Showing 42001 words to 45000 words out of 121037 words

Chapter 15 - RUMBUN QAYA COMPLETE hausa Novel

03 Sep 2024

17341

sanarwa ko Hamma Haydar bane ba? Zata fara dai tuntubar Kamal ya gaya mata gaskiyar komai kar ya sakata a matsala da karancin shekarun ta.


***Da sassafe Habib ya iso gidan ya tsaye a waje har sai da Aryan din ya gama shiryawa ya fito sannan ya ganshi zaune tare da Baba me gadi, tashi yayi da sauri ya gaida shi ya karbi jakar hannun sa ya saka a mota ya bud'e masa bayan motar amma sai yaki ya wuce ya zauna a gaba yana kin kallon sa. Rufe kofar yayi ya zagayo ya zauna sannan yace

"Sir da ka daure ka zauna a bayan"

"Anan nake son zama Habeeb."

"Please sir, bana so oga Kamal yaga kamar bana aiki na yadda ya kamata."

"Menene aikin naka?" Ya tambaye shi

"Driver."

Dan shiru Aryan din yayi kamar ba zai koma ba, sai kuma ya bud'e kofar ya koma bayan ya shiga ya rufe ba tare da ya sake cewa komai ba.
Gidan Ya Nabeela suka fara zuwa, tun daren jiya ta kira shi akan maganar daddy, hankalin ta ya kasa kwanciya dan duk wanda tasan suna harkar tafiye tafiye da Daddyn suna gari babu inda suka je, sannan duk rashin shirin da yake dasu musamman ma Aryan baya taba yin wata tafiya be sanar dasu ba, sannan wayar sa a kashe kuma maigadi yace be ga fitar sa ba dan tazo jiyan gidan lokacin Hajiya Zeenat tana sama sai wasu mutane da bata nutsu dasu ba da ta gani a gidan dan har ita kanta sai da suka tsaida ita da tambayar wajen wanda zata. Ko baccin kirki bata samu tayi jiyan nan ba kwata-kwata, shiyasa ta kira Aryan din shine yace mata zaizo da safe.
A zaune ya sameta tayi jigum tana zaune ko kayan baccin jikinta bata cire ba sai Hijab data dora akai ta sallami yan makaranta ta dawo ta zauna a falon tana cigaba da gwada kiran wayar Daddyn ko zata samu ta shiga. Tasowa tayi da sauri ta tare shi

"Aryan daddy ba kalou ba wallahi, ni ban yarda da matar nan ba,jiya da naje yanayin yadda take kaffa-kaffa da saman Daddyn na ji ban amince ba, dan Allah kayi wani abu akai, kar taje ta cutar da shi."

Hannun ta ya kama ya rike suka zauna ya zama tamkar shine wan itace kanwar saboda yadda duk ta rikice.

"Ya Nabeela, me yasa zaki damu kanki haka? Bayan kinfi kowa sanin Daddy ya zabi matar chan akan mu, duk abinda ya faru a yanzu be kamata ki damu ba, dan hakki ne ya fara bibiyar su idan ma wani abun ne ya same shi."

"Aryan! Kasan me kake fada kuwa? Daddy fa akace mahaifin mu."

"Na sani, ki kwantar da hankalin ki dan Allah, damuwarki matsala ce a gareni fiye da duk abinda zai same shi, amma zan bincika saboda ke, zan gano menene matsalar, amma saboda ke."

"Naji, ka shiga dakin sa ka dubo da kanka, ban yadda da ita ba wallahi, she's hiding something matar nan bata tsoron ALLAH."

"Zanyi, amma sai na gama da office"

"Na yarda, ina jiranka dan Allah."

"Ok, ki kwantar da hankalin ki, babu komai in sha Allah."

"Tohm shikenan."

"Bari naje, zamuyi waya anjima."

"Ok."

Maganganun Ya Nabeelan ya dinga tattaunawa da zuciyar sa har suka iso company, yana zuro kafarsa suka hada ido da Adam a tsaye cikin fence yana kallon saitin sa, tahowa yayi wajen sa kai tsaye ya ganshi sarai anma sai yayi kamar be ganshi ba ya shiga barin wajen yayi hanyar nasu building din. Daga kafa yayi ganin zai shige ya cimmasa ya tsaida shi.

"Aryan please dan tsaye, tambayar ka zan,."

"Menene?"

