Showing 9001 words to 12000 words out of 121037 words

Chapter 4 - RUMBUN QAYA COMPLETE hausa Novel

03 Sep 2024

17329

fa, bana so ki damu ne, kuma ba wani ciwo naji ba, dan kurjewa nayi sai hakan ma kuma ya zama alkhairi."

"Kin dai girma Raihana, ai shikenan, ki kula da kanki dan Allah."

"In sha Allah Dadah nah, ina Babbo? Da Hamma Hydar da Hamma Lamido?"

"Bakya kiran su a waya ne?"

"A ah ina kiran su, kawai wai dai."

"Suna lafiya duk sun fice sai ni kwal a gidan."

"Allah sarki Dadah na, dole kiyi missing dina wallahi."

"Ke ai naga kamar baki ma damu ba, duk wannan kawa zucin gidan tunda kika taho nan shikenan, bansan me Maimunatu take baki ba da har kika manta mu haka."

"Kai ina, ai ban manta ku ba wallahi, kullum da daddare sai na tuno gida."

"Ba wani nan."

"Allah kuwan da gaske."

"Toh yayi, kije ki huta naji an ce yanzu kika dawo, saura kuma ki dinga wasa da cikin ki yadda kika saba rashin son cin abincin nan."

"In sha Allah Dadah, shikenan zan kira anjima idan su Hamma na sun dawo."

"Haa nannde wonnde."

"Haa gonngo."

Tashi tayi ta kaiwa Addah Maimuna wayar ta dan ta tashi ta shiga ciki, sannan ta wuce dakin su ta cire kayan jikin ta, ta dan kwanta kafin anjima ta tashi tayi wani abun dan sai da ta fara lekawa ta kitchen taga an gama komai dama dai tasan da wuri ake gama girkin rana a gidan saboda yara yan makaranta da ake kai musu.

***Washegari ta sake shiryawa kamar jiya sai dai yau ta dan makara, a gaggauce ta shirya ko breakfast bata tsaya tayi ba, ta tafi. Tana zuwa ta ajiye jakar ta kenan Zainab ta shigo office dinsu tace tazo in ji oga, yadda tayi maganar fuskar ta a hade ba walwala, yasa Raihana ta zata wani laifin tayi, sai dai bata gane wanne ogan ake nufi ba sai da taga sun nufi hanyar office din oga kwata -kwatan, sai a sannan jikin ta ya saki dan bata son duk wani abu da zai hada ta dashi, wani irin kwarjini yake mata.
Siririn medicated glass ne sanye a idon sa yana kallon computer, shigowar su ya saka shi dagowa ya kalle su kad'an sannan ya cigaba da abinda yake yi

"Sir gata."

"Ok you can go." Yace dai ya jawo drawer dake jikin table dinsa ya shiga dubo abu, juyawa Zainab tayi cikin yanayin da ya saka Raihana a tunani, sai ta lura tamkar zata bangaje ta sanda take juyawa amma kuma sai tayi saurin dauke tunanin hakan tayi mata uzuri kila haka yanayin ta yake ko kuma dai bata lura ba.

"Ina kwana?" Tace daga in da take tsaye ta hade hannayen ta, ta damke su waje daya.

"Kina lafiya?" Yace mata bayan ya ciro abinda yake so ya ciro din

"Alhamdulillah." Ta amsa tsoron da take ji yana raguwa jin ya tambaye ta tana lafiya, sai kuma fuskar sa da take a dan sake ba kamar ranar ba, hakan ya bata kwarin guiwar sake matsowa ciki sosai dan da daga dan baya baya ta tsaya

"Aiki nake so kiyi min, ki dauki wannan takardar kije ki shigar da duk wani information a cikin system din, kin iya excel?"

"Eh na iya sir."

"Ok, ki yi shi kamar yadda yake anan sai ki tura min komai ta wannan email din da yake k'asa , duk abinda baki gane ba kizo ki tambaye ni, I need it zuwa 12."

"Ok sir." Ta dauki takardar ta juya ta fita.

Zaman ta kenan ta kunna system din wayar Abdulhakeem tayi kara, ya daga taji sanda yake cewa ok sir, ya katse sannan yace

"Oga Aryan yana kiran ki."

"Ni kuma? Yanzu na dawo fa."

"Toh dai yana kiran ki." Yace yana dariya ganin yadda ta zaro ido

"Ni wallahi bana son zuwa."

