Showing 111001 words to 114000 words out of 121037 words

Chapter 38 - RUMBUN QAYA COMPLETE hausa Novel

03 Sep 2024

17346

waje ya zauna suka gaisa sannan Barr Awais ya turo masa file din gabansa yace

"This is a sad news."

"Me ya faru Barr.?" Yaja takardar gaban sa yana dubawa

"Menene ma be faru ba? Mutanen nan ta karfi da yaji suna kokarin sauya dokar nan, ko nace ba sauya ta zasuyi ba, kawai bata aiki ne akan masu arziki."

"Ban gane ba?"

"Duba a hankali." Yace yana mikewa tsaye. Ran Aryan din ne ya baci sosai bayan ya gama karantawa, ya mike shima yana kallon Barr. Awais din.

"Me suke nufi?"

"Zasu bada belinta a zaman da za'a yi next."

"Innalillahi, haka k'asar tamu ta zama? Kisa fa ta aikata,duk shaidu sun bayyana, me yasa zasu sauya komai?"

"Wallahi tallahi, at first da na samu labarin ban yarda ba, sai gashi na samu waya daga Barr namadina ya kuma tabbatar min da zargin da ake yi, yanzu haka kotu ta hana hukumar DSS kama Justice Mandawari duk da dama ya fice daga k'asar tunda aka kama Hajiya Zeenat. Ashe shiri yake yi sosai akai, domin gaba daya saman tasu ce, yana da manya sosai a k'asar nan. Anya wasu alkalan zasu gama da duniya lafiya kuwa? Sune suke Sawa ayi mana kudin goro gaba daya."

Shafa kansa Aryan yayi da ya daure masa tamau saboda abinda yake shirin faruwar wanda be taba kawowa ba, yace

"Yanzu menene abun yi?"

"Dole zamu jira zaman da za'a yi jibi, anan zamu tabbatar da gaskiyar abinda yake yawo akan maganar."

"Ya Allah!"

Ya zauna a hankali ya dafe kansa, me yake shirin faruwa? Dafa shi Barr Awais yayi ya tsaya a gabansa ya dago yana duban sa

"Menene alakar Alhajin ku da Adam?"

"Adam? Babu wata alaka face ta auren mahaifiyar sa da Daddyn yayi."

"Ok, ya shigar da kara kotu ne, yana bukatar kotu ta bi masa hakkin sa a matsayin sa na d'a wajen Alhajin."

"Wannan maganar banza ce."

"Yana da support sosai, dan haka ne ma nake tunanin akwai wani gagarumin abu da mu bamu sani ba, alakar Hajiya Zeenat da Alhaji. Am sorry to say amma akwai abinda mu bamu sani ba."

"Na gaji wallahi, na gaji da duk wannan abubuwan dake faruwa. Inaga zan yi nisa da kowa na bud'e sabon shafin rayuwata. A sanda nake tunanin komai ya wuce a lokacin wani sabon al'amarin yake budewa."

"Ba zaka ce haka ba, dole sai anyi hakuri sannan za'a kai gaci, sannan muna bukatar tabbatar da gaskiya domin a samu yiwa kowa adalci. Sai dai ina da yakinin a yanzu muna da bukatar support din Alhaji, domin a bayanin da na binciko, akwai wani babban al'amari da yayi matukar bani mamaki."

"Menene?"

"Tabbas Hajiya Aisha matar Barrister Nasir tana nan da rai, kuma tana wani waje a killace wanda nake kyautata zaton Alhaji yana da masaniyar komai."

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun."

"But bincike na ne ya sanar dani hakan, bani da tabbacin gaskiyar maganar, ina tunanin Hajiya Zeenat tasan abinda ya faru."

"Ta sani, dan duk abubuwan da ya aikata tana da masaniya itace dai bata bari yasan nata."

"Yanzu me ya kamata muyi?"

"I don't know, ban sani ba wallahi. Kaina ya kulle gaba daya."

"We have to figure out abinda ya kamata if not duk effort dinku zai tashi a waste."

"Ya ma tashi."

Ya mike dan be kuma sai me zai ce ba

"We have to wait zuwa ranar muga abinda zai faru, idan yaso sai muga action din da ya kamata mu dauka."

