bude baki cikin tsananin karfin hali da jarumtar da su suke rasawa tace,

"Insha Allah wannan karan zaa dace da zuciyar da zatai mata,
Zaa dace,Jan Zata rayu kaman kowacce 'ya insha Allah,
Jan zata zama kaman kowanne dan adam,zatai karatu me zurfi ta zama abinda kakeson ta zama insha Allah....

Rawa muryanta tafara yi karfin zuciyarta na neman karyewa dan haka tai shiru tana damqe hannuwan Dad din da dan karfi tana qasa da idanuwanta dake neman cikowa da hawaye.

Dzat din sake kame hannuwanta yayi da nasa yana kasa cewa komai dan irin hakan baya magana kowa ya sani.

Anny matar yayan jannah din wadda ke tsaye gefen mijinta MAHIR ZADEEN riqe da hannunsa tana kokarin kwantar masa da hankali tareda basa kwarin gwiwa dik da itama a sanyayen take sbd duk lokacinda zaa ce jannah ba lafiya a cikin matsanancin tashin hankali take duk da tasan ta riga ta tsira ta fita daga layin wainda zaa iya rabasu da zuciyar dake bugawa a kirjinsu sbd dubawa ko zata daidaita da wadda zata zaunu a kirjin wadda suke son nemowa zuciya kota halin yaya.

Baro gurin Mahir tayi ta dawo gefen Mimi tayi ta zauna ahankali tareda dafata ahankali tana furta mata kalaman kwantar da hankali da fatan ranar warakar jannah taxo.

Mahir zaunawa yayi shima yana dora kafarsa daya akan daya sbd sanyi da shima yake ratsashi wanda yakejin kamar fatar jikinsa ce ta bude kai tsaye sanyin na shigar masa kashi yana daskarar da jininsa gashi kayan bacci ne a jikinsa riga da wando masu tsananin taushi sbd tsadarsu sai jacket daya doro akai.

SALEEM ZADEEN wanda yake bin mahir kuwa kasa zama yayi sbd kansa dayake jin kaman yana motsi dan shi sam dan zafi ne baya da hakurin suspense irin wannan kansa yakejin kaman zai zare.

Shima riga da wando ne a jikinsa na bacci sedai shi hoodie jacket ce a jikinsa sai kai da kawo yakeyi yana kasa dago jajayen idanuwansa da suka sauya.

Kofar palon aka turo da sauri wadda ta saka dukkaninsu dagowa suna kallan Dr AMMAR ZADEEN wanda kai tsaye ya komar da kansa baya ne yayi karatun likitan Zuciya sbd Jannah kadai.

Idanuwansa da sukafi na kowannensu sauyawa ya dago ya kalli kowannensu kafin ya kalli dzat ya basa kwarin gwiwa ya juya ya fice zuwa dakin da jannah din take da doctors sbd shi biyawa yayi inda aka sanar dashi ana tinanin an samu donor kafin ya wuto nan shiyasa suka rigasa isowa.


Zaman kusan awa daya zuwa biyu sukai cikin tsananin daci da damuwar zuciya kafin Ammar ya fito ya shigo dakin yana sauke numfashi me tsananin zafi da huci ya qaraso ya zauna kujeran datake kallan su Dad din ya dago idanuwansa ya kalli dad.

Ajiyar zuciya me sanyi dad din ya sauke a natse yanajin hankalinsa na dawowa jikinsa take yaji dacin zuciyarsa ya ragu sbd yasan Ammar ko zuciya dubu jannah ke buqata zai nemosu ayita gwadawa har a samu wadda zatai daidai a saka mata kota halin yaya ba damuwarsu bane.

Mahir ma ganin hakan ya sauke ajiyar zuciya a boye kafin ya juya ya kalli Anny da kusan itama take ta fahimci akwai wani abin kenan da ido yai mata maganar ta fita da Mimi.

Ajiyar zuciya da numfashi itama ta sauke tareda dafa Mimin cikin kulawa da nuna tausayawa sosai da nutsuwa tace,

"Mimi muje mu duba Jannah din doctors din sun fito"

Dagowa Mimin tayi ta kalli Ammar wanda ya gyada mata kai alamar eh zasu iya zuwan,
Mahir ta kalla shima ya sakar mata murmushin karfin halin alamar insha Allah jannah yanzu zata samu sauki.

