Showing 63001 words to 66000 words out of 121037 words
tana kokarin kama staircase din sai ta dakatar da ita
"Ki turo min Adam."
"Toh." Tace ta cigaba da hawa a hankali zuciyar ta na mata zafi.
A bedroom din Mummy ta same shi, ya kwanta lamo a saman gadon ta yana kuka k'asa -kasa, da sauri ta karasa ta dagoshi ta rungume shi suka sake fashewa da kukan a tare, Sun dade a haka kafin ta cika shi ta shiga share masa hawayen dake bin fuskar sa
"Ka daina kuka kaji? Idan kana kuka kanka zai yi ciwo."
"Ni Mummy!"
"Zata dawo ne, very soon kaji? Amma sai ka daina kuka ka daina yiwa Anty Zeenat rashin kunya."
"Bana son ta, I hate her. Muguwa ce sosai ita ta dauke min mummy ta."
"Shsshh!" Ta rufe masa baki da sauri tana kallon kofar da ta bari a bud'e,tashi tayi da sauri ta rufo ta sannan tace
"Don't say that again kaji? Ka daina fada kar Daddy yaji."
"Na daina." Yace yana kwanciya a jikin ta.
"Good boy."
Tace tana share kwallar da ta zubo mata. Tunowa tayi da sakon Kiran Adam ta mike da sauri ta fita, taje ta same shi yayi kacha-kacha da falon ya zubar da ledojin munch-it da caprison ko ina.
"Anty Zeenat na kiran ka."
"Ta dawo?" Yace yana tashi daga riginginen da yayi yana kallo
"Tana falon k'asa."
Fita yayi ta jawo karamin dustbin ta kwashe komai da ya zubar sannan ta share wajen tas ta goge. Muryar Daddyn su taji a falon sa na sama, tayi saurin komawa bedroom din Mummy ta rike hannun Aryan ta dawo dashi dakin sa, sannan ta rufe dakin Mummy din ta sauko kasa.
Fada Daddyn ya hau ta dashi ta in da yake shiga ba tanan yake fita ba, bata san takamaimai laifin da tayi masa ba,sai da ya gama banbamin tana durkushe sannan ya hau kwala wa Aryan kira, kin sakkowa yayi yasa key a kofar dakin nasa yana jin Daddyn yayi ta kiransa har ya hakura ya kyale shi.
***Gida Aryan ya koma da safe bayan Ya Nabeela tazo asibitin da nufin ya shirya. Dakin sa ya shiga da ya watsa ruwa ya sauya kayan sa ya fito ya tarar da Adam yana jiransa a falo.
"Me yake faruwa?" Ya tambaya yana kallon Aryan din da yanayin sa
"Baka sani ba?"
"Eh ban sani ba, nake so ka sanar dani."
"Da yake ka ajiye ni ne ko? Toh ban sani ba."
"Please Aryan, ba fada nake so ba, just tell me, me yake faruwa ina Mom dita?"
"Ban sani ba, dan bani da lokacin batawa, kawai dai mu hadu a kotu, koma me yake faruwa idan kaje chan zakaji."
Wucewa yayi da nufin sauka Adam din ya riko shi da sauri
"Aryan dan ALLAH! Help me."
"Me kake so nace maka Adam?"
"Me ya faru?"
"Kamar yadda ka samu labari haka ne,kuma DSS ne sukayi kamen bayan hakan bansan komai akai ba, ina tare da daddy a asibiti."
"Bashi da lafiya?" Ya fada cike da tashin hankali
"Eh." Kawai yace cike da kosawa,ya karasa sauka. Da sauri Adam din yabi shi suka sauka a tare yana shiga mota shima ya shiga tasa yabi bayan Aryan din.
***Raihana na zaune tare da Daadah tana gyara mata kanta, suna yar hirar su, hankalin ta baki daya yana kan hirar da suke yi bata ji ringing din da wayarta take yi ba har sai da Hydar da ya shigo lokacin yace
"Ba wayarki bace ba?"
Sai lokacin ta ankara ta tashi da sauri ta dauki wayar sai dai sunan da ta gani akan screen din wayar ya saka ta jin kamar an sare mata kafarta, tayi sakale da wayar a hannu ta saci wajen da Hydar yake tsaye yana kallon ta
"Aryan ne?" Yace yana kafe da ido
Daga masa kai tayi alamar eh
"Share shi please, me zai ce miki?"