Barr auwal ya fada yana kallon Aryan din. Be ce komai ba, ya juya kawai ya fice daga wajen. Yana fita suka saka dariya gaba dayan su Barr Awais ya dauki waya ya yi kira sannan ya ajiye yana murmushi.

***Bayan motar ya bud'e ya shige dan gaba daya ya rasa me yake shirin faruwa dashi, wacce irin rayuwa mutanen mu suke yi? Tabbas be yarda da maganar Barr Awais ba, dan duk wani abu ma da yake faruwa dole da saka hannun sa. Shikenan babu wanda zakayi trusting a duniyar nan kowa ya lalace ya zama mutumin banza? Gidan sa ya ce Yahya ya kaishi dan ko magana baya son yi sosai, da k'yar ma ya iya bud'e baki ya amsa masa da in da zai kaishin ganin ya nufi main house din su dashi. Suna isa ya balle murfin motar ya fice ya shiga ciki ko bi takan Baba me gadi da ke masa magana be yi ba, be ma jishi ba kwata kwata saboda yadda hankalin sa baya tare dashi. Be san yadda Kamal zai ji ba, abinda yayi sacrificing dukkan time dinsa akai, cikin dan kankanin lokaci wasu mutane marasa daraja sun lalata komai. Saukin ta daya gaskiyar waye shi ta bayyana ga mutanen da ya kamata su sani din, amma bayan wannan babu wata nasara. Shiyasa tun farko Aryan be so aka yi ta daga zaman nan ba, domin yasan yadda k'asar take ya kuma san mugun connection din Hajiya zeenatun zata iya komai, tunda ta riga ta bar hannun DSS ta koma hannun kotu in da suke da damar yin abinda suke so domin alkalan nan ba kirki ne dasu ba.
Kasa zama yayi ya dinga zagaye a dakin cikin yanayin bacin rai me tsanani. Ji yake kamar ya juyar da rayuwar sa ya chanja ta zuwa wani bangare na daban ba wanna din ba, ya manta kowa da komai ya fara rayuwar sa sabuwa ba tare da kowa a tattare dashi ba.
Karar wayar sa ta dawo dashi cikin hayyacin sa, ya kalli me kiran Kamal ne, yana kallo ta gama burarin ta, ta katse sai kawai ya duka ya kashe wayar baki daya ya juya ya bar dakin.

***Fita sukayi bayan Kamal ya kawo Khadija gidan ya tafi. Ya Nabeela tace su fito suka nufi wani hadadden beauty spa and salon da tayi ma Raihanan booking jiya da daddare. Me wajen kawarta ce shiyasa ma suka karbi Raihanan duk da ana booking ne kusan wata guda kafin nan in dai bridal treatment ake so. Cike da kwarewa receptionist din ta karbe su ta basu wajen zama sannan tayi waya aka kawo musu ice tea kafin ta zo kansu. Kallon wajen Raihana take cike da burgewa kad'an kad'an suna hira har aka ce su taso aka shiga dasu ciki Ya Nabeela kuma ta nufi office din kawarta da tazo saboda Ya Nabeelan amma ba ko yaushe take shigowa ba ma.
Cike da kwarewa aka shiga wanke musu kafa dukan su daga ciki kuma ana shirya kayan da za'a soma mata gyaran jikin na alfarma irin na manyan mata yan kwalisa. Ita aka fara gamawa wankin kafar aka ce ta taso, kafar tayi wani irin kyau da taushi ta dinga kallon kafar kamar ba tata ba saboda yadda tayi kyau kwarai. Ciki aka shiga da ita wadda zata mata gyaran jikin ta soma aikin ta bayan ta sauya kayan ta zuwa rigar da ake amfani da ita idan zaa ma mutum gyaran.
Sai la'asar likis sannan suka gama da wajen dan ma dai akwai ma'aikata itama Ya Nabeela an gyara kai da kafa haka ma Khadijan Kamal. Wani irin kyau fatar Raihanan ta fara tun a yau din kuma a kalla zasuyi kwana biyar zuwa sati daya suna zuwa ta tabbatar idan aka yi kwanakin nan ita kanta ba zata gane kanta ba. Har suka isa gida Khadija na ta koda ta Ya Nabeela na dariya suna zuwa sallar magriba sukayi suka ci abinci. Sosai Raihana ta sake da Khadijan dan tana da sakin fuska da wasa da dariya sosai a dakin da aka bawa Raihanan suka zauna suna hira har Kamal yazo daukar ta. Duk sai taji babu dadi kamar kar ta tafi haka dai ta rakota falon in da Kamal da Ya Nabeela suke maganar Aryan din da kiran da Kamal yayi masa be d'aga ba daga baya kuma wayar tasa a kashe

