Showing 60001 words to 63000 words out of 121037 words

Chapter 21 - RUMBUN QAYA COMPLETE hausa Novel

03 Sep 2024

17350

zauna a gefen ta ya rike hannun ta a cikin nasa ya sunkuyar da kansa. A gefen sa Kamal ya zauna ya dora hannun sa a saman kafadar Aryan din, dagowa yayi suka had'a ido sai ya juyar da kansa ba tare da yace komai ba. Shima Kamal din be masa magana ba dan ya san ba zai saurare shi ba. Cigaba da zama sukayi har zuwa sanda Dr ya fito suka tashi gaaba daya suka isa wajen sa, bayani yayi musu akan zasu maidashi ICU sannan ya wuce su kuma duk jikin su ya kara sanyi sosai.
   Gida suka fara lallaba Ya Nabeela ta tafi saboda dare yayi sosai ya zama sai Kamal din da Aryan kadai har aka gama duk processing komai Kamal ya biya Bill din duk Aryan na kallon sa amma yaki masa magana shima kuma ya share shi kansa tsaye yake abubuwan sa dan ya riga yasan waye Aryan duk abinda zai kallon sa kawai zai, ya kuma san abun da ya tsana a shareshi idan ya nuna yayi fushi ka nuna sam baka san yanayi ba yafi saurin sakkowa. Wasu allurai likitan yace a siyo a pharmacy Kamal yasa hannu zai karba Aryan ya karbe yana bata fuska

"Zan iya kula dashi."

Dariya ce ta kwacewa Kamal ya fizge takardar sannan yace

"I can do it too, kai I'm already doing it ma."

"Ya isa hakan toh, I will take over."

"Waya saka?"

"Ni na saka kaina."

"Kana magana da hukuma ne please, so ka gyara maganar ka kaga yaran chan jiran umarni suke kawai."

Tsaki Aryan yaja kawai ya barshi a wajen yana masa dariya. Daya daga cikin yaran ya bawa takardar ya samo allurar a pharmacy ya kawo sannan ya kaiwa likitan. Sosai Aryan ya cika fam da abinda Kamal din yake masa, amma ya kyale shi dan ya lura so yake ya tike shi kamar yadda Adam yake masa a ko da yaushe.

     Tare suka jera suka tafi masallaci da asubah dan a zaune suka kwana, sukayi sallar suka sake jerowa suka dawo sai a lokacin Kamal yace

"Zanje gida na dawo, sannan inaso ka san Hajiya Zeenat ta shiga hannu, sai ka shirya shari'ah da ita."

   Da sauri Aryan ya kalle shi,amma sai yayi tafiyar sa ya barshi a tsaye cike da mamakin Kamal din. Bin sa yayi da sauri ya sha gabansa yana kallon sa

"Yaushe? Me ya faru? Ya akayi duk hakan ta kasance?"

"Sai naje naga Madam naga yadda ta kwana tukunna, kasan me iyali gashi na barta ita kadai kuma ba wani Jin dadi take ba, mayi magana dai yanzu sauri nake."

"Please kamal, tell me everything dan Allah."

"Ka daina fushin kenan?"

"Dan Allah!"

"Labari ne me tsawo, amma from abinda ka gani a jikina zaka gane cewa duk plan ne, kuma a karshe munyi nasara, yanzu sai kayi taking over daga nan, da mun tura ta kotu aiki ya koma hannun ka. Sannan, barrister Matawalle yana tare da mu, duk da yana yi ne ba dan mu din ba shima saboda tasu matsalar amma a kalla mun samu strong evidence na videon ta da yake wajen sa wanda shine mafarin komai, kuma shine zai yi linking duk wani abun da ta aikata tare da me taimaka mata."

"Huhh!" Ya sauke ajiyar zuciya cikin wani irin yanayi ya rungume Kamal din kwalla na taruwa a idon sa. Kwallar shima Kamal ya goge a boye sannan ya bubbuga bayan Aryan din yace

"Over to you Barrister ARYAN!"

