Showing 87001 words to 90000 words out of 121037 words
wardrobe dinta ta dauko wani zumbulelen Hijab dinta tun na islamiyya ta zura sannan ta fito. Yana zaune a falon an kawo masa ruwa da abinci Dadah na gefen sa a kujerar sai Hamma Hydar da yake zaune a dayar kujerar suna magana. Da kallo ya bita ta kamar tsohon maye, ta turo baki ta hade rai ta zauna ta gaishe shi ya amsa yana kallon yanayin dake fuskar ta
"Yasu Mama da Amina?" Tace kamar dole
"Lafiya Lou, sun ce a gaishe ki, Amina taso biyo ni toh amma jibi zasu fara exams shiyasa."
"Ok, Allah ya bada sa'a."
"Har yanzu bakya jin dadi ne?" Hamma Hydar yace ganin yadda take magana.
"Kasan sai a hankali dama jikin zai ware." Daadah tayi saurin kareta
"Kin shanye dose din magungunan ki?"
"Eh na shanye."
"Nasan halin ki dakin magani, karki min karya."
"Allah Hamma na shanye. Ko Dadah?"
"Ta shanye."
"Ya karfin jikin?" Muhd yace
"Alhamdulillah."
"Allah ya baki lafiya."
"Amin."
Sai ta mike
"Karatu nake Daadah, bari na karasa."
"Toh." Tace bayan ta gano ta tsaf zaman ne ba zata iya ba.
Tana shiga dakin ta cire Hijab din tana jan tsaki, bata son naci a rayuwar ta, menene na zuwa kuma? Kenan dadewa ma zai yi tunda yake maganar da zasu zo da Amina Amma jibi tana da exams, gaskiya zai takura mata zai shiga rayuwar ta da yawa. Cigaba tayi da kwanciya a dakin kawai dan ko fita bata son yi.
Falon Abby Hydar yaja Muhd domin ya gaishe shi, Abbyn na zaune suka shigo Muhd yayi saurin zubewa a k'asa ya gaida Abbyn ya amsa a sake sannan ya tambaye shi mutanen gida.
"Duk kowa lafiya Abby, suna gaishe ku."
"Madallah, sannu da hanya."
"Nagode Daddy." Yace a ladafce. Wayar Abbyn ce kira ya shigo, Hydar ya dauko masa ya mika masa ya daga bayan ya kalli number
"Assalamu alaikum."
Daddy yayi sallama daga dayan bangaren. Wani irin dauke wuta Abby yayi, ya sake kallon number sannan ya saka wayar a handfree yana matsar da ita daga kunnen sa
"Barka da rana Alhaji Nasir."
"Da wa nake magana?"
"Ibrahim ne Nasir, baka dau muryar ba?"
"Wanne Ibrahim din?"
Dan jim daddy yayi cikin yanayin ba dadi yace
"Ibrahim Mukaddas."
"Ok, ina sauraron ka."
"Ya gida ya aiki?"
"Kasan bana aiki ai, gida lafiya Lou."
"Na kira ne na baka hakuri akan abinda ya faru..."
"Muje Muhd." Hydar yace yana mikewa suka fita
"Abinda ya faru ai ya riga ya faru, babu amfanin dawo dashi." Abby ya amsa bayan ya tari numfashin sa
"Haka ne, amma dai ka daure ka saurare ni,nasan ban kyauta maka ba..."
"Ina ganin da zamu jingine wannan maganar, kowa ya fuskanci rayuwar sa da yafi, gaskiya bana son dawowa da abinda ya wuce."
"Na sani, na sani amma dan girma Allah ka saurare ni, akwai maganganu masu tarin yawa da nake so mu tattauna, sannan ka fuskance ni."
"Ni ka fuskance ni sanda nake cikin matukar bukatar taimakon ka? Ka dubi halin da zan shiga da wanda iyali na zasu shiga? Ka tuna wannan? Ka kore su ka kwace musu muhalli sannan ka hau kan dukiya ta ka zauna daram."
"Ko sisi ban taba maka a kudin ka ba, wallahi duk abinda Ka mallaka a lokacin yana nan, ya ninka kansa saboda kasuwancin da nake maka dashi."
"Menene amfanin su, a lokacin da suke bukatar su me yasa baka neme su ka basu ba? Kasan wahalar rayuwar da suka sha? Kasan yadda akayi suka so nan?"