"Na zata ma zai dawo wallahi."

"Ai yana jin nauyin ki, da dai nine marainin wayon sa. Amma bansan me yasa ya kashe waya ba gaskiya, haka kawai baya kashe waya sai dai idan akwai yar matsala."

"Ko fushi yake na dauke masa matar sa?"

"Anya? Zan dai biya ta gidan na same shi idan yana chan."

"Ok."

Tace a sanyaye. Gaishe shi Raihana tayi sannan ta yi wa Khadijan sai da safe ta juya ciki. Duk sai taji ta kasa nutsuwa da ta ji suna maganar ya kashe wayar sa kuma shiru be dawo ba duk da Ya Nabeelan ce tace kar ya dawo amma ai da wasa take masa.

**RQ**

    49

***Kwantawa tayi lamo akan gadon cikin tunanin ko lafiya? Juye juye ta dinga yi har Ya Nabeela tayi knocking ta shigo ta sameta a kwance ta tashi zaune bayan ta shigo.

"Kin gwada kiran Aryan kuwa?"

Tace tana zama a gefen gadon. Girgiza kai tayi tace

"A ah."

"Call him please, na fara jin babu dadi, ko maida ke zanyi? Wai so nake yadda akayi auren nan urgent a kalla ki samu gatan da kowa ta samu, amma idan hakan zai takura masa gwara ki koma, bana son abinda zai taba lafiyar sa an samu ya fara warewa"

Shiru Raihana tayi bata san me zata ce ba tunda har lokacin nauyin Ya Nabeelan take ji sosai.

"Kira shi kinji? Bari naje naji shigowar Daddyn su Amna xan dawo."

"Ok tam."

Tace a sanyaye ya Nabeelan ta fita ita kuma ta dauki wayar ta, ta yi dialing number tasa. Kunna wayar sa kenan bayan ya tashi da k'yar daga wajen da yake zaune tun da ya idar da sallar isha. Ji yayi yana son kiran ta a kalla zai dan ji saukin abinda yake ji din a zuciya da ruhin sa. Sai ga kiranta ya shigo a daidai lokacin. Kallon number yayi kafin ya daga cike da mamakin co-incidence din da aka samu dan har ya hau kan number tata zai kira kiran ta ya shigo masa. Mikewa yayi sakale da wayar a kunnen sa ya koma saman gadon ya kwanta rigingine yana jin tayi sallama ya amsa a chan k'asan makoshin sa. Shiru ya biyo bayan amsa sallamar tasa saboda rashin sanin abinda zata ce masa, muryar kadai ta isa ta tababtar mata ba lafiya ba.

"Ya Nabeela ce tace na kiraka dama."

"Ok." Yace ya sake yin shiru. Sai ta rasa me zata ce masa kuma. Tana jin yadda yake sauki numfashi da dan karfi dan tana jin sound din sa. Kusan minti biyar suna a haka sai kudin ta ya kare. Kiran ya biyo a take ta d'aga jikin ta a sanyaye.

"Raihanaaa." Ya kira sunan ta cikin jan sunan. Har cikin kwakwalwarta taji yadda ya kiratan.

"Kina so na?"

"Na'am?"

"Tell me, kina so na? Zaki zauna dani duk tsanani duk runtsi? Ba zaki gujeni ba?"

"Menene ya faru?"

"Just answer me please, did you love me?"

Hadiye yawu tayi jin yadda ya tsare ta, muryar sa kuma a chunkushe alamun ba da wasa yake ba. Sake maimaitawa yayi a karo na uku ta tashi tsaye tana tattaro kalaman bakin ta da take jin sun mata nauyi tace

"Yes, ina sonka. Amma me ya faru? Me ya same ka?."