"A ah Aliyu, barta ta daga, ki daga mana kiji mai zai ce."
Daadah tace
"Daadah me zai ce mata? Mutumin da ya yi mata kora irin ta kare, kinji tsawar da yake mata ne? Idan tana da hankali ai ba zata dauki wayar sa ba."
"Duk naji wannan, a kalla dai taji me zai ce mata ko?"
"Ko me zai ce ma dai, muna nan akan bakan mu gaskiya, babu wata alaka da zata sake hada mu dasu, babu."
"Toh wai Hydar duk hakilon nan da kake, shi Aryan din yace yana son Raihana ne?"
"Ke Raihana yace yana son ki ne?"
Girgiza kai tayi tace
" A ah."
"A ah toh, ba abinda kake tunani bane ba, maza kirashi kiji dalilin kiran nasa."
Juyawa kawai Hydar yayi ya fice be sake cewa komai ba.
"Kinsan zuciya irin ta Hydar."
"Daadah wai dama Hamma Hydar yasan Aryan ne?"
"Hmm.. ya sanshi Raihana."
"Ok,wai menene yake faruwa? Naji tun ranar yana ta jaddada babu alaka a tsakaninmu dashi, kuma naji suna maganar da Abby ma har naji ya dau zafi sosai akai."
"Labarin na da tsawo Raihata, amma je kira shi kiji me yake faruwa sai ki dawo na baki labarin komai, be kamata a bar ki a duhu ma musamman tunda yanzu kema kin shiga cikin abun."
"Bari muga ko zai sake kira Daadah, ko mistake yayi dama ba kiran zai ba."
"Wa yace miki? Kira shi dan Allah wallahi tausayi yake bani."
"Kai Daadah, kamar kin sanshi?"
"Jeki dai ki kirashi kizo."
"Ok." Tace ta wuce dakin ta. Ta samu gefen gado ta zauna sannan ta shiga kan number Aryan din kirjinta na bugawa kamar zai fito, wani abu me kama da tsoro take ji musamman sanda wayar ta fara ringing sai taji kamar da bugun zuciyar ta yake tafiya.
"Hello." Yace cikin husky voice dinsa wanda yasa ta yin tsam
"Helloooooooo Raihanaaa?"
Yace yana tashi daga wajen da yake zaune, har cikin kwanyar kanta taji yadda ya kira sunan nata, karo na farko kenan da ya taba fadan sunan ta amma sai taji sunan yayi sounding wani iri kamar ba nata ba
"Helloooo." Ya sake maimaitawa
"Hello." Tace a gajarce
"Kina jina?"
"Umm."
"Ok, kina lafiya?"
"Lafiya Lou."
"Ok, sai anjima."
"Sai anjima?" Tace a ranta cike da mamakin sa,
"Ok." Tace a sanyaye
"I'm sorry, bye."
Ya kashe wayar, hankalin sa gaba daya yana wajen Dr da ya fito daga dakin Daddy shiyasa ya amsa wayar a gajarce, ya kirata ne ya sake bata hakuri kamar yadda Kamal yace kuma zuciyar sa ta amince da kiran dan haka kawai ya samu kansa da son ji daga gare ta, sai dai kuma bata daga wayar ba har ta katse lokacin kuma ya shiga wata sabgar sanda kuma ta kira yayi busy. Wayar ya tura a aljihun dogon wandon sa ya koma ciki yana shafa sumar gashin kansa Adam na tsaye ya dafe kansa tun bayan da ya ga halin da Daddy yake ciki jikin sa yayi sanyi sosai.
***Da daddare Kamal ya shigo asibitin, dan gaba daya be shigo ba ranar yana kan case din Hajiya Zeenat din in da suka gama tattare dukka bayanin wajenta da fari bata yarda ba amma daga baya da ta ji uwar bari sannan ta bud'e baki wasu abubuwan ma babu dadin ji dan ba karamin basu mamaki tayi ba dan wasu abubuwan ma basu san ta aikata su ba sai da tasha matsa sannan ta bud'e baki. Abu daya ne Abby ya dage ta fada musu in da Ahmad yake ko in da ta kaishi amma ta kafe akan bata san komai akai ba,dan tun bayan lokacin bata sake samun labarin sa ba, bata kuma sake ganin mutumin da ta ajiywa shi ba a lokacin da ta dauke shi, burin ta kawai a lokacin ta salwantar dashi kawai yadda zata fi samun saukin mallake daddy da duk dukiyar sa idan ya zama bashi da d'a namiji a matsayin magaji.