Bud'e masa kofar Aryan yayi ya shiga motar ya zauna sannan ya rankwafo jikin window yace

"I owe you Kamal. Bansan yadda zan saka maka duk abinda kayi min ba, you are more than a friend Kamal, bayan abinda ya faru da su Mummy na daina trusting duk wani friendships, na daina yarda da kowa da komai saboda ban taba ganin irin amintar su ba. Sannan abinda ya faru tsakanin Daddy da Barrister Matawalle ya kara tabbatar min da babu abokan gaskiya a duniyar nan. Amma banda irin ka Kamal, kai na daban ne."

"Kana mantawa baka saka sir a farkon sunan, ko kana so ka kwana a guard room ne?"

"Sorry Sir.' ya matsa baya ya sara masa sukayi dariya a tare

"Kaje ciki, zanje an dawo, we have alot to talk about akan case din, kafin na yi maka handing over na dukkan evidence din plus wanda na karba a wajen ka."

"Ok Sir, duk yadda kace haka za'a yi."

"Duk abinda nace? Kayi alkawari?"

"Eh nayi, anything."

"Ok, ka kira Raihana a waya."

"Me? Noo I can't me yasa Zan kirata?"

"Yanzu kace anything, so dole kayi."

"Please banda wannan, zanyi komai amma banda wannan."

"Hadda shi, call her and apologies again."

"Not now gaskiya, I'm sorry."

"Ok! Bari naje, ka koma ciki."

"Ok." Ya matsa daga jikin motar suka ja yana kallo har suka fita daga gate din sannan ya juya ciki yana jin sa wani irin sakayau kamar wanda kaya ta makalewa a makogwaro ya samu nasarar zare ta.

  

****Da farko Hajiya Zeenat ta dauki abun wasa dan tayi tunanin normal yan sanda ne suka kamota sai data ganta a office din DSS sannan jikinta ya soma rawa tasan tabbas ba wasa a lamarin su. Bata taba hasaso wannan ranar ba, bata kuma taba tunanin duniya zata juya mata baya haka ba, komai da take yi a cikin tsari da plan take yin sa abinda ya saka take nasara a duk abinda tasa a gaba, sai dai wannan karon ta gama tabbatarwa karyar ta kare bata da kowa dan hatta wadanda take tunanin suna tare da ita ashe duk karya ne. Sun yi outsmarting dinta sunyi wasa da brain dinta kamar dai yadda ta dinga yi da tasu a baya. Laifukan ta masu girma ne idan har zasu taru akanta toh tabbas tasan hukuncin da ya dace da ita shine na kisa, mutum daya ne take da yakinin be juya mata baya ba har zuwa karshe sai dai ta tabbatar daga zarar ya samu labarin kamata shikenan zai cikawa wandon sa iska. SAN Mandawari wanda duk wata nasarar ta da taimakon sa ne dan hatta shari'ar abby shine ya tsaya mata har sukayi nasarar tura shi gidan yari.
   Tana durkushe a k'asan dakin da aka ajiye ta ita kadai. Babu haske ko kad'an gashi an karbe komai nata an saka wayarta ana monitoring duk wata wayar da zata shigo daga daren zuwa wayewar garin yau. Budo kofar da aka yi ne ya bawa haske damar shigowa cikin dakin ta yinkura da sauri daidai lokacin da suka shigo su uku, Kamal ne a gaba sai Lamido sannan Abby a karshe, a gaban ta ya tsaya kamar jiya ta daga kan ta da k'yar ta kalle shi shima ita yake kallo, yana ganin lokacin da ta sauya masa rayuwa a saman fuskar ta, lokacin da suka kala masa sharrin kisa.