"Dan Allah Raihana ta daina zuwa ne?"

Kamar wanda ya sokawa mashi haka yaji, yayi masa wani kallon lallai ma ka raina mun hankali sannan yayi shigewar sa. Tsaki Adam yaja ya juya yana kunkuni.
Kanshi tsaye ya wuce office dinsu ko wajen yin attendance be je ba, ya samu desk dinta empty ba kowa,juyawa yayi ya wuce office din sa kawai ransa a bace dan idan akwai abinda yaki jini shine Adam ya tsaida shi da shirmen sa, musamman yanzu da maganar wata daban take hada su ba abinda ya saba hada su a baya ba. Haka kurum a duk sanda irin haka ta faru yake kasa controling fushin sa, ya kasa zama sam a office din ya fito ya leka office din Kamal shima be zo ba, agogon hannun sa ya kalla yaga karfe tara har da rabi ta dan gota ma. Tasowa Zainab tayi daga wajen zaman ta cikin yauki da yanga tazo ta tsaya a gabansa tana murmushi

"Akwai abinda kake bukata ne sir?"

"Babu komai, idan corper din nan tazo kice tazo ta sameni a office." Sai ya juya ya koma office din ya barta a tsaye mamakin sa na neman kai ta kasa, akan Raihanan ya kasa nutsuwa tunda ya shigo haka ko kuma wani abun tayi da ya kasa hakura ya jira ta shigo. A sanyaye ta koma wajen zaman ta, ta zauna tana ko zama sai ga Raihanan ta shigo sanye da black abaya tayi rolling da mayafi mustard colour wanda yayi masifar karbar farar fatar ta. Wani kululun abu ne ya tokare Zainab a makogwaro ta yi saurin dauke kanta ganin tana bi suna gaisawa da mutane, ko da tazo kanta tayi mata sallama kamar yadda ta saba ta wuce office dinsu ta bar Zainab da wani irin sanyayyan kamshin ta da ya cika mata hanci. Tana sane taki fada mata sakon Aryan din dan zuciyar ta zata iya bugawa idan ta cigaba da ganin Aryan din yana kula Raihanan.
Bayan mintuna kamar ashirin da zuwan ta, tana zaune kawai dan bata san aikin da zatayi ba Kamal kuma har lokacin be shigo ba bare ta tambaya shi, Aryan kuwa ko giyar wake tasha ba zata tunkare shi ba dan a dar dar take dashi gani take kamar zai gano abinda tayi. Kanta ta dora a saman desk din kawai ta kulle idon ta, ta kunna suratul bakara ta makala earpiece dan ta gaji da kallon wayar.
A kanta ya tsaya yana nakaltar yanayin ta, amma sam bata san ya shigo ba, dan ko alamun an tsaya a kanta bata ji ba, a hankali kad'an kad'an take motsa bakin ta, tana bin kira'ar shuraim kuma har lokacin bata bud'e idon ta ba. Dan rankwafowa yayi a daidai saman kanta ya sa hannu ya zare earpiece din daga jikin wayar ta dago da sauri idanun su suka sarke da juna. Diriricewa tayi dan bata tsammaci ganin sa a wajen ba dan ba kasafai yake shigowa ba, waigawa tayi taga babu kowa ashe a office din su abdulhakeem duk sun fita sai ita kadai sai shi da yake tsaye a gabanta rike da earpiece din. Ji tayi baki daya office din yayi mata wani irin fadi da girman gaske, daidaita nutsuwar ta tayi ganin ko gezau be ba yana kallon ta kamar be san me yake ba.

"Ina kwana?" Ta tattaro jarumta ta gaishe shi ganin yaki cewa komai

"Follow me." Yace kawai ya juya ya fice daga office din rike da earpiece din nata a hannun shi.