Hannun Aryan ya kama bayan ya fito daga dakin Daddyn suka fito waje, suka samu gefen bishiya suka tsaya ya kwashe masa duk yadda akayi ya sanar dashi sannan yace
“Zaka ji ni shiru na kwana biyu, ina da yakinin zakayi abinda Ya dace wajen ganin mun yi nasara.”
“Karka ce min tafiya zakayi ka barni?”
“Kamar dai haka ne, ba zan dawo ba kuma har sai ka nemo ni.”
“Ban gane ba!?”
“Zaka gane idan aikin ya biyo ta kaina.”
“Kamal please waye kai? Kana sani tunani wallahi.”
“Na lawyer bane ba kai? Find out please. And please be fast about it dan zan zauna zaman jiran ka ne.”
“Ba zaka fada min ba?”
“Yes! Na riga na gama part dina.”
“Ok. I will find out.”
“Please do, cox I’m eager.”
“Ok, stay safe please. Ko ina zaka make sure to stay healthy. I will look for you kamar yadda kace in sha Allah.”
“That’s my friend. Allah ya bawa Daddy lafiya Ya kuma baka nasara.”
“In sha Allah Captain!” Ya tsara masa Sannan ya kame suka kwashe da dariya
“Did you call her? Ka kirata?”
“Wa? Ban kira ba bani ma da wannan lokacin ni.”
“Ok let me find out.” Ya zaro wayar sa. Da sauri Aryan ya warce yana hararar sa
“Me kake shirin yi?”
“Kiran kanwata zan yi naji ko ka kira ka sakè bata hakuri.”
“Akan me wai? Ka damu da ita sosai ni da ko tuno sunan ta ma banayi.”
“Ikon Allah. Waye ya gama mana wakar I love her ranar?”
“Ni ne, amma ai ba love na love nake nufi ba, na addinin muslunci.”
“Hard guy.”
Ya dake shi a chest sannan yace
“please ka dan bude zuciyar nan taka haka nan mana, Atleast we are one step toward victory.”
“We still have alot Kamal, kama hajiya zeenat kamar dai eye opener ne, we have to find out ina Ammy take? Ina Ahmad?”
“Sannan sulhu sakanin daddy da Alhaji Matawalle.”
Kamal yace
“Anya? Haka zai yiwu?”
“Gashi nan dai. Muyi addua sosai akai. Dan inaso mu kulla alaka me karfi bayan wannan ma, ko da yake kamar fa an ce min raihana tana da saurayi ko? Shaf na manta nake ta wannan abun.”
Ya dan bubbugi kansa alamar yayi kuskure. Yanayin fuskar Aryan din ce ta sauya nan da nan, ya yi kicin da fuska ya hade rai kmar bashi ne yanzu suke magana normal ba.
“Kasan ashe wai akwai wani guy da yake ciki, ta fada min sam na manta amma dai babu wani official magana akai gaskia.”
“Toh ni menene nawa da zaka din ga fada min? Ina ruwana?”
“Oh na manta ba ruwan ka, bari na wuce gobe da safe zan zo na dauke ka mu je Office dina.”
“Ba zan je ba.”
“Me yayi zafi ?” Ya fada yana kokarin hana kansa dariya
“Ba komai , kaje bari na koma ciki sai anjima.”
“Ok sai anjima. Ma yi waya.”
“Oho.” Aryan yace yana juyawa Ya bar Kamal a wajen dariya na neman kashe shi
*RQ*
29
****Da sassafe Kamal yazo daukar Aryan ya same shi tare da Adam a asibitin. Adam tun da yazo yaki tafiya babu wanda yake ma wani magana a cikin su amma kuma duk abinda ake bukata da sauri yake tashi yayi. Kallon sa Aryan yayi yasan tafiya zai kuma shi sam zuciyar sa bata yarda da zaman Adam din a wajen shi kadai ba duk da ya nuna damuwar sa amma ba zai iya tantance gaskiyar sa ba
"Kana ganin mu tafi mu bar Adam anan? Shi kadai?"
