Showing 6001 words to 9000 words out of 83661 words
yi cikin zuciyarshi.
Ƙwatsam seyaji...........
Littafin *BA SON TA NAKE BA* Na kuɗine akan farashin Naira #500 kacal, 0078174806 starling bank shaidar biya tanan 08142105218
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_
_*infection*_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_
_07084653262_
*BA SON TA NAKE BA*🌹
{ Tausayi ne }
NA
*AUTAR MANYA*
HOME OF QUALITIES WRT ASS....
005
Saukar tattausan hannu agadon bayanshi tare da wani irin ƙamshin shu'umin daddaɗan turare mai kashe jikin mutum.
Tsintar kanshi yayi da lumshe idanunshi nan da nan jikinshi yahau rawa bakinshi na fitar da wani irin zazzafan huci, kamo ƙasan laɓɓanshi yayi yana faman tsotsa yana fitar da hucin zazzafan feeling ɗin dake taso masa.
Kwanciya tayi lamo a faffaɗan gadon bayanshi idanunta lumshe tana jin tamkar ba'a duniya take ba sabida tsabar shauƙin soyayyarshi dake huɗa sassan jikinta tana jin daman su dauwa ma a haka.
Kanta ta ziro ta gefen wuyanshi hannunta takai dai dai saitin cream ɗinshi ta ɗauko da wani irin salo ta buɗe tare da lakatowa tana kokarin shafa masa agadon bayanshi ƙara manne masa tayi ajikinshi tana goga masa tudun cikakkun kirjinta masu firgita maza.
Cikin wani irin salo mai kama dana tafiyar tsutsa take shafo man a tsakiyar allon bayanshi tsintar hannunta tayi da cigaba da mirzawa aguri ɗaya haka nan kanta har yanzu na saƙale da gefen wuyanshi tana fesa mai sassanyan numfashinta mai cike da wani irin ƙamshi mai kashe jiki.
Hannun ta sauke daga tsakiyar gadon bayanshi ta ƙara mayarwa dai dai saitin ƙugunshi tana wani irin matsawa tamkar tana mai tausa.
"Ashhhhhhh"
Barrister ya faɗa tare da matse cinyoyinshi yana wani irin fesar da huci gaba ɗaya jikinshi rawa yake da wani irin zafin nama yake ƙoƙarin juyowa domin ganin wadda take ƙoƙarin jefa rayuwarshi a masifa sedai juyowar daze yaci karo da tattausan laɓɓan ummul data tura masa cikin bakinshi cikin hatsabi banci irin nata take sarrafa harshenta acikin bakinshi kuma har lokacin hannunta yana bisa saman ƙugunshi gaba ɗaya sun manne sun zama abu ɗaya tamkar zata shige cikin jikinshi haka take faman sarrafa shi.
Ƙarar wayar shi ita tai saurin dawo dashi daga duniyar daya faɗa jikinshi na rawa ya tunkuɗeta ya turata gefe.
Dafe jikin madubin yayi yana wani irin fitar da zazzafan huci bakinshi baya ambaton komai se kalmar.
"Ƙanu innalillahi wa'innah ilahirraju'un"!!!
Kalmar hakan kaɗai itake yawo a saman laɓɓanshi.
Wannan wace irin rayuwa ce mace da ƙoƙarin yima namiji fyaɗe mai ma ya kaishi biye mata? abin da bai taɓa aikatawa ba tsayin rayuwarshi bai taɓa haɗa jiki da mace ba se matarshi wannan wace irin shaiɗaniyyar yarinyace zata biyo shi har ɗaki ta nemi jefashi cikin halaka?
Da ƙyar ya gyara zaman tawul ɗin dake ɗaure a ƙugunshi tare da azamar yayimo jallabiya black colour ya sanya gudun kartaga al'aurarshi kafin ya dai dai ta nutsuwar shi.
Ya tunkaro ta fuskarshi da zallar rashin imani tamkar bai taɓa wata aba wai ita dariya ba.