Wata irin ajiyar zuciya ya sauke me karfi sannan ya k'ara gyara kwanciyar sa ya dora wayar a saman kirjin sa a hankali yace

"Nagode sosai, babu abinda ya faru inaso kawai na sani ne."

"Ok, but muryar ka..." Katse ta yayi yace

"Missing dinki nake, inaso na ganki. Nazo?"

"Eh kazo." Tace zuciyar ta na wani irin harbawa da sauri.

"Ok, I'm coming right away."

"Ok." Tace a sanyaye suka ajiye wayar. Sai ta kasa tashi daga in da take zaune kirjinta na cigaba da dukan uku uku, yanzu idan yazo ya zatayi dashi? Daga jin yadda yake magana rigima kawai yake nema,kar Ya Nabeela tace ma so take ta tafi, amma kuma ya zatayi masa? Ba zata iya hanashi zuwan ba dan tana son ganin shi ta kuma san halin da yake ciki.
   Dawowa Ya Nabeela tayi dakin ta tambaye ta sunyi waya? Eh tace mata amma sai ta kasa fada mata yace zaizo yanzu. Sai da safe tayi mata ta ja mata kofar ta nufi part din Dr Farouk saboda lokacin kusan goman dare.
  Da kansa yake driving din duk da jikin sa babu kwari sosai amma kuma yasan idan ya ganta zai samu wani kaso daga cikin energy din nasa, duk da yasan Ya Nabeela zata masa tsiya amma kuma bashi da wani option idan ba zuwan ba, yana so ya rik'e ta a jikinsa yana shak'ar kamshin jikinta me dadi da yake saka shi manta dukkan damuwar sa. A waje yayi parking motar ba tare da ya shigo ba, ya kwankwasa kad'an gate man din ya leko ya ganshi sannan ya bud'e masa da sauri. Haske sosai a harabar gidan ba zaka ce daren yayi har haka ba. Suka gaisa ya zaro wayar sa ya kira Raihanan ya ji tana ina. Sai da kirjin ta ya buga da karfi da taga kiran nasa wanda ta tabbatar da ya karaso kenan. Dagawa tayi jiki a sanyaye yace tana ina, ta fada masa tana dakin sa. Murmushi yayi da ya tuna da kofar baya ta dakin da yake amfani da ita idan baya son shiga cikin gidan. Ce mata yayi ta bud'e masa back door din, ta tashi ta bud'e masa ya shigo ya maida kofar ya rufe. Taku daya tayi da nufin komawa tsakiyar dakin ya riko ta da sauri ya sakata a jikinsa yana sauke nannauyar ajiyar zuciya. Boyayyar ajiyar zuciya ta sauke itama dan ba karamin nutsuwa take ji ba a duk lokacin da ya rungume ta a jikin sa. Hancin sa ya kai saman wuyan ta ya shiga shinshinawa a hankali kamshin da jikin ta ke fitarwa na gyaran jikin da akayi mata ya shiga fizgar shi. Hadadden kamshi ne me aji da sanyin dadi wanda be taba jin irin sa ba.

"I love this scent!"

Yace yana kara kai kansa sosai ya zura a jikin wuyan nata wanda take jin hakan tamkar tafiyar tsutsa. Kankame shi tayi yayi murmushi yana raba jikinsa da nata ya zaunar da ita sannan ya durkusa a gabanta ya rike hannun ta.

"Wani abu zai faru dani wanda ni kaina bansan menene ba, abu daya na sani shine, sai na cika alkawarin da nayi wa kaina, ko da kuwa hakan na nufin katsewar numfashi na. Ina fatan zaki zauna dani duk runtsi duk wuya, ba zaki gujeni ba."

gid'a masa kai tayi idon ta na cicikowa da kwalla. Hannu ya kai ya share mata saman idon yana girgiza mata kai

"Karki zubar da hawayen ki akan abinda be chanchanci zubar su ba, zan yi komai da kaina ba tare da kowa ba, kuma sai na tabbatar da duk wanda yake da hannu ya fuskanci hukunci me tsanani."