***Karar motar Yan sanda ce ta fara isowa kafin su hauro saman su shigo dakin su zagaye shi, kalmar da ogan cikin ya furta a lokacin da yake ce masa "you are under arrest." Ita tafi komai tsaya masa a lokacin ya kasa tantancewa abinda suke nufi da kalmar sai da yaga wani yazo ya damki hannun sa ya zura masa ankwa sannan abun ya shiga dawo masa a kansa.
   Sakkowa sukayi dashi bayan sun dan gama dudduba dakin suka bar wasu cikin yan sandan a dakin hade da likitan da ya karaso a lokacin. Zeenat na zaune a falon ta hada kai da guiwa tana ta rusa kuka tamkar ranta zai fita, Nabeela na daga jikin kujera itama tana kuka sai Aryan da yake kiran mummyn sa a rikice yake gaba daya. Ammy ce ta shigo jin hayaniya a gidan ta tarar da mummunan tashin hankali a take ta yanke jiki ta fadi kasa sumammiya amma Abby yana kallo haka suka fice dashi suka saka shi a mota. Cikin kankanin lokaci labari ya soma zagaye gari anacewa aminin miji yaci amanar mijin bayan yayi tafiya, ya haike wa matar sa bayan nan kuma ya kashe ta har lahira.
    Runtse idon sa yayi yana jin kamar a lokacin komai yake faruwa, yana jin da zai iya komar da hannun agogo baya da sai ya goge sanin da yayi wa Daddy iyakar rayuwar sa, amma duk da haka ba zai manta abinda yayi masa ba, ba kuma zai taba yafe masa ba har duniya ta nade.
  Da niyyar yi mata magana Abby ya shigo amma sai ya fasa saboda baya ko son ganin fuskar ta, juyawa yayi ya bar Kamal da Lamido a dakin daga baya Lamido ya fita jim kadan wasu mata kedaru suka shigo, suka gaishe da Kamal din sannan ya basu umarnin su dan sassamata yayi ficewar sa. Jibgarta suka fara yi sukayi mata likis dan sai da suka farfasa mata jikinta sosai fatar nan me laushi da sheki tayi dud'um nan da nan ta sauya fasali da halitta ta koma kamar ba ita bace Hajiya Zeenat yar gayu me aji da tarin kudi.

***Adam na kwance a gida yana baccin asara bayan ya tabbatar da ya gama hada Aryan da Raihana ya kuma tabbatar zuwa lokacin Aryan ya yi mata korar kare shikenan hankalin sa ya kwanta ya samu damar shekar baccin sa hankali kwance duk da kuwa yana son yarinyar amma haka zai hakura bashi da asara tunda Aryan dai be same mu. Wayar sa ce ta farkar dashi ya daga yana jan tsakin katse masa baccin da yake yi amma abinda yaji a cikin wayar sa sashi wartsakewa nan da nan ya diro dga gadon ya hau neman dogon wandon sa da ya jefar tun a hanya da daddare. Da k'yar ya zura ya fito hankalin sa tashe da mummunan labarin da ya samu na zuwan DSS companyn su suka kuma yi awon gaba da wasu daga cikin securities din dake zaune a gate sannan suka hada da Abdulhakeem da wani abdullahi da yake a office din Adam din. A hanya kafin ya karasa office din ya sake samun labarin da ya sake rikita shi ya sashi chanja alakar motar tasa daga zuwa office din zuwa nearest police station dan tuni labari ya warwatsu a social media an kama Hajiya Zeenat Mukaddas bisa zargin yinkurin kashe mijinta, Alhaji Ibrahim Mukaddas,salwantar da rayukan wasu mutane da kuma wasu manyan laifukan da ta aikata wanda take da daurin gindi daga chan sama. Duk in da Adam yake tunanin zai sameta yaje amma sai ya tarar bata nan, haka ya wuni cur yana zagaye karshe ya hakura da ya gano tabbas daga saman ne aka kama dan be kawo DSS bane ba, kuma ko da ace ya sani bashi da hanyar tunkarar wajen domin bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane ba.

    ****Matsawa Daddyn ya dan soma yi ya dan daga dan yatsan sa kafin ya bud'e idanun sa a hankali, da sauri likitocin suka rufa a kanshi dan dama suna cikin dakin harda Dr Mahfouz da ya iso da safe, sun yi kokari sosai wajen samun daidaituwar numfashin shi saboda irin shak'ar da Zeenat tayi masa bayan ya riga ya gama zama so weak saboda ajiye shi da tayi babu ruwa babu abinci, sun yi kokari sosai wajen samun daidatun amma kuma ya sake komawa wani baccin me matukar nauyi wanda suke tunanin zai yi wahalar gaske ya farka a nan kusa duk kuwa da yana numfashi amma idan har ya kai wasu hours be farka ba, toh tabbas ya shiga coma sai dai wani ikon Allah kuma.
   Dr Mahfouz ne ya samu karfin guiwar yi musu bayani nan da nan Ya Nabeela ta rushe da kuka Aryan kuwa shiru yayi kawai ba tare da yace uffan ba, sai Kamal da yayi kokarin samun karin bayani daga bakin Dr Mahfouz din sannan ya yi kokarin kwantar musu da hankali.