Ta fada tana mikewa, bata ma san ta fada ba sai da taji Abdul din na mata dariya

"Hala dai oga yana miki kwarjini, muma duk kusan hakan ce amma wallahi he's very very nice."

"I don't think so."

Tayi gaba tana jin suna mata dariya shi da dayan da bata gama rike sunan sa ba. A kofar ta tsaya kamar ba zata shiga ba, ta dan juyo sai taga Zainab tana kallon ta, juyar da kanta tayi ta kwankwasa sannan ta tura kofar, babu kowa a ciki, sallama tayi a hankali jin shiru ya sakata juyowa da nufin komawa, sai gashi yana kokarin shigowa, saurin ja baya tayi dan kansa tsaye ya shigo saura kiris su yi karo, kamar be lura da abinda ya kusan faruwa ba ya wuce ya zauna.

"Sir gani."

"Na ganki ai."

Sai da ya gama ja mata aji a yadda ta lura sannan yace

"A cikin rules dinmu, babu fashi sai ta zama dole , shima sai ka rubuto email na dalilin rashin zuwan ka, sannan kullum idan kazo sai ka dauki attendance na time din da kazo da kuma time din da ka tafi."

"Ok sir."

"Zo ki saka hannun ki anan yayi capturing." Ya nuna mata wata na'ura akan desk dinsa, zuwa tayi ta dora thumb din ta, amma sai yaki dauka, be kalle ta ba yana jin dai tana ta sakawa tana cirewa.

"Come to my office." Taji yace a waya kawai, sai kuma aka shigo.

"Sir gani."

"Zo ki rike hannun ta yadda zai yi capturing naga kamar bata iya ba."

Yace ya mike ya fice daga office din, wani abu ne ya tokare mata wuya, ta tsaya kawai Zainab din ta matso da nufin kama hannun ta, saurin hanawa tayi tace

"Zan iya da kai na." Wani kallo Zainab din tayi mata sai kawai tayi tsaki ta juya ta fice.

Gefen rigar ta, ta saka ta goge hannun sosai sannan tayi bismillah ta saka, sai gashi yayi, ta cire ta saka dayan hannun shima ya dauka. Murmushi tayi dan a rayuwar ta, ta tsani ace bata iya abu ba, duk yadda zatayi taga ta iya kuwa sai ta koya. Daga shi har Zainab din ta lura yan rainin hankali ne, itace secretary dinsa daga gani shiyasa komai sai yace ita.

Tana tsaye ya dawo ciki rike da tarin wasu takardun, ya kalli na'urar ganin tayi sai ya dauke kansa daga kai yace mata shikenan, thank you tace masa tayi gaba cike da jin haushin yadda yake abubuwan sa, gashi daga gani yana da son aiki dan ko da yaushe cikin yin sa yake yi kamar wani agogo.


****Karfe sha daya da mintuna hamsin ta gama aikin da ya sakata, ta tattare dukka ta tura masa sannan ta tura copy din a nata email din. Kafarta ta dan mike da tayi mata tsami saboda zama ga bayan ta da ya gaji dan kusan awoyin ta uku chur a zaune tana aikin, bata so ya sake kiran ta kuma shiyasa tayi iya kokarin ta, ta yi masa aikin daidai yadda tasan zai yaba, yau gaba daya bata ga Kamal ba, kamar ma be zo office din ba, dan tabbas da yazo zata ganshi ko taji wucewar sa.

A gaggauce ya fito bayan ya karasa tattare dukkan aikin da yasan Daddy zai gani idan ya shigo, karfe daya da rabi jirgin su zai sauka, gashi yace masa lallai ya je ya dauko shi, duk da hakan yana cikin sharudan Daddyn amma sam baya so, musamman tafiya da zata hada shi da Adam waje daya, sannan idan yaje din abinda zai gani ba zai masa dadi ba, amma haka zai hakura dan yasan duk hanyar da zasu bi su hanashi aiwatar da abinda yake niyya zasuyi ne, dan haka ne ma ba zai basu kofar hakan ba.
Waya suke da Kamal yana kokarin fita daga cikin building din, a daidai lokacin itama take kokarin fita dan dama sha biyu tayi zata dinga tafiya dan ba zata iya wunin da suke yi ba, an ce sai 4 suke tashi amma gaskiya ita tafiyar ta zatayi.
Bata ganshi ba kawai tafiyar ta take yi, shima kuma wayar da yake ta dauke hankalin sa baki daya, yana yi masa bayanin abubuwan da zai karasa idan ya shigo shi daga airport ba zai dawo office din ba sai gobe. Driver daddy ne zai dauke su zuwa airport din, Adam tuni ya fito yana zaune a gaban motar yana latsa wayar sa, daga kansa yayi da niyyar ganin ko Aryan din ya fito sai ya hange ta tana tafiya hanyar gate, da gaske yarinyar tayi masifar yi masa, kuma duk yadda zai yi sai yayi ko ta hanyar amfani da Mom dinsa ne ganin ta bashi dama, ba aure bane shi yanzu a gaban sa ba duk da ya isa ace daga shi har Aryan din sun yi aure, amma tabbas yana jin zai iya auren ta ko dan ma Daddy ya sake yarda dashi tunda an ce cikar kamalar mutum itace aure. Balle murfin motar yayi ya fito, fitowar sa ita ta ankarar da Aryan ya kalli wajen da ya nufa.