Raɓe take a gefen gado sakamakon jefawar dayay mata ta haifar mata da buguwa a ƙugunta wanda bata jin ko yatsa zata iya ɗagawa a halin yanzu bare ta iya fita daga ɗakin duk da tsananin tsoron shi dake nausarta wanda tana jin tamkar ta arta aguje domin ceton lafiyar jikinta.
Duk takunshi ɗaya zuwa gabanta yana mai dai dai, da dokawar kirjinta mai ɗauke da tsananin tsoronshi gami da wata irin kwantacciyar soyayyarshi dake huda mata dukkan sassan jikinta.
Agabanta ya zube tare da dafe hannunshi a ƙasa yana mai ƙureta da kallonshi mai nakasa dukkan sassan jikin ma'abocin kallonshi.
Tura kanta tayi tsakanin cinyoyinta tama kasa jure kallonshi gareta.
"Mai ya kawo ki ɗakina?"
Saukar sassanyar muryarshi ma'abociyar nutsuwa kamala da haiba ta dirar mata cikin kunnenta.
Bai jira amsarta ba ya cigaba da cewa.
"Kamar yadda kike gurɓa tacciya shine nima kike son gurɓata mini rayuwa? kamar yadda kike najasa shine kike son nima na zama najasa zaki biyoni har ɗakina kinemi cillani a tarkon shaiɗan?"
A wannan karon muryarshi cike da tsantsar ɓacin rai yake faɗin maganar sedai tsabar nutsuwar shi yasa bai ɗaga murya ba, inma ka gansu bazaka ɗauka magana yake jefa mata ba seka rantse maganar arziki suke duba da yadda yake fitar da maganar a sautin hankali da nutsuwa tare dayin ƙasa da murya tamkar mai yin raɗa.
"To zan baki shawara in ma kina ganin hakan waye wa ne to sam ba waye wa bane sema naƙasu daze janyo miki tare da zubewar mutunci kamarki yarinya ƙarama wadda a tsarin ilimi ba lallai kin kammala karatun secondry ba amman ki zaɓi wannan harkar ta jagaliyanci wadda baxata fusheki komai ba se taɓewa da wahalar rayuwa, ban taɓa ganin shaiɗaniya irin kiba hakan yasa na baki muhalli na matsayin karuwa ƴar jagaliya maiwa maza fyaɗe marar kamun kai daƙiƙiya marar tunani naji ina tausaya miki da wannan makauniyar rayuwar da kika zaɓa ma kanki tabbas idan kika yarda na kuma saka idanuna akan fuskarki zan sauya maki halittar zubinta zan maki mugun tabon da ƴan gidanku bazasu ƙara shaidaki ba"
yafaɗa tare da saurin tashi ya wurga mata wayarta se yanzu ya tuna ashe ɗazu garin sauri bai saka ma ƙofarshi key ba wannan dalilin ya bata damar ratso mai ɗaki harta so jefa rayuwarshi cikin bala'i da dana sani wanda wayar da sukai da basmah ita ce ummul'aba isin na shigar shi cikin halin feeling wanda idan yana ciki yake jimawa bai dawo dai dai ba wanda shine har ita wannan shaiɗaniyar yarinyar ta sami damar raɓar jikinshi.
Daga zaunan datake ta yunƙura kaɗan tana matse fuska alamar har yanzu akwai zafin buguwa a tare da ita amman hakan bai sa ta zauna ba seda ta cigaba da tashi har Allah ya bata ikon miƙewa gaba ɗaya tare da taimakon dafe bangon datai ta kai duba gareshi ya bata baya tare da zira hannu cikin aljihun jallabiyar jikinshi.
Murya can ƙasa mai cike da kukan nadamar abin da tai take furta.
"Nima ba laifina bane laifin zuciya tace wadda batai min adalci ba don ta kaini inda bazata sami muhalli ba! nagode da dukkan furucinka gareni amman kasani atun haɗuwarmu dakai a ɗazu naji duk duniya bani da Aminin zuci idan ba kai ba Ina sonka! ina son ka!! ina Sonka!!! wanda soyayyar ka ce tajani na afka maka kuma ka riƙe a ranka har abada Ummul khairi mai son kace.........
