Showing 45001 words to 48000 words out of 66781 words
shi yan yana tambayar sa. Duk sauran maaikatan suka yayyabe su.
Alhaji Sambaso ya saka hannu yana rufe bakinsa alaman hamma ce tataho,
"Alhaji ayi hakuri amaana afuwa, Ashe hutawa ma kake"
"Wallahi kuwa bansamu bacci bane gaba daya nache bari na dan huta. Bayan tafiyar Alhaji ateeks"
"Ranka ya dade wani mummunan labarin ne ya faru"
"SubhanAllah Allah yasa muji alkhairi meya faru kuma?"
"Wani ne ya fadi daga barandar ofishin ka...
Kafin su karasa maganar da suke. Alhaji Sambaso ya katse su cikin buda baki yace,
"Ba dai junaidu ba da yazo duba gyaran da zaa mun a barandar"
"Allahu Akbar kabiran. To shine... Bawan Allahn nan yazo dazo yake tambayar mu wajen ka muka nuna masa ofishin ka . Dama bakuwar fuska ne kam. Amman daya nuna katin ka dinnan nasan babban bako ne shysa ma muka kyale shi ya shiga. Ashe ashe ajalinsa ne ke kiran sa. Kuma akwai tsani fa a bayan kofar bai duba ba kenan ya taka karfen dama karfen ai girgidi yake"
Alhaji Sambaso farin ciki ya taho masa ya danne don kar su gane. Ba kadan ba yaji dadi da daya ji daya a cikin maaikatan yace dama karfunan barandar suna girgidi..
Wucewa yayi gaba tamkar Wanda yake cikin tsananin tashin hankali .mutanen suka rufu akansa sam ba dadin ganin gawar ma ta bappah junaid. Aka dakko kyalle aka rufe shi.
Alhaji Sambaso ya sanya aka kirawo ambulance nan da tazo aka fara wucewa aasibiti aka gyara shi sannan aka kira gidah da number Ashir dake cikin wayar ta bappah junaidu.
Nan ake sanar dashi zaa kawo gawar mahaifin su ya fado daga benen barandar me tsananin tsayi ya rasa rayuwar sa yanzu ma gasunan akan hanyar motar kwana kwana sun biya ta asibuti an gwada gwaje likitoci sun tabbatar ya rasa ransa..
Ashir baki daya dama suna zazzaune a parlor ne. Ya na tsaye wayar ta fadi daga kunnen sa yana salati
"Menene Ashir? Menene ?"
"Hamma menene?"
"Ashir Ashir menene?" Bappah Auwalu ya shiga girgiza kafadun Ashir. Ashir yana zubar da hawaye duk tsananin dauriyar sa jikin sa na rawa yace,
"Abbiey ne..."
"Abbieey din. Meya same shi meya samu junaidun?"
"Bappah.... Abbiey ya ra su... Abbiey ya rasu bappah "
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un.......
Bappah junaidu ya ambatada da karfi gwiwoyin sa sun gaza daukar sa ya zube awajen ya fara kuka sosai tamkar karamun yaro ...
_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_
_KU MARMATSO KUSA...🔊_
_ZAFAFA BIYAR 2024_
_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_
_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_
_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_
_________
_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_
_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_
_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_
_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[3/5, 7:07 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_35_
:::::::::
Nawraah na sama ta sakko rike da bokiti a hannun ta da kaya aciki. Tana murmushi tana taka kafafun benen tana sakkowa tace,
"Hamma! Yau ni ma na rigaka Ina son na samu lada.... Na wanke kayan abbiey daya cire jiya. Yana dawowa zan gaya masa"
Tana sakkowa ta tsaya tana duban su. Yadda sukai cirko cirko masu kuka nayi masu salati nayi.
"Menene?" Ta tambaye su jikinta a sanyaye ..
Duk sukayi shiru suna kuka sosai. Ta karasa kusada da Layla ta dafa kafadarta,
"Meya faru ? Eh? Menene? Wane ne ba lafiya ko wani abun ne na daban?"
Layla ta daga fuskarta sharkaf da hawaye ta saukar ta akan Nawraah tace,
"Bappah ne?"
"Bappah sani Bappah salisu ko bappah Auwalu? Meya same su bappahn?"
Layla ta sake girgiza mata kai tache,
"Bappah junaidu?"
"Bashida lafiya? Wani abun ne ko? Daman yadda kwana biyu abbiey yake yi nasan bashida lafiya. Me akace ya same shi?"
"Nawraah. Abbieyn ku Allah ya masa rasuwa"
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un..." Ta fada da karfi ta zube awajen a sume.