"Ina zata?" Ya tambayi kansa da kansa.

Wani kallo yaga Adam din yana mata duk da baya jin abinda yake cewa, yanayin yadda ta nuna tamkar ta kosa da maganar da yake mata, sai a sannan ne yayi mata kallo sosai, har yaso ketara kallon da shari'ah ta yarje ma mutum, tsaki ya samu kansa da ja, baya son Adam yana shiga duk wata harka da ta dangance shi, sannan bazai taba yarda mutum irin Adam yayi mu'amula da ita ba, duk da ba wai ya santa bane ba, amma dai tunda a karkashin office dinsa take toh dole zai yi protecting dinta daga mutane irin Adam, shaidanun zamani. Motar ya bud'e ya shiga sannan yace wa driver ya karasa wajen da Adam din suke tsaye, suna isa ya bud'e murfin kofar sannan yace

"Raihana, come in."

Kallon sa tayi, yanayin fuskar sa da take a gimtse babu ko fara'ah daya, yanayin sa yayi mata kama da na wanda yake cikin tsananin bacin rai, ji tayi kamar ta juya ta zura da gudu dan yadda yake kallon ta

"Bata shiga motar strangers, ko pretty?" Adam yace yana mata murmushi, hakan ya sake kular da Aryan ya kuma tabbatar da zargin sa akan Adam din

"Kuna bata mana lokaci, I said get in malama." Ya yi maganar a dan zafafe

Gefen mayafin ta ta damke da hannun ta, idanun ta suka ciciko, ya dauke kansa tamkar be gani ba, a hankali ta saka kafarta cikin motar, ta zauna daga karshen kujerar sosai sannan ta sauke kanta k'asa. Wani murmushi Adam yayi kawai, be ce komai ba, ya bud'e gaban motar ya zauna sannan driver yaja suka bar wajen.

Shiru ne ya biyo bayan hakan a cikin motar, baka jin motsin komai tamkar babu kowa a ciki, hannu Adam yasa ya kunna Bluetooth din motar yayi connecting da wayar sa, hakan ya dauke shirun da sukayi ya maye gurbin sa da wakokin kudancin Nigeria. Daidai wani round about Aryan yace su tsaye, driver ya faka sukayi shiru, bayan mintuna biyar Kamal ya karaso a motar sa, yayi parking a bayan su sannan yace yazo, shi da Shahida kanwar sa da hajiyar su ne, daga asibiti suke abinda ya hanashi shigowa yau kenan sun kai Hajiya taga likita, bud'e kofar yayi sannan yace ta fito, ta fito a sanyaye suka nufi motar Kamal din, har kasa ya durkusa ya gaida Hajiyan ta amsa sannan ta saka musu albarka, suka gaisa da Kamal sannan yace ta shiga motar, shiga tayi ta zauna a gefen hajiyar ta gaishe ta. Shi kuma ya juya ya koma motar su, suka bar wajen.


LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+22799643131

Books biyar  1250CFA
Books hudu  1050CFA
Books uku  850CFA
Books biyu  650CFA
Bookk daya  450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
RUMBUN QAYA*

 
           Page 6

©® *_Hafsat Rano_*

ZAFAFA 2023🔥🔥🔥🔥🔥

_____________

_*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_

_*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._

_*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._

_*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_.

_*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._

_*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._

_*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_

_*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._

_*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._

*_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._*.