Miqewa tayi Anny tabi bayanta suka fice daga gurin Anny taja kofar ta rufe suka nufi dakin da jannah din take.

Suna ficewa Ammar ya sauke numfashi tareda dagowa ya kalli dzad dake jiran bayaninsa ya bude baki yace

"Ansamu donor wanda ta ko ina muke saka ran tayi....

Katsesa DadZad yayi da cewa

"Mene ake jira to?

Saleem da baida hakurin jiran komai batareda sanin abinda Ammar din zai fada ba ya matso gaban Ammar din kai tsaye yace

"Indai ansamu zuciyar da zataiwa Jan ko duka tawa dukiyar dana mallaka akeso zan bayar a karbo heart din ko a inane take kawai ka tabbatarda ka amsota Jan ta sameta"

Yana gama fadar haka ya juya ya nufi kofa ya fice zuwa dakinda jannah din take ya turo musu kofar da karfin daya saka dukkaninsu rintse idanuwansu banda Dad da bai motsaba har lokacin jiran sauran bayanin Ammar din yake wanda daman ba duka zance sukeyi da Saleem ba sbd zafinsa da rashin hakurinsa tareda rashin yadda da raayin kowa wani lokacin sai na kansa.

Ammar takardin dake cikin aljihun jacket dinsa ya fitar ya ajiye akan table din gabansu ya mayar da bayansa jikin kujeran dayake ya jingina yafara cewa

"Daya daga cikin asibitin da muka saka likitocinmu aka samo wadda zatai daidai insha Allah kuma kusan shekarunsu daya da Jannah din sedai matar Aure ce dan tanada tsohon ciki ma sedai batareda saninta ba likitocin sun duba zuciyar komai lafiya kalau."

Ajiyar zuciya me tattareda samun kwanciyar hankali mahir da dad din suka sauke lokaci daya sbd abinda kawai suke son ji kenan indai komai lafiya kuma ana tinanin zatai to sauran bayanin ba damuwarsu bane sbd sai sun rabata da wannan zuciyar datake bugawa a kirjin ta sun sakawa tasu yar batareda saninta ba sbd itace kusan ta numbar da bazasu iya kirgawa ba sai an cire aga bata daceba.

Dad din a natse yana komawa take Dzad dinsa ya gyara zamansa na asalin Me kudin dayake murza lokacinsa a yanzu ya kalli takardun batareda ya miqa hannunsa ya tabasu ba yace

"Kawai ku saka lokacinda zaayi aikin shine abinda yakeda mahimmanci amma sauran aikin ba buqatan damuwa,
Ku saka likitan datake gani acan asibitin gwamnatin ya turota nan asibitin batareda bata lokaci ba."

Mahir daya miqa hannu ya dauko takardun ya bude ya zubawa sunan dayake kai idanuwansa tsawon seconds ya duba bayananta da bai fahimci komai a cikinsu ba sbd tin daga sunan da garin datake babu wanda ko a cikin wani yare ya taba ji sbd ba anan suka tashi ba bare susan sunayen garuruwa duka bare qauyuka dayake ganin kamar dabbobine kadai suke iya rayuwa a cikinsu.

Jefa takardun yayi a kan table din kafin ya kalli dad din a natse yace

"Inaga zaifi tinda an samu wanda zatai din and she's preg abari ayi amfani da tsufan cikin da haihuwansa"

Kallansa Ammar yayi yana tinanin abinda yake fada wanda shi idan tasa zaa bi babu abinda zai tsaya jira bayan cirewa da sakawa Jan.