"Ban kyauta ba, na sani wallahi ban kyauta ba, Dan girman Allah Nasir kayi hakuri ka yafe min, dan Allah."
"Ba zan iya ba, ba zan taba yafewa duk wanda suka jefa rayuwata da ta iyalina a bakin kunci ba."
"Ka saurare ni dan Allah."
"Karka sake kirana dan Allah, ka rike girman ka na rik'e nawa, mun riga mun manyanta yanzu rayuwar yaranmu ce a gaban mu."
Sai ya kashe wayar kawai yana kaiwa karshe. Dama dai Daddy yasan zaa yi haka, ko ma fiye da haka dan yasan iya karshen bata masa yayi, ya kuma cutar dasu. Baba Rabi'u dake kusa dashi a zaune ya girgiza kai kawai
"Ina ganin ka barshi ya sake warwarewa."
"Ba zan warware ba , kafin tafiyar nan zan aika yaran nan da komai da nasan nasa ne, bansan me Allah zai yi ba achan, ko rai zai yi halin sa, kar na mutu da hakkin sa."
"In sha Allahu ma babu abinda zai faru, ka tura su din hakan ma shawara ce."
"Abinda za'a yi kenan."
"Toh maganar yaran fa? Wa zai shiga masa gaba?"
"Rabi'u kana ganin Nasir zai saurare ni da maganar auren Yara? Ai a yadda ransa yake a bacen nan ba zan iya masa maganar ba."
"Shikenan, Allah yasa muji alkhairi."
"Toh Amin ya ALLAH."
***Kwana biyu da zuwan Muhd duk in da Raihana tasan zata hadu dashi bata zuwa, zaman da take a falo ma ta daina sam ko yaushe tana daki idan akayi mata magana sai tace kawai tafi son zaman hakan ne. Hydar ne ya sanarwa da Abby dalilin zuwan Muhd din da izinin fara magana da Raihanan da yake nema a take Abby yace ya amince masa farin ciki fal zuciyar sa dan dama baya son wata magana ta taso akan Raihanan dan ba zai iya chanja alkawarin da yayi ma kansa ba. Har daki Hydar yazo ya sameta da maganar yace ta zo Muhd din yana falo zasuyi magana. Kamar wadda aka watsawa tafashshen ruwan zafi haka taji maganar. Ranta duk ba dadi ta sake zunbudo Hijab din ta fito babu kowa a falon, juyawa tayi ta nufin komawa Hydar ya kwala mata kira daga waje. Fitowa tayi yace taje falon su Muhd din yana chan yana jiranta. Zumburar baki tayi ba tare da ta bari ya gani ba, ta nufi shashen nasu fuskar ta a turbune tana cika tana batsewa haka kawai take jin wata irin tsanar shi na shigar ta, bata son naci gashi nema yake ta karfi da yaji sai yasa an mata dole.
Yana zaune ta shigo ya mike yana karyar da kai murmushi kwance a fuskar sa.
"Alhamdulillah, tunda na samu Hydar ya fito min dake, wai Raihana gudu na kike ne?"
"A ah." Tace a kufule
"Toh bismillah, zauna magana zamuyi, kinsan fa dan ke nazo garin nan amma kike ta share ni."
"Ni ba share ka nake ba, kawai bana jin dadi ne."
"Wai har yanzu zazzabin be tafi ba?"
"Umm."
"Toh ko zamu koma asibiti."
"Bobbo Sadeeq ne yake bani magani."
"Oh na tuna fa Sadeeq likita ne, toh bari na masa magana ko?"
"AI zan masa da kai na."
"Ok, sannu, zamu iya maganar yanzu? Saboda gobe nake so na koma na bar aiki a gabana."
"Kai na ke ciwo bana son yawan magana."
"Toh, yanzu ya za'a yi?"
"Nima ban sani ba."
Shiru yayi duk sai yaji babu dadin yadda take amsa masa, wanda ta nuna masa clearly bata raayin sa, gashi shi kuma da gasken gaske yake son ta, har yana jin idan ya rasata zai iya shiga babbar matsala. Be zata abun zai zama haka ba, ganin yadda suka saba ta sake dasu sosai ya dauka da ya kawo kokon barar sa zata amsa. Toh ko dai tana da wanda take so ne? Ya tambayi kansa. Toh amma idan akwai ai Hydar zai fada masa. Toh ko dai be mata bane ba?
"Raihana ko dai ban miki bane ba??"