Sukai kanta da sauri. Bappah Auwalu ya saka aka kawo ruwa aka yayyafa mata. Ta farfado da kyar tana wani irin sauke numfashi mai nauyi tamkar zata shide..
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un... Bappah Auwalu ku tasheni daga baccin da nake.. wai abbiey ya rasu? Abbiey fa kukace? Abbiey ya rasu fa kukace? Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin wasa ne? Layla meyasa zaki ce abbiey ya rasu akan wane dalilin abbiey zai rasu eh?" Ya karasa fada tana sakin dariya harda tafa hannuwa tamkar sabuwar marar hankali, can kuma ta saki kara mai razana ta fashe da wani irin kuka tana birgima.
"Wayyo Allah na. Abbiey. Wayyo Allah na! Wayyo Allah na Ummy. Wai abbiey shima shikenan ya rasu ya bar mu? Abbiey ya tafi shima? Ummy ma tarasu fa? Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Waya kashe mana abbiey? Kashe abbiey sukai. "
"Kiyi hakuri Nawraah babu Wanda ya kashe junaidu kinji. Lokacin sa ne yayi. Kinaji daga wajen aiki ne wai a karfen baranfa ya taka shine ya fado rai yayi halinsa sun akai shi asibiti ma ance ya cika. Yanzu sun taho kawo shi gidah. " Ya karasa fada mata shima yana sake barkewa da wani kukan
Baki daya sai suka bude shafukan kuka. Nusaiba daga can gefe tayi shiru itama kanta a kasa. Hakika mutuwar kanin mijin nata junaidu ta razananta kwarai matuka. Agubi agubi anyi musu mutuwa biyu kenan ajere ba daukar lokaci.
"Shikenan Hamma bamuda iyaye? Abbiey da ummy sun rasu? Shikenan bamuda sauran gata ko Hamma? " Ashfeef ya fada yana girgiza kai.
Ashir ya katse hancinsa Yana goge hawayen fuskar sa yace,
"Ga mota can inaga sune..."
Dunguma sukai suka fita wajen ...ambulance ce ta kawo shi har kofar gidan suka shigar dashi gidan bisa jagorancin maaikatan..
Daya daga cikin leburan dake kamfanin na Alhaji Sambaso yace,
"Ina wunin ku? Kuyi hakuri fa. Allah ubangiji ya gafarta masa.ya kyautata namu zuwan Allah Kuma ya baku hakurin rashinsa...wallahi Yana gyaran wani bangare ne dake babbar barandar ofishin mai gidan mu. Ashe bai hau tsaani ba sai yahau karafunan barandar a haka ya taka. Su Kuma dama rawa sukeyi shine ya fado Allah yayi masa rasuwa. Domin kwanyar kansa ma afashe take... Inshaa Allahu aljanna makoma ce agareta shi. Yanzu zamu jira a gama wanke shi sai mu sallah shi mu Kai shi gidan gaskia baki daya daku iyalan sa..."
Bappah Auwalu ya fara kiraye kirayen dangi na kusa dana nesa Yana sanar musu rasuwar junaidu. Auta daga iyalan yafendo. Dangin Hamidniyya Lebanon.. Hakika kowannen su mutuwar ta dake shi .
Alkalani yayi kadan wajen bayyana adadin alhini da dangin suka shiga baki dayan su. Musanman iyalan sa na cikin sa sun shiga cikin dimuwa marar misaltuwa.
Haka aka yi masa wanka. Anayi jini na fita daga jikinsa har da guda guda. Haka aka nannade shi duk da hakan jinin yaki tsayawa.
Aka Kira iyalan sa daya bayan daya suka yi masa sallama. Kowanne da koke koke aka futar da shi.
Aka dauke gawar junaidu aka sanya a makara aka sallace shi aka kai shi gidan sa na gaskiyar wato makabarta.
Allahu Akbar wata bishiya ce ta raba tsakanin kabarin marigayi Bappah junaidu da mai dakin sa marigayiya malama Hindu. Allah ya jikan su ya gafarta musu ya musu rahama..
Hakika junaidu ya samu sheda daga bakunan iyalan sa na cikin sa, dangin sa su bappah Auwalu bappah sani da matayen su baki daya dai dangin hamidniyya Lebanon. Sannan mutanen wajen aikin sa dama yan unguwar baki daya sun yabe shi. Ya Kuma samu mutane sosai da suka sallace shi suka kai shi makabarta.
A farfajiyar gidan aka shinfida tabarma aka fara makoki dukkuwa da ahalin Hamidniyya Lebanon basa zaman makoki, Amma mutane na zuwa yi musu ta'azyiya wasu tundaga birnin bunza na kusa dana nesa...