"Ƙarya kike munafuka ƴar iska ba sona kike ba sha'awa ta kike irin na matan bariki marasa aji irinki! to ki sani Ni ALIYU DIKKO nai miki nisan da har abada bazaki kamoni ba Domin wuta da ruwa basa haɗuwa kin taɓa ganin tsafta da najasa sun haɗu? to ni dake babu maganar soyayya domin bakya cikin types na matan dana ke burin mallaka a rayuwata"
Yafaɗa yana mai nufota kamar ze shaƙeta.
Da wani irin sauri ta juya har tana ƙara yarda wayarta a karo na biyu tai saurin nufar ƙofar fita muryarta a dakushe ta furta.
"I love you for ever Aliyu"
Tana faɗin hakan ta fice a ɗakin tare da datso ƙofar ta silale a wajan tare da sanya kuka! mai ƙarfi na jimamin Rashin Aliyu na har abada anya zata jure........?
Littafin *BA SON TA NAKE BA* Na kuɗine akan farashin Naira #300 kacal, 0078174806 starling bank shaidar biya tanan 08142105218
*BA SON TA NAKE BA*🌹
{ Tausayi ne }
NA
*AUTAR MANYA*
HOME OF QUALITIES WRT ASS....
007
Ƙarfe 4:30am ya farka bakinshi ɗauke da addu'ar tashi daga barci ya ziro da santala santalan ƙafafunshi zuwa ƙasa tare da miƙewa tsaye, yana mai yamutsa fuskarshi wadda take nuni da baccin nashi bai ma ishe shiba agurguje ya faɗa bathroom ya haɗa ruwan ɗumi ya watsa ajikinshi tare da ɗauro alwala.
Ya fito gami da shinfiɗa darduma ya soma gabatar da raka'atul fijir seda ya duba time yaga lokacin shiga masjid yayi sannan ya miƙe ya gabatar da asubahi bayan ya idar ya soma rera karatun alkur'ani mai girma wanda inba tsakanin jiya da yau ba ya ɗauki lokaci mai tsayi baiyi karatun kur'ani ba kuma Alhamdulillahi tun jiya daya karanta baqrah yaji daɗin azuciyarshi hakanan yau ma dayake karatun nan baƙaramin daɗi yake jiba.
Seda ya karanta shafi biyu nadaga cikin suratul kahfi sannan ya rufe qur'an appks ɗin dake wayarshi kana ya soma karanta azkarul subhi, Bayan ya kammala yayi salati ga Annabi muhammad (s.a.w)Tare da shafe jikinshi kana ya miƙe.
Gaban mirrow ya tsaya yana shafawa jikinshi cream ƙarfe shidda dai dai ya kammala shirinsa cikin haɗaɗɗun Ash colour suite waɗanda suka amshi kalar fatar jikinshi sukai mai wani irin kyau ɓarin turare yayi ma jikinshi haɗi da ɗaukar wata ƙaramar baƙar jaka wadda takardune masu yawa acikinta.
Wayarshi ya ɗauka tare da manna baƙin glass a saman fuskarshi ya nufi fita daga dakin yana zuba wani irin haɗaɗɗan ƙamshi.
Ƙofar ɗakin yayi ma key da sauri yake tafiya yana dannah layin mutumin dasukai magana dashi ajiya Cikin nutsuwa mutumin ya ɗauka suka soma gaisawa kafin ya sanar masa cewa gashi nan a hanya.
Direct wajan motar shi ya karasa ya buɗe ya shiga tare da bata wuta kai tsaye hanyar kotun da zasu fara shari'a ya wuce.
Tafiya kaɗan ya ƙarasa a bakin kotun suka haɗu da mutumin atare suka ƙarasa ciki inda shi ya wuce wajan alƙali shikuma mutumin ya zauna zaman jiranshi.