_ZAFAFA BIYAR 2023_*🔥🔥🔥
_*Sabuwar shekara sabon salo sabon taku,*_
_*Makaranta littafan hausa kuma masoya marubutan zafafa kuzo ga sabuwar tafiya zazzafa tazo karku bari ayi babuku *_

_*Zafafan alkaluman haziqan maruban zafafa biyar kowa yasan na daban ne,wannan karon ma sunzo da sababbin salo me kama zuciya.*_
_*ZAFAFAN MARUBUTAN SUNZO DA SABABBIN LITATTAFANSU NA 2023 Kamar haka,*_

1  _*IDON NERA*_
    Mamuhgee

2  _*DAUDAR GORA*_ ciki ka shata
    Billyn Abdul

3  _*RUMBUN QAYA*_
     Hafsat Rano

4  _*KI KULANI*_ mallakin zuciyata
    Hafsat Miss Xoxo

5   _*A RUBUCE TAKE*_ qaddarata
    Safiya Huguma

_DUKA GUDA BIYAR DIN ZAKA SAMESU A FARASHIN 1200_

Guda 5 1200
Guda 4 1000
Guda 3 800
Guda 2 600
Guda 1 400

_*zaku saka kudin a wannan account din👇*_

_*0022419171 Access Bank Maryam sani*_

Saiku tura shedar ta👇

_*09033181070*_

Idan kuma katin Waya ne zaku tura katin MTN ta wannan layin👇

09166221261


TEAM ZAFAFA BIYAR🔥🔥
MUNGODE🙏🙏❤️
RQ*

      Page 21

***Tashi tayi jiki a sanyaye ta bishi, su Zainab suka bita da kallo kamar zasu cinye ta. Sai da ta fara knocking a kofar dan ya riga ya shige sannan ta tura kofar ta shiga kanta a k'asa sosai tana tsoron hada ido dashi. Tana jin idanun sa akanta sanda ta shigo har ta karaso ta tsaya a gaban table din.

"Goodmorning sir." Ta maimaita gaishe shi jin yaki cewa komai

"Zainab bata fada miki ina kiranki ba?"

Girgiza kai tayi

"Bata fada min ba."

Waya ya jawo gabansa yayi kira

"Come please."

Yace kawai ya ajiye wayar. Cikin siritar da murya ta shigo tana gwalli tazo ta tsaya ta gefen kujerar sa

"Sir gani."

"Nace idan tazo ki turo min ita kamar ko?"

"Na'am?"

"Yes! Me yasa baki fada mata ba?"

Kallon bangaren da Raihanan take tsaye tayi,sannan tace

"Na fada mata sanda ta shigo, amma bata ji ba cox bata min magana ko nayi mata ni."

"Innalillahi!" Tace tana kallon Zainab din

"Eh a gabana kika gaisa da kowa kika ki kulani, ina ta miki magana kikayi biris kika wuce office na dauka ma kinji ne kawai ba zaki amsa bane ba."

"Ikon Allah!"

Kawai tace ba tare da tace komai ba kuma, abin ya tsallake tunanin ta gaba daya ma, shiyasa ta kasa cewa komai tana jiran gogan da ya kirawo ta yayi magana

"Excuse us please."

Ya cewa Zainab kawai ba tare da ya ce komai akan abinda tace din ba, sai data fara dan dukar da kai alamun respect sannan ta juya ta fita.

"Zauna." Ya nuna mata kujera, zama tayi a darare tana jiran abinda zai ce

"Ya jikin naki?" Yace yana kokarin bud'e computer sa

"Na samu sauki."

"Ok good, aiki zan saka ki, amma anan zaki zauna kiyi shi."

"Ok sir."

Takarda ya turo mata gabanta yace ta duba kafin ya gama shigar da komai, ta dauka ta fara dubawa shi kuma ya cigaba da abinda yake yana jin nutsuwa sosai na saukar masa.

***Yau baki daya Kamal be shigo office din ba, ya dai kira Aryan din ya sanar dashi ba zai shigo ba shiyasa ma aikin ya rinchabe ma Aryan din dole ya rarrabawa su Abdulhakeem aikin Raihana kuma na taya shi da wani anan office din nasa. Yanayin yadda aikin ya dauki zafi sosai ya saka sam basu gane lokaci ya ja sosai ba dan har azahar na neman kufce musu. Sallah yace suje suyi dukka sannan suyi lunch daga nan sai suzo su kara ko away daya be sannan kowa ya tafi. Tunda Raihana tazo office din basu taba dadewa irin ta yau ba, gashi ta kasa ce masa zata tafi dan ya tsare ko ina motsi kad'an zai ce ta duba masa abu kaza wanda kuma ko ta duba daga baya sai ya sake dubawa dan ba wai tasan kan aikin bane dukka, musamman harka ta kudi da lissafi yana da rikitarwa sosai. Ta idar da sallar kenan tana zaune tana tunanin ko ta gudu sai tunanin kiran da Hajiya Zeenat take mata ya shigo mata, ta manta shaf tace zata kirata idan zata zo gashi bata fadawa Kamal din ba ma bare ya gaya mata abinda zatayi. Wayar ta, ta dauka tayi masa text message ta ajiye tana jiran reply dinsa akan zuwan.