"Zan iya ganin shi?" Aryan yace yana kallon Dr Mahfouz

"Zaka iya, muje." Bin bayan sa yayi suka shiga dakin dake cike da wasu irin na'urori manya manya, daga kofa ya hangi Daddyn a kwance sambal tamkar bashi ba, dan har wani irin dashewa fatar jikin sa tayi kasancewar babu riga a jikin sa an kakkafa masa wasu irin na'urori da suke nuna duk abinda yake fafuwa a jikin nasa.

"Zai tashi Dr?"

"Muna fatan hakan Aryan, amma... Yana bukatar addu'ar ku."

"Ok, Allah ya bashi lafiya."

"Amin ya Allah, in sha Allah komai zai wuce, abinda ya faru shine ta dade tana cutar da shi baa sani ba, akwai wata kwaya da take bashi a ruwa ko lemo da take kashe jikin mutum slowly, shi ta dinga bashi tsawon lokaci sai yanzu damage din ya nuna, so amma muna iya kar kokarin mu akai sannan ko ma sai kun hada da addu'a sosai, we are monitoring his kidneys yanzu haka and we are hoping ya zama babu abinda ya faru dasu."

"Allah yasa."

"Amin Amin."

Shiru sukayi na dan wasu sakanni, sannan Aryan din ya juya ya fita cikin karyewar zuciya.



🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*_SAK'ON ZAFAFA BIYAR GA AL'UMMAR K'ASAR NIJER_*🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

_ASSALAMU ALAIKUM MASOYA MAKARANTA LITATTAFAN ZAFAFA BIYAR JAMA'AR NIJER_

_DIMBIN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI A GAREKU_

_MUN FIDDA TALLA MUN BADA NUMBER DA ZAKU TUNTUBA,TO AMMA WANCAN NUMBER DA ZAKU TUNTUBA BA'A SAMUNTA,A HALIN YANZU GA SABUWAR NUMBER DA ZAKU TUNTUBA DON TURA KATI KU SAMU DAMAR SHIGA GROUP NA ZAFAFANKU BIYAR_

+227 90 16 59 91

*Yan jamhuriyyarmu nigeria kuma😂🇳🇬🇳🇬,zaku ci gaba da pyment ne ta account dinmu na*

Maryam sani
0022419171
ACCESS bank

Ku tura shaidar biya ga

+234 903 318 1070

*Katin waya ko VTU zaku tura ta wannan number*

09166221261


Litattafan dai sune kamar haka

RUMBUN KAYA Hafsat rano

A RUBUCE TAKE Huguma

IDON NERA Mamuhghee

KI KULANI Hafsat xoxo

DAUD'AR GORA Billynabdul


*Muna godiya da zabin zafafa biyar*🤝🤝🤝🔥🔥🔥🔥
*RQ*

     28

****Kwana daya tak da faruwar abun Daddy ya dawo a hargitsa, tuni Hajiya Zeenat ta riga ta juya masa labarin abinda ya faru wanda ya samu komai a baibai. Yadda yake jin tsanar Abby da abinda ya aikata masa me girma ne, musamman video da Hajiya Zeenat din ta aika masa tun a chan din. Be taba tunanin zai ci amanar sa haka ba, dan a duniya ya yarda dashi fiye da yadda ya yarda kansa. Labarin da Hajiya Zeenat ta shirya shine dai yake cigaba da yawo a gare hakan ya kara tunzura daddy yaci alwashin sai ya ga bayan Abby ko da kuwa zai karar da duk abinda ya mallaka.
Barrister Mandawari shine ya shiga shari'ar a lokacin kuma yana da sama sosai dan haka shine ya sauya komai na abinda ya faru ya maida shi kan Abby din wanda dama ya dade yana envying nasa da duk nasarar sa.
Babu wata hanya da suka barwa Abby da zai kare kansa, haka yana ji yana gani suka tura shi prison ba tare da ya aikata komai ba.