Ƙarfe 11:00am aka soma gabatar da shari'a wanda Barrister Aliyu Ali Dikko shiya tsayawa mutumin dake ƙarar Abokinsa daya cinye mai kuɗinshi wanda ya ranta mai waɗanda kuɗin suke da mugun yawa cikin nasara suka soma gabatar da shari'ar wanda mutumin bai musa ba sedai yace aɗan ɗaga mai ƙafa sabida halin rashin da ake fama dashi a ƙasarnan dan haka alƙali yayi rubutu tare da buƙatar kowani ɓangare su sanya hannun yarje jeniyar biyan kuɗin da mutumin ya amince zeyi nan da ƙarshen wata.
Alhamdulillahi Anyi shari'a lafiya angama lafiya don Kuwa komai ya tafi cikin tsanaki bayan an tashi Aliyu sukai musabaha da jama'ar wajan sannan ya hau motarshi yayi gidan kakarshi kamar yadda Yayi ma Ammin shi alƙawarin zuwa....
Banda rawa babu abin da jikin ummul keyi wanda hakan yayi matiƙar bawa ameerah tsoro aranta take ayyanah kodai Ummul tana da wata lalurar ne wadda ita bata san da ita ba Babu abin da take face saurin taje ta sadata da inda ta buƙata saboda gudun kar wata matsala ta afku duk da har zuwa wannan lokacin bata tunanin acikin Ahalin ummul da wanda yasan inda take da zama.
Tafiya ce mai shegen nisa kafin su ƙarasa cikin unguwar Tunga wadda anan gidan mahaifan ummul yake tafiya ameerah take a hankali tana bin yadda ummul ke nuna mata ada idan sunje har suka ƙarasa cikin layin gidan su ummul wanda ya cika da yara ana ta wasan ƙasa wasu kuma na ƴar gala gala alamar yawanci yaran basuje makaranta ba sabida anyi ruwan dare gari duk ya jiƙe.
Tunda motar ta doso layin yaran suka fara ihu! suna bin bayan motar suna shafata kafin ameerah ta sami waje adai dai bakin wani ɗan madaidaicin gida mai ɗauke da farin gate tai parking motar tata.
Dayake baƙin glass motar ameerah kedashi yasa na waje baya ganin na ciki dan haka seda yaran suka gama ihunsu sannan ameerah ta kashe motar tare da fitowa waje.
Itama ummul a hankali ta buɗe nata ɓarin tare da fitowa ta dubi wani ɓaɓurarran gidan ƙasa dayafi ko wani gida lalacewa a layin ta lumshe idanu tare da nufar wannan gidan mai farin gate gami da sanya hannu tana kwankwasawa.
Kamar zata faɗi ameerah tayi saurin tarota jikinta ahaka wata ƴar yarinya da bazata fi shekara goma sha biyar ba tazo ta buɗe musu gate ɗin tare da rabewa ta basu waje suka shiga ƙaramin tsakar gida se kofar falo wadda ɗakuna da kicin da toilet ke ciki wanda alamu sun nuna gidan mai komai acikine.
A ɗan ƙarami falo suka yada zango saman kujera ummul ta kwanta tana kiran.
"Hajjah hajjah hajjata kina ina?"
Muryarta a hankali tana mayar da numfashi.
Da sauri wata fara jajir ɗin tsohuwa wadda zata kai shekaru sittin a duniya ta fito daga cikin ɗakin dake kallonsu bakinta ɗauke da far'a take furta.
"wana keji kamar ummi agidan nawa?"
Tafaɗa tana ƙarasowa zuwa gaban ummul ganin ummu kwance saman kujera yasa wannan tsohuwa wadda ta kira da suna hajjah ta ɗagata da sauri ta ɗora saman cinyarta.
A kiɗime take kallon ameerah tare da cewa.
"Mai ya sami ummi kuma ke yarinya?"
tafaɗa duk hankalinta yana wajan ummul.dake zubar da hawaye.
"Hajja tun jiya take ta zazzaɓi shine yau tace akawota gidan ki"
Ameerah ta faɗa tana mai yaba karamcin tsohuwar.