"Yes akwai jamian mu a wajen duk da ba gane su zai ba, zasu kula da Daddyn har ka dawo."
"Ok, muje."
Suka fice Adam din yana kallon su ba tare da sun masa sallama ba. Shiru ne ya biyo baya tun da suka dauki hanyar babu wanda yayi magana a cikin su har suka kusa zuwa, sosai yanayin Kamal ya koma irin very serious din nan da suka isa gate din cike da mamakin sa Aryan yake kallon komai har suka shiga cikin harabar wajen yayi parking da sauri wasu matasa maza suka karaso suka bud'e masa kofar sannan suka gaishe shi irin tasu gaisuwa.
"Sir Indabawa ya shigo?"
"Yes, anan ya kwana ma."
"Ok... Aryan show them your I'd card."
Hannu yasa a jikinsa ya dudduba be ji shi ba
"Yana mota ko office."
"Ohh..."
"Zamuyi searching dinsa ne sir?"
"Oh yes, kuyi tunda haka dokar tace."
"Ok, zamuyi searching dinka idan ba zaka damu ba."
Kallon Kamal yayi ya gid'a masa kai
"Haka dokar take Aryan, next time don't forget your I'd card ."
Kamal yace yana kallon sa
"It's ok, bismillah."
Duba shi sukayi da yar karamar na'urar su suka tabbatar babu wani makami ko wani abu a jikin sa sannan suka ce babu matsala.
"Are you for real?" Aryan yace suna tafiya ganin yadda ake saluting Kamal din yana babbasarwa.
"Kai ne kadai ka raina ni ai." Ya bige shi a kafad'a
Office dinsa suka isa, ya daga kai ya karanta sunan da yake rubuce a saman office din sannan a hankali ya furta
"You are unbelievable."
Ciki suka shiga ya nuna masa wajen zama sannan ya zauna a kujerar sa ya hau tattare abubuwan da yake son mikawa su ga Aryan din, sai da ya hade su waje daya tsaf sannan ya taso ya dawo kusa da Aryan din ya mika masa
"Na gama part dina, yanzu saura naka part din, I trust you."
"I will take over in sha Allah."
"Good, ina nan ina jiran ka."
"Wai da gaske kake? Tafiya zakayi?"
"Yes da gaske mana, baka so kasan waye ainahin Kamal din naka?"
"Is there anything da ya kamata na sani? Bayan wannan abun da na gani?"
"Akwai da yawa ma."
"Ok, let see."
"Yawwa, lets go an meet Indabawa, daga nan sai kaga Hajiya Zeenat din."
"Bana son ganin ta, mu hadu a court kawai."
"In kace haka, shikenan."
"Yaushe zaku mika ta kotu?"
"Yanzu maganar da zan oga kenan, sai ya saka hannu sannan. Dole kuma za'a bata damar daukar lawyer."
"Ok. Allah ya bamu sa'a."
"Amin dan saurayi."
"Zaka fara ko?"
"Kayi zuciya mana idan baka so na dinga tsokanar Ka."
"Toh yanzu wannan aikin da yake gaba na zanji ko da wanne?"
"Da dukka mana."
"I can't concentrate ai."
"Shine ma zaka fi samun concentration din ai,guy kasan falalar dake tattare da nisa'u kuwa?"
"Ban sani ba, bana ma so na sani, muje dan Allah."
"A ah wait! nine oga anan ai, kaga hungry boys din can na waje, da nace tak zasu zo su sabe min kai sama."
Dariya Aryan yayi yace
"In ka fasa."
"Naji tausayin ka ne, kar nayi ma me rabo asarar handsome guy kamar ka, shiyasa kawai."
"Naji, muje dan Allah, a duk serious abu sai ka kawo wasa."
"Na fada maka, kai kadai ka raina ni wallahi, amma ba komai."
"Naji, lets go oga kwata-kwata."
"Muje." Yace yana mikewa suka fita daga office din.
Sun dade sosai a office din Indabawan suna magana dan har azahar basu bar wajen ba ana sukayi sallah sannan suka fito. Kan Aryan yayi masifar daukar charge dan yana bukatar yayi zama sosai ya duba dukkan shaidun da suke hannun sa, dan ya lura akwai abubuwan da basu gama bayyana ba Wanda suke bukatar nutsuwa sosai kafin su soma shari'ar. A gidan sa Kamal ya sauke shi amma sai yaki shigowa, har Aryan din ya soma tafiya ganin Kamal din be fito daga motar ba ya sashi dawowa baya
"Ba zaka shigo ba?"