Suma yan yankin bunza sosai sun yi alhini da jimamin rashin junaidu. Domin yanada halaye na kwarai bai taba fada da wani ba .. kowa nasa ne ga temako .
_Yanzu zamu sake tsunduma cikin labarin:_
_KWANKWASON JIMINA MAI WUYAR SHAFAWA... Ayi hakuri da yadda rubutun yake zuwa... Labarin na gaba In shaa'Allah_
_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_
_KU MARMATSO KUSA...🔊_
_ZAFAFA BIYAR 2024_
_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_
_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_
_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_
_________
_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_
_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_
_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_
_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[3/6, 1:52 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_36_
:::::::::
Anyi shela anyi cikiyar wadanda ke bin junaidu kudi ko wani na ajiya suyi magana a basu. Yawanci ma anfi samun wadanda shi yake binsu bashin basu biya shi ba.. duk wadanda suke binshi bashin da yawan su wasu sun yay'yaafe. Wasu kuma sun karbi wani kaso na cikin kudin sunce sun bar sauran..
Sai wani mutumi daya tashi ya taba kafadar na gefen sa suka mike. Suka ce hakika ana bin Junaidu zunzurutun kudade masu matukar yawa.
Hakan ta faru ne kuma alokacin da daya daga cikin yaran sa babu lafiya. Aka tambaye su adadin kudin sukace ai wannan magana ba tasu bace. Domin suma shedu ne na mutumin da junaidu ya karbi bashin agaban su. Kamar jingina yayi ya karbi tarin kudi...
Aka nemi ganin mutumin don sanin waye shi da yadda zaa biya da sanin ma shin nawa ne adadjn kudin daya karba? akace daya mutumin yayi tafiya sai ya waiwayo gidah nigeria tukunna.
Daya daga cikin su ya karkare magana da
"Abunda ya saka muka fada ma saboda hali ne irin rayuwa kada abar mamaci da tarin bashi akan sa. Duk kuwa da kadarar sa ya jinginar ya karbu kudin. Amman dai mun ga yakamata fadar shi yafi alkhairi Allah yasa mu dace"
"Ko zamu iya sanin kadarar daya bayar ya karbu kudin a hannun sa?" Bappah salisu ya tambayi mutumin
Mutumin ya girgiza kai sannan yace,
"Wannan batu baki daya sai an kawo takardar da faifan bidiyo da sukai yarjejeniyar ya sanya hannu tukunna shi mamacin. Kafin shima Alhajin ya rattaba nasa hannun"
"Toh Allah ya rufa asiri. Allah ya dawo dashi lafiya. Shi Kuma wannan Dan uwan namu Allah ya jikan sa ya gafarta masa Allahumma Aameen"
Suka amsa da aameen baki daya. Aka shiga yiwa bappah junaidu addu'oin samun rahamar Allah da nasarar amsa tambayoyin kabari.
::::::::;;;;;;
Sannu ahankali haka mutane suka fara darewa, kowanne yanzo daa irin kyawun halayen da yake fada game da manacin.
Hakika bappah junaidu ya samu yabo sosai daga bakunan abokanan sa, Yan unguwa, Yan wajen aikin su, makotan su, Yan unguwar baki daya dama dangi na kusa dana nesa.
An kakkawo musu kayayyakin abinci na tallafawa marayun. Saboda kallo daya zakai musu su baka matukar tausayi marar misaltuwa. Dubada duk ba wani kawo girma sukai sosai ba har shi Ashir din. Be Kai shekarun da zaa ce zai hade kawunan Yan uwan na sa ba.
Amman dake yanada zuciyar tashi ya nemi na kansa don kare daraja da martabar yan uwan nasa. Hakan bai hanashi kutsawa nan da can ba don ganin ya rufa musu asiri...wannan kenan
Haka aka nannade makoki. Akabi mamacin da addua. Hadi da dangana da hakuri da iyalan sa zasuyi. Kowa ya watse na kusa dana nesa
Idan ka tsame dangi mafi kusantana marigayin ba. Wato su Bappah Auwalu da su Bappah sani...
A parlorn Bappah Auwalu suka hallara baki daya iya yan dakin su. Sai nusaiba da tayi kanai kanai taki tashi suna magana tana tsoma baki..
Ba wanu abu ya bari da yaran zasu mori ba illa dubu biyu da dari uku dake aljihun sa Kafin rasuwar sa, sai Kuma wayar torchlight dinsa . Da wasu dari takwas dake drawer dinsa.
Toh su aka harhada dai aka gangada dai da sauran abubuwan sa aka raba gado aka baiwa yaran sa.