"Call her kice zaki taho yanzu." 
   Yayi mata reply a take, tana duba message din ta kira number Hajiya Zeenat din, tace mata zata zo yanzu, toh tace mata duk da bata gidan amma ta lissafa zata iya zuwa kafin ta karasa ta jirata ko ma suyi daidai dan bata so damar yau din ta kufce mata.
  Tashi tayi daga wajen sallar ta gyara mayafin ta sannan ta komo office din ta ganshi ya dora akan aikin ba ko hutawa, sau daya tak ya kalle ta sanda ta shigo ya cigaba da abinda yake yi, daga in da take ta tsaya tace masa zata tafi. Banza yayi Mata kamar ba dashi take magana ba, wanda a zahiri ya ji ta sarai sai dai haka kawai yaji maganar ta, ta dan bata mishi rai haka kawai kuma. Sai da ta kara maimaitawa sannan yace

"Go."

A bacin rai duk da be dago ba amma taji yanayin yadda yayi sounding, juyawa tayi kawai tayi ficewarta ya bi bayan ta, da kallo nan take sai yaji aikin ya fice daga kansa. Lunch din da yayi musu order dukkan su ma'aikatan ya kalla, kowa ya dau nasa sai nata kawai da nashi a wajen a ajiye. Ajiye pen din hannun sa yayi ya ji ba zai iya cigaba da rubutun ba, ya rufe komai ya tashi ya hau tattare kayan sa.
  Tana tafe suna waya da Kamal yana gaya mata abinda yake so tayi masa a cikin gidan, har ta karaso gate ta dagawa masu gadin hannu dan har sun saba sannan ta fita. A daidai lokacin shima Aryan ya fito Habeeb dake zaune karkashin wata bishiya yayi saurin sanarwa Kamal fitowar Aryan din dan sun san dole idan ya ganta zai iya cewa su rage mata hanya kuma hakan zai bata musu shirin su. Da sauri Kamal yace mata ta samu wani wajen ta dan labe ta jira wucewar motar Aryan din. Da sauri ta shige wani dan lungu ta labe. Daga ganin yadda ya fito neman ta yake yi, yadda yake rarraba idanun sa a tsakanin wajen ya tabbatar musu da hakan, wajen sa Habeeb ya karaso bayan ya jawo motar

"Baka ga wata yanzu ta fita ba?"

"Ai da yake yallabai bacci ne ya dan dauke ni naji sanyin kasan bishiya, inaga ta fita ban lura ba sam."

"Ok, muje."

Ya bud'e masa motar ya shiga. Ta na nan a labe suka zo suka wuce sannan ta fito ta karasa titi ta samu abun hawa ta fada masa in da zai kaita.
  Tun kafin ta karasa Hajiya Zeenat tayi waya tace a barta ta shiga, dan haka kai tsaye ta wuce in da tasan zata same ta. Falon tsit babu motsin kowa, dan zama tayi kad'an tana sake karewa falon kallo, sai ga kiran Kamal.

"Kinga kafar bene?"

"Eh." Tace tana kallon stairs din

"Yawwa, tashi ki hau karki kashe wayar."

Tashi tayi a tsorace ta kama matattakalar ta fara hawa cike da tsoro, babu abinda kirjinta yake sai dukan uku-uku. Shi yake directing dinta har taje kofar, tasa hannu ta murd'a da nufin budewa amma sai ta jita a rufe

"A rufe take da key."

"Gosh!" Ya hau kama goshin sa yana murzawa

"Kinsan me zaki? Saka bakin ki a jikin kofar ki kira sunan Daddy."

"Ok." Tace, ta dan makala kanta a hankali tace

"Daddy."

Shiru babu wani motsi, ta sake maimaitawa a karo na biyu, sai taji kamar motsi kamar gurnani, sake fadan sunan tayi, sosai taji sautin numfashin babban mutum me cike da wahalarwa.

"Akwai mutum a ciki Sir, wallahi akwai mutum." Ta fada a rude tana yin baya

"Calm down Raihana, don't panic please, maza ki koma falon kaza ki jirata, suna daf da shigowa gidan kiyi sauri."