Dad shiru yayi batareda ya kalli kowannensu ba sbd maganar mahir din dan mahir shine kusan kamar me hangen lamuransu a duk lokacinda zaayi huldan business da irin wannan mummunar ta bayan fagen shine yake aunawa da hangowa ya fada yanda zaayi kuma hakan akeyi a dace sbd yanada ilimin nutsuwar fahimtar komai da mutane,
Hakama yanada wani irin ilimin dayafi duka familyn harshi dad din dan duk da dukkaninsu baa qasar suka taso ba sai yanzu ne da suka zabi dawowa gida sbd nemawa jannah kalbim.
#MAMUH
#ZAFAFABIYAR
#MASTERPIECE
#BESTSTORY
#BESTLOVE
#BESTROMANCE
#BILLIONAIRES WAR
#CRAZYLOVE
#ZADEENS
#LIMBAS



ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
_*KALBIM*_
_Mamuhgee_
#ZafafaBiyar

2
*ZUZEAMVENTURES*
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci? cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah >?p?=?L? Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k>?m? Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
=????=????=????=????=????=???? ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA? NEW PROMO YA KAMMALA=؃?
***********
Shiru dukkaninsu sukai daga dzad din har Ammar suna sake shiga nazarin maganar mahir wanda yake sake kokarin nazarta yanda zasu samu damar samun komai batareda wani damuwa ba dan shi sam baya yadda da damuwa ko tangarda a aikinsa shiyasa yake tamkar maye gurin nutsuwa ya hango ya hanga kafin ya fada.

Dzad duk abinda mahir ya fada yana kokarin bada damar abi hakan sbd yafi kaf yayansa nutsuwa da bin komai a tsare amma ayau yanajin kaman hakurinsa bazai barsa ya jira lokacin da mahir din yake fada ba sbd kada su rasa zuciyar wadda ake jiran kokuma idan gurin haihuwar ta rasu fa.?

Sun raba mutane da dama zuciyoyinsu sbd jannah amma babu wanda aka dace wanda ma basu san adadinsu ba ta boyayyar hanya
To ayanzu da suka samu bayan tsawon lokaci ana nema kuma a tsaya jiran wani haihuwar.

Mahir daya fahimci tinanin da Dad din yake sake bude baki yayi yace

"Jiran haihuwarta na nufin samun dama da dalilin rasuwarta ga mutane da yan uwanta shiyasa ana buqatan a jira lokacin haihuwan tayi sbd lokacin haihuwar ya matso sosai hakan ne zai saka komai ya tafi very neat tin daga cirewa da sakawan da rufe komai".

Ammar da zuciyarsa ke bugawa da sauri yana jin kansa na juyawa idanuwansa na ja jin yakeyi kaman bazai iya jiran lokacinba dan kuwa shi jinma yake kaman ya fizgo zuciyar a daren nan yazo ya sakawa Jan,
Shi a yanda yakejin yana zaucewa akan ciwon jannah duk mutanen dayake gani suna yawo zai iya ringa binsu yana fasa kirjinsu yana qwato zuciyoyinsu babu ruwansa da rayuwarsu indai jannah zata rayu.

Mahir ganin alaman Dad ya aminta da hakan ya sakasa kallan Ammar shi da Dad a tare sbd sanin shine mai juyewan kai idan wannan lamarin ya taso kwata kwata bayaji baya gani kawai abu daya ya sani shine karban kalbim kota waye ba ruwansa.

Dad ne ya bude baki a natse yace

"Ammar abari ayi hakan sbd tafiyar da komai batareda garaje ba ko dan ita jannah din hakama aikin nutsuwar da kwanciyar hankalin zaifi,
Tinda aka riga aka sameta duk inda zata shiga bazata gujewa abinda yake jiranta ba sbd yanzu zuciyar Jannah ce kai tsaye take bugawa a kirjinta babu abinda zai hana jannah mallakar wannan zuciyar me bugawa."

Numfashi me zafi da damuwa Ammar ya sake kafin yaji ya aminta da hakan dan haka zasu saka masu bibiyar yarinyar da bincike sosai akanta duk da babu ruwansu ba abinda ya shafesu da inda ta fito kokuma wace ita waye danginta.


******ASALIN LABARIN/SHEKARUN DA BAYA.

PROF ZAHARADDEN ZAADEN shine asalin mahaifin Yayansu uku biyu maza sai mace daya wadda yayunta mazan ke tsananin kauna sbd mahaifiyarsu ta rasu a hannun matar mahaifinsu suka taso,

Prof dan bokon gaske ne wanda ilimin bokon dana addinin suka shigesa sosai hakama yanada arziki sosai wanda ya dade sa barin qasar yana malaysia acan yake zaune da iyalinsa gabaki dayansu.