•••••Suna isa airport din daidai lokacin jirgin ya sauka, tun kafin ma Aryan ya samu damar fita Adam ya fice daga motar cikin yanayin bacin ran abinda Aryan din yayi masa, sai dai tunda ya nufi wajen da Daddyn yake ya saki fuskar sa kamar babu abinda ya faru, ya kuma tabbatar da idan Daddyn ya fito dashi zai fara arba kafin Aryan din ya kuma san hakan me zai kara zama a gareshi.
  Hango fitowar su yasa shi nufar su da farin cikin sa, tare Daddyn yake cikin tagawar manyan abokan kasuwancin sa. Cike da tsananin girmamawa da kankan da kai ya tare su da gaisuwa har da durkusawa chan kasa, wanda hakan yake kara Samar masa fada a zuciyar Daddy dan shi mutum ne me matukar son girmamawa da sanin ya kamata. Shiyasa a ko da yaushe suke samun matsala da Aryan dan shi duk irin wadannan abubuwan be iya su ba sam. Kamar yanzu ma sai gashiya nufo su yana tafe yana amsa waya sai dai yana cike da wani irin haiba da kwarjini da kowanne lokaci yake samun galaba akan Adam din da duk kudure-kuduren sa. Ganin sun hango shi sun ya saka shi katse wayar da suke da Ya Nabila ya nufe su cikin tafiyar sa. Idanu duk suka zuba masa har Adam din hakan ya sakashi jin ya takura sosai, ya dan rissina kad'an ya gaishe su suka amsa babu yabo babu fallasa, hakan ya dan bata ran daddy ganin irin tarbar da sukayi wa Adam ba irin ta Aryan din ya samu ba, hakan kuma baya rasa nasaba da shi yadda Adam din yazo musu fuskar sa a sake cikin iya mu'amula da mutane.
  A wajen shiga mota Daddy suka rabu da sauran, Adam ya karbi key din driver da ya kawo su ya shiga wajen tukawa yana jaddada shine zai kai Daddy gida, dariya sukayi shi da Daddyn dan shi komai Adam din yayi yana burge shi sosai yasan duk abinda zai ya faraanta ran Daddyn, a dole ba dan Aryan yaso ba, ya shiga gaba gefen sa ya zauna shi kuma Daddy ya hakimce a baya yana cigaba da nazarin halayen Aryan din duk da ba wai yau ne karo na farko da ya fara fuskantar hakan daga gare shi ba, amma kuma a yau sai yaga ya sauya masa sosai ya nuna matukar yanayin damuwa a tattare dashi, yasan damuwar sa bata raba dayan biyu akan abinda ya kwallafa rai ne yake ganin idan be cimma ba tamkar bashi da wani amfani a duniyar ma baki daya, dalilin sa kenan na sake komawa karatu a karo na uku yayi karatun da yake da yakinin samun cikar burin sa ta wannan hanyar, sai dai katse shi da Daddyn yayi ya kuma gindaya masa sharuda masu yawan gaske ciki har da dawowa yayi aiki a karkashin company sa wanda hakan yayi matukar takure shi, sai dai a duk wani abu da Daddyn zai saka shi ko ya gindaya masa baya taba iya ketare shi, shi din me matukar biyayya ne a gareshi ko da kuwa babu wata alama da take nuna soyayyar sa ga mahaifin nasa dan har kwanan gobe yana cikin mutanen da yake zargi wajen salwantar da rayuwar mahaifiyar sa, me tsananin so da kaunar sa.      Shiyasa komai ya tsaya masa chak dan yana rayuwa ne kawai a karkashin ikon sa ba wai dan yana so ba, sai dan cika umarnin Allah da Yace lallai ya zama wajibi 'yaya su yiwa iyayen su biyayya akan duk abinda be sabawa Allah ba.
   Hirar dake wakana tsakanin Daddyn da Adam din yake sauraro cike da kulawa Daddyn yake saurare shi yana kuma amsa masa daidai kamar yana hira da abokan sa makusanta. Aryan ya kan yi mamaki idan yaga yadda Daddyn ya sake da Adam ya bashi dukkan yarda fiye da kowa a duniyar nan, yayi matukar yarda dashi har ta kai baya ganin iyawar kowa sai ta Adam din. Duk da dai shi Aryan zai iya rantsewa da wayon sa ba zai iya tuna wata hira doguwa da ta hada shi da Daddyn ba, dan baya jin akwai wani abu da zasu iya tattaunawa akai idan har ba maganar mahaifiyar sa bace ba, tun da kuma yaki zancen yace masa baya so, tun daga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login