***Zaune Ammy take ta hada kanta da guiwa tana kuka sosai, tun bayan da aka karkare shari'ar kuma aka tisa keyar shi zuwa prison ta saddakar da rayuwar ta da ta yaranta ta shiga cikin babbar matsala. Zagaye suke da ita dukkan su, Lamido na tsaye daga saman kanta kasancewar shine babba, Sadiq na durkushe a gabanta sai Haidar da yake rike da hannun karamar kanwar su Raihanawadda take kuka itama ganinAmmyn na kuka ba tare da tasan abinda yake faruwa ba.
  Banko gate din gidan aka yi da mugun karfi, duk suka mike a firgice, kafin su farga har sun shigo ciki, suka shiga watsi da kayansu suna watso musu su waje, dukkan su kukan suka saka da kyar suka kyale su, suka dauki abinda zasu dauka suka fito daga gidan, su kuma suka saka padlock suke datse suka tafi bayan sun watso musu da ragowar kayan nasu waje. A daidai lokacin motar da Hajiya Zeenat ke ciki ya shigo layin, tayi murmushi ganin su a kofar gidan tsaye cirko-cirko, dan dama sun yi magana da Daddy tasan kuma zai aikata komai a yadda yake jin tsana da kiyayyar su a lokacin. Lamido ne ya durkusa ya dauki Raihana da hannun days, dayan hannun nasa ya rike jakar yan kayan su da suka samu suka dauka. Sauran abubuwan na hannun Sadiq da Haidar da ya rike hannun Ammyn suka soma takawa cikin yinkurin barin layin ba tare da sun lura da ita ba ma. Tana hangen su, har suka fice gaba daya daga layin dake dauke da tsirarun mutane suna kai kawo.

"Wannan shine sakamakon duk wanda yace zai ja da Zeenatu!" Tace tana murmushi. Yanzu rayuwar zata dawo sabuwa taci karen ta babu babbaka tayi rayuwa me inganci. Gate din gidan aka bud'e driver ya saka motar ciki ya samu gefe daya yayi parking sannan ya fito da sauri ya bud'e mata kofar, ta fito a hankali ta shiga takawa zuwa balcony din da zai sadaka da cikin gidan.
 
   Kuka Aryan yake sosai yana kiran mummyn sa, Nabila na rik'e dashi tana rarrashin sa amma sam yaki yin shiru, yau kwana wajen arba'in kenan da rasuwar Mummyn, amma ya kasa hakura, babu irin lallashin da ba'a yi masa ba amma kullum sai yayi kuka saboda shakuwar da suka yi da mahaifiyar sa.
Da kallo Zeenat ta bisu cikin zuciyar ta,ta ayyana sune kadai suka rage mata a yanzu, sune kadai matsalar ta. Siririn tsaki taja a ciki -ciki, dole zata bi komai a sannu kafin tayi maganin su. Karasowa tayi da nufin rike hannun aryan din ya fizge da sauri yana matsawa baya.

"Don't touch me!"

Ya fada da karfi yana sake yin baya da sauri

"Aryan nice fa? Aunt Zeenat come here my boy."

Tace tana sake matsowa, cigaba da matsawa yayi yana mata kallon tsana kafin ya juya da gudu ya haye sama. Kallon Nabila tayi wadda itama ita take kallo tace

"Ina Adam?" Ta zame jakar hannun ta tana jan tsaki

"Yana falon Mummy yana kallon cartoon."

"Ok." Tace tana zama a cikin jerin manya manyan kujerun dake zagaye a falon.

"Jeki kawo min ruwa."

Juyawa tayi zuwa kitchen ta dauko ruwa da cup ta kawo mata, ta ajiye,.

"Kije ki dubo yaron nan, dan wannan bakar zuciyar tasa zata iya sakashi aikata komai,yaro karami da shegiyar zuciya kamar fir'auna, sai kace akan sa aka fara mutuwa. Mtsw!"

Taja tsaki tana balle murfin ruwan

Bata ce koma ba, dan ita dama ba me yawan magana bace ba, ta juya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login