"Ok."

Tace da sauri ta yi hanyar sauka daga saman, ta dinga hadawa da bibiyu ta sauka ta zauna tana dafe kirjin ta

"Daddyn Aryan ne kenan a ciki?"

Wani hawaye ne ya biyo mata ya sauko tayi saurin share shi jin alamun ana shigowa, tayi matukar kokari wajen daidai ta kanta sanda Hajiya Zeenat ta karaso ciki fuskar ta a sake da fara'ah

"Yau ga yata da ta gujeni."

Zamewa tayi daga kujerar ta zauna akan carpet sannan ta hau gaishe ta

"Tashi ki hau kujera mana, tashi tashi sai kace wata bakuwa Raihana?"

"Nan ma yayi Anty."

"Toh ai shikenan, ya gida ya mutanen gidan?"

"Duk lafiya lou."

"Masha Allah , ya labarin Abban ki kuwa? Kin sake zuwa kin duba shi?"

"Ai ya fito ma."

"Kai haba? Ah Masha Allah, yaushe? Shine amma baki fada min ba."

"Last week ne Anty, sannan bani da lafiya."

"Ok haka ne, toh sai na shirya ai naje na gaishe shi ko?"

"Ai baya nan Anty,baya kasar."

"Ah lafiya dai ko?"

"Da sauki toh."

"Ayya toh Allah ya bashi lafiya, yana dawowa ki sanar dani zanje na duba shi nayi masa barka da arziki."

"Ok tam in sha Allah."

  Wayar tace tayi kara, message ne daga Kamal

_"maza ki fice Aryan yana hanyar zuwa."_

Yunkurawa tayi da sauri

"Hajiya zan tafi, Addah tana kirana."

"Toh, toh shikenan sai munyi waya ko? Wajen aikin naki ba dai wata matsala ko?"

"Babu komai Anty, nagode."

   Sauri ta dinga yi tana waige har ta fita daga unguwar baki daya, har ta samu napep ta shige. Bayan wajen mintuna ashirin da tafiyar ta sannan Aryan ya iso. Da k'yar ya iya bari Habeeb yayi parking a harabar gidan ya balle murfin motar ya shiga ciki a sukwane. Yanayin yadda ya shigo gidan ya saka Hajiya Zeenat mikewa tsaye,

"Lafiya?"

Ta tare shi tana tambayar sa, wuce ta yayi ya fara hayewa saman da sauri da sauri. Bin bayan sa tayi da sauri tana kiran sunan sa. Kai tsaye dakin daddy ya nufa, yana zuwa ya tura kofar da karfi. Babu kowa a ciki sai dakin da yake a gyare ko ina.

"Menene wai Aryan?"

"Ina Daddy?" Yace yana zare mata ido cikin matukar bacin Rai.

"Mtsw! Taja tsaki,

"Dalilin da zaka shigo gidan a haka? Baka san yayi tafiya bane ko me? Me kake nufi kenan da abinda kayi yanzu?"

"Ina kika kaishi? Yana ina?"

"Ban sani ba, tunda baka yarda ba ai gidan ba bakon ka bane ba, ka shiga ka bincika. Mtsw!"

Ta juya ta barshi a tsaye a wajen. Dafe kansa yayi da hannu biyu da yake masa wani irin bugawa ya shiga bi dakunan daya bayan daya yana dubawa har da lekawa kasan gado. Text message din da aka tura masa ya sake dubawa yana son sake tabbatar da abinda yake kunshe a sakon

_"Kayi sauri kaje mahaifin ka yana rufe a dakinsa, suna kokarin chanja masa dakin dan haka sai kayi sauri."_

Abinda ya taso shi kenan afujajan duk da be san waye yayi amsa message din ba, waye yake kokarin wasa da hankalin sa? Ya tambayi kansa. Kiran Ya Nabeela a karo na kusan biyar ya shigo, dagawa yayi yana yarfe hannun sa ya zauna a gefen gadon Daddyn ya dafe kansa sannan ya daga

"Ya ake ciki Aryan?"

"Bata ciki ya Nabeela."

"Na shiga uku, yanzu ya zamuyi?"

Idon sa ne ya sauka akan yar karamar wayar Daddyn da ta kusa shigewa kasa gado, hannu yasa ya dauka ya ganta a kashe alamun charging

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login