_"Eh."_ tace a zuciyar ta, amma a zahiri sai taki magana kawai ta cigaba da wasa da gefen Hijab dinta.
"Ciwon kan ne?"
"Umm."
"Ok shikenan, ki koma ciki amma ki bar wayarki a kunne dan Allah, zan kiraki."
"Toh." Ta tashi tayi ficewar ta,ba tare da taji komai ba, ko rashin kyautawar ta. Tana zuwa daki ta zare Hijab din tana jan siririn tsaki.
_*RQ*_
Page 39
***Kansa da ya kwanta luf ya kalla a cikin mirror sannan ya dauko designer perfume dinsa ya feshe jikinsa dashi. Kananan kaya ne a jikin sa brown chinos da riga long sleeve wadda ta dan matse shi kad'an. Ya gama saka two set na kayan sa a cikin suitcase dinsa. Turo kofar Kamal yayi ya shigo bayan ya dan kwankwasa. Dawowar sa kenan da ajiye Ya Nabeela da Khadija a gidan Ya Nabeelan ya gama shiryawa shima har ya karbi duk takardun da Daddyn ya bashi su kaiwa Matawallen.
"Kar muyi missing flight muje ko?" Yace daga jikin kofar,
"Ok." Aryan yace ya dauki wayoyin sa ya makala airdrop a hannun sa sannan ya shiga jan suitcase din tasa ya fito ya rufe kofar. A k'asa ya tarar da Daddy tare da Kamal a tsaye suna magana, ajiye kayan yayi a gefe ya karasa ya durkusa a gaban Daddyn ya gaishe shi
"Har an fito?"
"Eh."
"Ok, Allah ya kiyaye hanya, Kamal ka dai ji me na fada maka ko? Akan wannan maganar."
"Eh Daddy, in sha Allah zamuyi abinda kace."
"Ok, sai kun dawo, Allah ya kiyaye."
"Amin Daddy." Suka hada baki a tare. Fita sukayi aka saka kayan nasu a booth sannan driver yaja suka nufi airport. Suna zuwa basu samu delay ba suka tashi sai Adamawa-yola. Duk abin nan Aryan be san daddy yasan da maganar shi da Raihana ba, be san Kamal ya gaya masa ba kawai a zuwan zasu je kai sakon Daddyn ne. Maganar da Daddyn yakewa Kamal din kenan dan yace kar su matsa idan yaki amincewa dasu suyi hakuri dan shi babu abinda zai iya.
Suna sauka a airport Kamal ya kira Lamido yace sun sauka, dama ya sanar dashi zuwan su tunda dama suna communicating, address din ya turo musu saboda lokacin yayi nisa baya kusa, sannan ya kira Raihana ya gaya mata akwai baki zasu zo amma sai yaji wayarta a kashe. Baya so ya kira daddy dan yasan yadda yake ciki dasu ita kuwa dadah wayar ta sai kayi ta kira bata dauka ba bata ma san anayi ba. Tunowa da yayi Muhd yazo kuma yana nan yasa ya kirashi ya sanar dashi baki zasu zo ya sauke su a falon baki kafin ya karaso, sannan ya tura wa Kamal din number Muhd din yace su kirashi idan sun karasa. Kasancewar zuwan su kenan na farko garin yasa suka dan samu delay kafin su isa, dan sai da suka fara neman hotel wanda yafi kusa da unguwar su Raihanan suka ajiye kayan su, suka huta ma sannan kowannen su ya sauya shigar sa zuwa manyan kaya fararen shadda rika da wando. Rigar Aryan irin 3quarter din nan ce me gajeran hannu, haka yake son rigunan sa mafi yawancin lokuta shi kuma kamal nasa tazarce ne har kasa ya fito a magidanci sosai me aure while Aryan kana ganin sa kaga matashin saurayi.
"Dan Allah Aryan don't mess up, kaga dai abinda ya kawo mu, ba wai iya sakon Daddy bane kawai, munzo yada jam'iya ne, kayi abinda ya dace dan Allah."
"Ni ai ban iya komai ba kasan."
"Bance ba, kawai dai nasan halin ka ne, kar kaje kayi ma yarinyar mutane dunkum itama tayi shiru a rasa me magana."
"Wai me ka maida ni ne?"
"Me tsoron mata."
"Hmm, toh ai shikenan."
"Ko na rubuta maka abinda zaka ce idan kaje a waya? Sai ka faki idonta ka dinga karato Mata."