BOUKHAR Zadeen shine babba sai MAHMOUD Zadeen tukuna qanwarsu ZAYNEB,
Matar Mahaifin nasu bata taba haihuwa dashi ba dan haka su kadaine yayansa wanda suka girma kowannensu ya zama babban mutum,

A malaysia suka taso acan sukai karatu sai daga baya dukkaninsu su ukun suka dawo Nigeria tareda mahaifin nasu wansa tsufa yazo masa sosai.

Bayan tsawon shekaru Anyiwa Zeynab aure da wani prof itama a porthacort,

BOUKHAR da MAHMOUD kuwa kowannensu na qasa daban gurin karatu,

Mahmoud ya riga boukar aure kuma daga mahmoud din har zayneb babu wanda ya samu haihuwa a cikinsu har saida Boukhar yayi aure shine ya fara haihuwa a cikinsu.

Familyn ZADEEN's din sunada wani irin tarin arzikin dayake da yawan gaske da basuma san ya zasuyi dashi ba,

Bayan arzikin mahaifinsu prof me tarin yawa su kansu sun tara na kansu me yawan gaske dan kuwa ko Zaynab datake mace a cikinsu itama tanada nata arzikin sosai.

Suna tsananin son junansu wanda hakan ya saka iyalansu ma kansu yake a matiqar hade duk da su ukun gaba daya basa qasa daya.


Mahir shine babban dan Boukhar zadeen wanda ya haifesa a Greece,

Bayan haihuwar Boukhar Prof ya rasu wanda hakan ya saka dukkaninsu tattarowa suka dawo Nigeria.

Mahaifinsu nada kadarori sosai wanda bazasu iya gama hadasu lokaci daya ba dan haka mahmoud ne kadai ya koma boukar kuwa dole ya zauna Nigeria tareda iyalansa.

Umma matar mahaifinsu wadda ta riqesu tamkar yayan data haifa ba cuta ba cutarwa hannun Boukhar ta dawo dan yayansu ma basusan cewan ba itace ta haifi iyayensu ba sbd kulawa da kaunar dake tsakaninsu ta uwa da yayanta.

Mahir nada shekara biyar a duniya Zayneb ta samu ciki wanda yazo mata da matsala sosai sbd manyanci da dadewan datai bata haihun ba.

Cikinta na sake gaba girman matsalarta na qaruwa wanda daga baya aka gano tanada heart diseases wanda basu taba sani ba.

Hankalin familyn ya tashi sosai wanda ya sakasu dawowa da ita hannunsu aka fara neman mata lafiya.

Lokacinda aka gama bincike sosai akan ciwon nata aka gano tana buqatan heart transplant maana dashen zuciya.

Hankalinsu ya tashi sosai sbd ciwon nata bawai sbd zuciyar da zaa nema dinba sbd ganin sukeyi sunada dukiyar da zasu iya siyan mutum gaba dayansa su cire abinda sukeso a jikinsa.

Cikinta na kaiwa wata tara suka tattara gaba daya familyn suka koma Greece sbd haihuwarta da basa fatan matsala komai kankantarta.

Tin daga kan ummah da zayneb din da boukar da matarsa da mahir da mahmoud ma acan ya samesu da fmlynsa suka dawo zama.

Cs akaiwa zayneb aka ciro mata Baby boy wanda Boukhar ne ya saka masa suna Ammar sbd har lokacin mijinta bai taho ba yana porthacort da matarsa daya dan haka suka suka tattara suka watsar.

Tinda zayneb ta haifi Ammar bata sake lafiya ba sai ramewa takeyi tana wani irin hasken daya saka hankalin duk wanda yake familyn nasu tasu musamman yayun nata wainda suka ringa nema mata donors tako ina amma babu inda aka samu,

Sassaucin da suke samu a zuciyoyinsu shine likitoci sun tabbatar musu da akwai sauran time sosai kafin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login