"To sannu ummi salame zoki kawo mata magani tasha taje ta kwanta daman seda nace karki tafi ki zamanki anan kika kama hanya kika tafi yanzu wa gari ya waya kin bar ahalin ki cikin takaici"
Hajjah ta faɗa tare da amsar ruwan da salame ta miko mata.
Tashi ameerah tayi tare dayi ma hajja sallama ta kama gabanta wanda hajja ita kuma ta kamo ummul jikinta ta bata maganin tasha sannan tace ta kwanta bayan ta kunna mata fanka.
"Yi bacci anjima idan babanku ya fita se a aika akira babar taki, ni bana son ma ki ƙara tafiya ko ina"
Lumshe idanu ummul tayi tana mai jin hajja da tatsuniyarta amman tafiya kam seta koma
"Bara na koma kicin na ƙarasa girki wannan ɗan rigimar ne ze ƙaraso gidan tunda yayi aure shekara biyar yaron nan bai ƙara tako ƙafarshi gidana ba se yau"
Tafaɗa tare da nufar kicin.
Gyara kwanciya ummul tayi ba jimawa bacci yayi awon gaba da ita.....
Littafin *BA SON TA NAKE BA* Na kuɗine akan farashin Naira #300 kacal, 0078174806 starling bank shaidar biya tanan 08142105218, Idan kuma katin Mtn zaki Turo na 400
*BA SON TA NAKE BA*🌹
{ Tausayi ne }
NA
*AUTAR MANYA*
HOME OF QUALITIES WRT ASS....
008
Tuƙi yake cike da wata irin nutsuwa wadda a zahiri haka halittarshi take gaba ɗaya soya ke ya ƙarasa gidan hajja don ba ƙaramar wahala ya kwaso ba,da ƙyar yake tuƙin ga unguwar da hajja take mai azabar nisa daga inda ya fito.
Yana tafe yana duba tsarin sauye-sauyen da aka samu a garin sabida yaɗan jima bai shigo ba ahaka ya shiga cikin unguwar su hajja yana tuƙi yana jan tsaki akai akai sabida yadda wajan duk ya cika da tudu da kwari na ruwan sama da akai duk ya sanya hanyar tayi babu kyan gani.
A hankali ya ƙarasar da motar shi cikin layin sosai ya ware ido yana kallon yadda yara ke faman wasannin su rabon shi da gidan hajja tun kafin yayi aure shekaru biyar kenan se yau da Allah ya kawoshi yasan ba ƙaramar mita hajja zata yi mai ba tsintar kanshi yayi da ɗan sakin ƙaramin murmushi kafin ya kashe motar ya fito waje hannun shi riƙe da key tare da wayar shi wadda take faman zuba ringing na kiran da basmah take mai tun jiya wanda bai sami damar ɗagawa ba.
Cikin ɗan zafin nama kaɗan ya ƙarasa bakin gate ɗin lokaci wajan 12:30pm rana taɗan soma fitowa wannan yasa yake ta yamutsa fuskarshi kasance warshi mutum marar son zafin rana da zafi ko kaɗan, Azurfar dake yatsunshi yasa yake ɗan duka gate ɗin cikin ɗaga murya hajja dake ƙoƙarin fitowa take furta.
"Wani marar haƙurin ne ze karyan ƙofar?"
Dariya yaɗan ƙunshe yasan za'a rina hajja da mugun son abin duniya ita komai nata kif kif ne bata son wasa da abin duniya, Harta karaso ta buɗe mai gate ɗin tana faman mita shikuma bai yi magana ba.
tana buɗewa yayi wani irin sauri ya ɗaneta yana cusa kansa a saman wuyanta yana furta.
"I miss you hajjata"
Ture shi tai tare da cewa.
"Da Allah sakar ni gososo dakai zaka ɓallan ƙashi damma ƙashin bana rainon madara bane yasha jar dawar da ya horu"
Taɓe baki yayi tare da langwaɓar da kanshi gefe yayi kalar abin tausayi tare da ce mata.
"Haba hajjata duk duniya in kika cire su ammi wa nake dashi idan bake ba wa ze rungume ni yashafa kaina naji dadi idan bake ba amman shine zaki min haka"
Yafaɗa