Wata dariya ce ta tasowa Aryan din, gaba daya Kamal ya gama maida shi wani bita chan, shine har sai an rubuta masa abinda zai ce din? Dariyar da ya dade beyi irinta ba ya dinga kyalkyalawa, Kamal ya tsaya yana kallon sa da mamakin sa.
"Allah ka ma maida ni wani iri, yanzu har sai na rubuta min abinda zan ce?"
Dariya Kamal din yayi shima sai lokacin maganar ta bashi dariya
"Toh ai kaine wallahi, nasan halin ka."
"Hmm, toh muje dai, na matsu na ganta wallahi."
"That's my guy, haka nake son ji, be romantic."
"Muje toh, Mr Romeo."
"Sunana kenan, ko kace laila majnun, yaro ba zaka gane ba ne, aure yayi wallahi."
"Nifa kanin ka ne, don't spoil me."
"Zaka ce na fada maka, muje." Ya dauki wayar sa dake saman gadon suka fito. Uber sukayi har unguwar tasu, sannan suka duba house number din suka tsaya a daidai date din gidan. Number da Lamido ya turawa Kamal ya kira Muhd yana ganin kiran ya fito waje ya same su, da kallo Aryan ya bishi dan be manta fuskar sa ba, sallama yayi musu suka bashi hannu suka gaisa sannan yace su shigo.
"Wannan gayen shi na gani ranar fa ya kawo ta office."
Ya fadawa Kamal k'asa k'asa.
"Da alama a gidan yake shima."
"Ok." Yace yayi shiru suka bishi ya bud'e musu kofar falon suka shiga sannan yace yana zuwa. Suna zaune ya dawo da bottle water da cup ya ajiye musu sannan suka sake gaisawa
"Lamidon yana hanya ya kusa karasowa."
"Ok mun gode, Alhaji yana gida?"
"A ah, ya fita dazu."
"Ok, Raihana fa?"
"Tana nan."
"Ok. Mun gode." Fita yayi ya bar su, kusan mintuna biyu da zuwan su Lamido ya karaso gidan. Sauri ma yayi sosai dan wani aiki yake gashi da nisa yake. Falon ya wuce direct ya same su, dan sun yi waya da Muhd yace sun karaso. Gaisawa sukayi da tambayar aiki tsakanin sa da Kamal sannan suka gaisa da Aryan.
"Abubuwa biyu ne suka kawo mu Sir, na farko sakon me gidanmu ne yace a kawo wa barrister wasu takardu gasu nan."
Ya daga envelope din,
"Sai kuma magana ta biyu wadda na fara maka maganar a waya, maganar Aryan ce dama, munzo neman izinin a bamu damar ganin Raihana"
"Ok,Masha Allah, abinda ya kamata muyi kenan bayan wannan case din, ina da niyyar ganin family dinmu sun hadu sun dawo kamar yadda muke a dah, yanzu kalli Aryan ni dashi kamar strangers haka ma Abby da Alhajinku. Dole muyi wani abu a matsayin mu na manya, duk abinda ya faru ya faru ne bisa kuskure,kuma bawa baya taba wuce kaddarar sa."
"Naji dadi sosai daka fahimce mu sir, Allah ya bar zumunci, aikin yanzu na mu ne mu karasa shi dan dama mune muka fara shi, daddy bashi da matsala so yake ma Abbyn ya yafe masa laifukansa, ko ya samu ya karasa rayuwar sa cikin kwanciyar hankali."
"Ka bar komai a hannu na, duk da nasan abu ne me matukar wuya amma dole zamuyi nasara a karshe."
"Godiya muke Sir, Allah ya kara girma."
"Yanzu mu shiga gidan ku gaisa da Daadah, sai muci abinci mu fita akwai wani abu da nake son nuna maka."
"Ok sir."
"Muje Aryan."
"Ok." Suka bi kofar dake cikin falon wadda kai tsaye zata kaika cikin gidan. A main falon suka zauna ya shiga ciki ya kira Dadah yace tazo su gaisa da baki, ta fito tana tambayar su waye. Sai da suka gaishe ta sannan Kamal yayi mata bayanin su, aikuwa nan da nan ta hau murna. Ta tashi tace musu tana zuwa ta nufi dakin Raihana. Fitowar ta kenan daga wanka ta gama busar da dogon gashin kanta da hand dryer tana daure shi waje daya Daadah ta shigo.