"Su waye menene suka yi maka?"

"Karki damu, just pray for me."

"Tom, please karka saka kanka a wani abun dan Allah."

"Ba abinda zai faru kinji? Na miki alkawari amma karki sanarwa kowa, sirri ne tsakanin mata da miji."

"In sha Allah."

Tace a sanyaye. Mikewa yayi daga gabanta ya zauna a gefen ta yana jawo ta jikin sa. Ya lumshe idon sa yana jin saukin abinda yake ji a ransa na bacin rai. Abinda ya rasa a baya da har ya bari bacin ransu yayi masa mummunan tasiri a rayuwar sa. Amma banda yanzu da yake jin yana da abu me muhimmanci da zai yi protecting, yana kuma da burin tara family nasa na kansa. Yayi musu irin tarbiyyar da yake so. Su rayu cikin so da kaunar junan su.
Ba zai kyale duk wanda ya shiga gonar sa ba a wannan karon, idan har ya tabbatar da Barr Awais amanar su suka ci, sai yayi maganin su da duk wanda suke yiwa aiki, zai aje rigar hukuma ya saka wadda ta dace dasu zai kuma yi amfani da abinda Hajiya Zeenat din take ji da takama dashi wato dukiya wajen yakar ta.
    Baya yayi dasu suka kwanta akan dan madaidacin gadon da yafi kama da na mutum daya, ya kara jawota sosai jikinsa har kusan rabin ta na saman sa. Hannun sa ya kai saman gashin ta yana shafawa a hankali, yana sauraron heart beat dinta take tafiya kusan daidai na nasa bugun zuciyar.

"Inason babies Raihana."

Da sauri ta yinkura zata tashi ya matse ta yana murmushi

"Ba yanzu nace ba, kawai nace inason yara ne, da yawa da yawa kinga mu bamu da yawa, ina sha'awar naga mutum da yara masu yawa."

"Ni ba ruwana." Tace tana turo baki.

"Da ruwanki, kece zaki bani dukka kuma."

"Ka tashi ka tafi kar Ya Nabeela ta dawo."

"Um um ba in da zani, idan tazo ma shikenan kinga"

"Dan Allah ni dai ka tafi."

"Kora ta kike?"

"Eh." Tace tana tashi zaune.

"Ba in da zani, ai daki na ne nan din."

"Yanzu ai ya zama nawa."

"Aro dai aka baki."

"Toh ka tashi ka tafi." Ta ture shi ganin yana matsowa gareta.

"Kinaso in tafi?"

"Eh."

"Ok zan tafi, amma har yanzu b3 na a low yake, dazu ma 30% kawai yayi kuma ya zuke nan da nan, yanzu 50 nake so yayi kawai sai na tafi."

"Toh ba sai ka saka charjin ba, ai akwai wuta." .

Tace pretending bata gane me yake nufi ba. Murmushi yayi yana mata wani kallo me dauke da ma'anoni. Bakin ta da yake maganar ya bawa attention dinsa sosai. Kunya taji ta rufe fuskarta da sauri ganin yadda yake kallon ta.

"Kinga yanzu ma ya koma 0, anya ba bari zanyi yayi 100% ba kawai?"

Mikewa tayi ta hau yunkurin sauka daga gadon cike da dana sanin cewa yazo, ita wai ta tausaya masa ne amma ashe ba haka bane ba. Riko ta yayi ya dawo da ita kan gadon ya yi mata rumfa da jikinsa ya dora mata baki daya nauyin sa.

"Kin yarda in samu full charge din?"

Girgiza masa kai tayi alamar a'ah da sauri tana matso kwallar jin yadda ya danne ya hanata kwakkwaran motsi.

"Dan Allah kayi hakuri."

"Dan Allah kiyi hakuri." Ya ciji lips dinta na k'asa ya kwaikwayi muryar ta. Runtse idonta tayi ganin ya saka kansa a jikinta yana bin jikin nata da wani irin salon kiss. Jikinta ne ya dauki rawa ta rikice tsoro ya shigeta tayi kokarin ture shi amma ta kasa kwata kwata, numfashin sa yake sauke mata yana cigaba da abinda yake matan yana kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login