Wasu daga cikin kayan sawar sa bayan yaran sa maza sun dauka suna so. Sai Yan uwansa wasu ma suka dauki wasu. ragowar Kuma aka kyautar sadaka duk Wanda yazo karba sai ache masa yayiwa mamaci addua..
Baki daya a zazzaune suke suna kallon kuna. Suna magana,nusaiba na daga saman kujera tana jin abubuwan da suke fada. Wani ta saka baki baki wani tayi shiru..
Ashir ya taho daga gidan su zuwa gidan bappah Auwalu zai gayshe da bappanin na su kamar ko da yaushe yanata sauri ya karasa kofar gidan. Ya saka hannu zai murza kofar ya jiyo su suna magana haka sama sama tamkar masu rigima ko fada, Bappah Auwalu na cewa....
...
_Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._
_idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_
_zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._
_kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_
[3/6, 2:03 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_37_
_Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._
_idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_
_zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._
_kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_
°°°°°°
"Dukkanin mu nan uwar mu daya uban mu daya... Ba bare acikin mu idan kuka tsame Nusaiba..."
"Nima ba bare bace Auwalu . Auro ni fa kayi ka cire ni daga cikin dangi na ka dawo da ni naku. Kana da bakin cewar wani ni ce bare?" Nusaiba ta fada tana gatsine.
Yakumbo Aminatu ta tabo ta tana girgiza kai tace,
"Kash ba da wani abun ya fada ba Nusaiba. Dan Allah tashi ki koma daki. Idan muka gama kyaji duk yadda mukayi. "
Mikewa tayi tana zunburar baki hadi da kananun mita ta shige cikin daki. Ko da ta shiga ma d'age labule tayi ta kasa kunnuwanta tana jiyo abunda suke fada...
"Bappah sani, bappah Auwalu, Bappah salisu, Yakumbo Aminatu ... Kamar yadda yaran nan ke fada dukkanin su baki daya ciki harda yaran mu. Basuda wasu da suka fi mu ko suka kamo kafar mu. Mune uwar su mune uban su yanzu. Wallahi Allah sai ya tambaye mu idan bamu kula da yaran nan ba ... Bari na sake nanatawa. Acikin mu da muka rage mu hudu dinnan. Kowanne zai iya daukar yaran nan baki daya ya rike su ba wani abun bane. Zumunci ne. Naka shine naka. Ido biyun duk sun tsiyaye musu, sun rasa uwa da uba cikin kankanin lokaci baki daya ba jimawa. Zan sake nanatawa, Salisu, Sani, Ameenatou. Dukkanin ku kunfini karfi Kuma kowannen ku zai iya rike fiye da yawan yaran nan ma akarkashin sa. Allah ya hore muku. Yaran nan suna bukatar danshin iyaye atare da su. Ku temaka yanzu acikin ku wanene zai dauki yaran nan baki daya? Kuna ganin abunda mutanen nan sukazo sukace ma akan junaidu yayi jingina ya karbi kudi. Bayaga haka nace muku junaidu nima ya rantomun kudade nayi gyaran gidah har yacemun kyauta da fari nace masa wallahi bazan karba ba bashi nake so... Kunsan dai halin dan uwan mu da rufawa nasa asiri? Sam bayasan wani na waje yaji barakar mu. Zai iya salwantar da komai nasa don ganin ya sanya mu acikin farin ciki. Dan Allah kada mu bari yaran nan suyi maraicin iyayen su. Kada mu bari yaran nan su Gane Cewar bamuda hadin Kai a tsakanin mu ba zamu iya rufawa dan uwan mu asiri ba. Wanda dukkanin mu nan kowannen mu junaidu yayi masa da aljihun sa, da jikin sa da gumin sa. Bai taba gajiyawa ba..... Shin wa zai karbi rikon yaran nan su dawo hannun sa? Su hudu ne kawai, Ashir, Ashfeef, Nawraah sai Kuma auta Amnah... Wallahi summa tallahi da inada halin da zan rike yaran nan wallahi zan rike su, Amman banda shi. Junaidun dai ke rike damu duka har ni ya rasu. Dan kuwa komai na rayuwa wallahi shi yake mun ya dauke mun komai . Ba abunda zance da shi sai fatan Allah ya masa rahama yasa ya cika da kyau da imani amin "
"Aameen " suka amsa baki daya
"Sani zaka rike su?"
Bappah sani ya grigiza Kai Yana duban agogon hannun sa yace,
"Kasan halin da nake ciki yanzu. Wallahi Idan na ce zan rike yaran nan zan takura bazan iya ba wallahi."
Bappah Auwalu ya kada Kai ya dubu Bappah salisu yace dashi,
"Salisu kaifa! Nasan dai ba zaka ki ba. Kusan a bunza