"Wai ke lafiyar ki kalou kwana biyun nan baki da walwala bakya sakewa ko yaushe kina daki, bayan mun riga munyi magana nace kiyi addu'a."
"Hamma Muhd ne bana son gani, kuma kinga tunda yana gidan be kamata na dinga fita any how ba, kinsan ni da jin zafi bana son saka kaya masu kauri takura nake wallahi"
"Toh yanzu sai ki tashi ki zura ko doguwar riga ce muje ki gaida baki a falo."
"Baki akayi? Su waye?"
"Idan kika fito zaki gansu."
"Ok, bari na saka doguwar riga."
Ta bud'e closet din ta, ta ciro wata doguwar ta zura ta dora mayafin rigar akanta da ta tufke jelar ta sakko ta bayan ta.
"Ki dan kara fesa turaren ko?"
"Nasa roll on fa Daadah, wannan wanne baki ne haka da har za'a ce nasa turare."
"Zaki gani ai,maza fesa wanchan din chan sannan ki dan murza powder da lipstick."
"Toh, ko dai Hamma Muhd ne yace kizo ki fito masa dani."
"Kinji ki, maza dan Allah ni kin barni tsaye."
Powder ta shafa kad'an tunda ita dama ba ma'abociyar powder bace ba, ta saka lipstick kadan ta murza lips din nata sannan tace
"Yayi?"
"Saura kwalli, bakwa san saka kwalli yaran yanzu, ido firkai firkai "
"Kai Daadah." Ta dauki kwallin ta saka. Kallon ta Daadah tayi
"Ya kunnen ba dan kunne?"
"Daadah wai zance zani? Nifa dan kunne takura min yake."
"Saka dai, ko kanana ne, mace sai da kwalliya."
Bud'e wajen da take ajiye su tayi ta dauko ta saka.
"Ko ke fa, muje toh."
Tasa ta gaba suka fito. Dan corridor ne ya raba falon da dakin Raihanan. Dariya take suna magana da Dadah tana tsokanar ta kawai taga mutum a zaune, shine yake facing direct ta inda zasu fito sai Kamal da Lamido da dayar kujerar. Wani irin shock tayi, ta tsaya chak ta kasa karasawa saboda tsabar rud'ewa. Kasa k'asa yake kallonta, kallon da yasa taji kamar na bige mata guiwar ta, taji kamar ta juya saboda tsabar yanayin da ta shiga.
"Raihana, karaso mana kika tsaya anan." Kamal yace yana mata murmushi. Da k'yar ta iya maida masa murmushin ta karaso ta zauna kusa da Daadah ta manne mata kamar zata shige jikinta ta gaishe shi.
"Lafiya lou, ya gida ya kwana biyu?"
"Lafiya lou sir, ina wuni Sir?"
"Lafiya lou." Aryan yace yana kallon centre table din dake gaban sa. Ganin ta gaba daya ya sauya masa lissafi, ga wani irin nauyin Dadah da take wajen kuma yasan kowa yaga irin kallon da yayi mata.
"Mikewa Lamido yayi yace
"Oga muje ko, Raihana ki kai mana abinci falon baki yanzu."
"Ok." Tace ta mike da sauri tayi hanyar kitchen har tana hardewa.
"Ba yau zaku koma ba amma ko?"
"Eh sai sun ga Abby."
"Ok, shima ya fita ne ya shiga gari, kila sai magriba zai shigo."
"Ok Allah ya dawo dashi lafiya."
"Amin." Ta amsa suka fita ita kuma ta bi Raihana kitchen din da sauri
"A tsaye ta ganta jikin fridge bata taba komai a kitchen din ba, shigowar dadah tasa ta motsa ta kalleta tayi murmushi
"Lallai dole yarinyar nan kiki dan uwanki,."
"Kai Dadah, wai dama sune suka zo amma baki fada min ba, wallahi naji kunya."
"Toh ba gashi kin gani ba, ni kuma naga abinda nake son tabbatarwa."
"Nifa babu wani abu fa, ni ba ruwana wallahi."
"Munafuka,ni zaki wa karya? Ban ga abinda ya faru bane ba? Maza wuce ki kai musu abincin kizo muyi magana."
"Kai shikenan na shiga uku." Tace tana dora kayan akan wani babban tray sannan tasa plate uku da spoons ta dauka ta fita ta bi ta kofar da suka shigo din. Sallama ta fara yi a hankali ya amsa ta shigo