"Eh, tafiya zan."
"Muje mana mu karasa duba abubuwan nan sai mu fito anjima."
"A ah, ka ajiye su kawai ka fito na sauke ka a office."
"It's not safe ai na bar komai anan, ina ganin muje kawai na kai su gidan Ya Nabeela sai mu wuce office din."
"Ok, hakan ma yayi."
Fasa shiga gidan yayi suka koma tare ya kaishi gidan Ya Nabeela ya bata takardun da komai yace ta ajiye sannan suka fito a tare ta nufi asibiti wajen Daddy su kuma suka wuce office din.
***Kamar yadda suka dauki kwanaki basu shigo office din ba, haka suka tarar da ayyuka masu tarin yawa.
Zainab ce ta yi knocking sannan ta turo kofar ta shigo tana yauki da rangwada ta gaishe shi a ladafce ya amsa kansa akan aikin da yake yi ba tare da ya dago ba.
"Hope babu wata matsala sir, kwana biyu baku shigo office ba."
"Babu, akwai wani abu ne?"
"No babu komai,zuwa nayi dai naji."
"As you can see I'm very busy, so please..."
"I can help you." Ta tare shi
"It's ok, zan iya. Zaki iya tafiya "
Tsayawa tayi tana wasa da hannun ta, ba tare da ta fitan ba, so take ta tambaye shi Raihana amma tana shakku, dagowa yayi jin bata fita ba ya kalle ta, tayi saurin cewa
"Sir Raihana fa? Ta daina zuwa ne?"
"Zainab please go out."
Yace mata politely yana kokarin hana kansa yi mata wulakanci
"Ok sir, kayi aiki lafiya, idan kana bukatar wani abu ina waje."
Shiru yayi mata haushin nacin ta na tike shi, juyawa tayi ta fita ya ja tsaki da karfi. Ta fara isar shi da shegen iyayin ta.
Akan aikin suka dukufa suna kokarin resolving komai sune har bayan magriba suna office din. Sallah suka fito yi da mamakin sa, sai yaga Zainab a zaune babu kowa sai ita. kallon juna sukayi shi da Kamal da ya fito daga office dinsa shima sannan ya kalle ta.
"Baki tafi ba wai?" Kamal yace da mamaki
"Eh, akwai wani aiki da nake karasawa ne."
"Ko wanne aiki ne ba za'a barshi sai gobe ba Zainab?"
"Aikin me muhimmanci ne Sir, shiyasa."
"Still dai, gashi har duhu ya soma yi, ki jira idan zamu fita kawai sai muyi dropping dinki a gida dan samun napep idan dare ya fara yana wahala"
"Ok sir, nagode." Tace fuskar ta dauke da murmushin jin dadi, ta saci kallon bangaren da Aryan yake taga ya bata fuska
"Muje kar mu rasa jam'i." Yace kawai ba tare da ya saka musu baki a maganar tasu ba.
Tana zaune kamar mayya suka dawo daga sallar, ko motsawa batayi daga wajen ba kar ma su tafi bata sani ba dan ta samu opportunity me kyau da ba zatayi wasa dashi ba,shiyasa ko sallar bata tashi tayi ba tana zaune har suka dawo kowa ya shige office dinsa. Wajen minti talatin sannan Kamal ya fito ya shiga office din Aryan din yace su wuce.
"Kuje kawai zan taho idan na gama."
"A ah, motar ka fa tana asibiti, muje kawai ka ajiye mu a gida ka tafi da motar tawa ma hadu gobe idan Allah ya kaimu."
"Kaga akwai abubuwan da ban karasa ba, musamman harkar shigar da lissafin nan, kwana biyu na samu saukin sa."
"Amfanin Raihana kenan, da tana nan da tuni tayi."
"Zaka fara, shikenan muje kawai."
"Kai kuma baka san gaskiya, ka tsaya kallon ruwa dai, kwado yayi maka kafa."
"Wai dan Allah me yasa kake min haka? Ni menene nawa tsakani na da yarinyar nan ne wai? Aiki take kamar kowa nothing more."
"Kaga duk zagaye-zagayen ka ba zai maka ba, ni dai