Showing 48001 words to 51000 words out of 66781 words
junaidu yafi shakuwa da Kai ma"
Bappah salisu yayi hanzarin girgiza kai yace,
"Bazan iya rike su ba gaskia. Abubuwan sai ahankali yaran gaba na kadai ma sun ishemu. Bazan iya hadawa da yaran nan ba saboda banida karfin hakan"
Bappaah Auwalu ya kada Kai cike da takaici . Ya dubu gwaggo Ameenatu yace,
"Ke fa? Aminatu ke fa? Zaki rike su ko? Nasan ke bazaki ki amincewa ba ba zaki ki tallafar ahalin junaidu ba. Ni na sani"
Gwaggo ameenatou ta sauke katuwar bahaguwar zuciya tace,
"Ba wai naki bane. Amman Auwalu a situation din da ake ciki Allah mai gidan ma baze bari na dauke su duka ba. Kaga expenses din sunyi yawa. Amma dai ni Ina son abani Amnah zan riketa. A shirye nake na tafi da Amnah. Idan yaso su Ashir, Ashfeef da Nawraah sai asan yadda zaa kula da su. Ko a rarraba su. Ni na dau Amnah, Kai salisu ka dau Ashfeef da Nawraah, sani Kai Kuma ka rike Ashir dakin nan na wajen gidan ka ku bashi ya zauna aciki ya muku tsaro ma tunda namiji ne Kuma babba, Ko duk wata wata zamu dinga harhadawa yan kudi ana kula dasu. Kowannen acikin mu sai a bashi ya kula da dan dake gaban sa yana ragewa. "
Ashir ya girgiza kai din takaici har hawayen bakin ciki yayi. Wato da iyayen su na raye bappanin nasu kamar su cinye su suna nuna suna kaunar su. Amman yau dan ba ran bappah junaidu da su ke uwa daya uba daya shine autan su Kuma 'yayan sa na cikin sa. Amma kowanne yaki amincewa ya karbe su.
Cikin zafin nama ya bude kofar ya shiga yana goge hawayen sa yana kallon su yace,
"Yakumbo ba zaki dau Amnah ba, ba Wanda zai dau kowa... Ku barshi kuje ku zauna da iyalan ku na cikin ku. Ni zan rike kanne na. Zan kula da cin su, Shan su, tufatar da su da yi musu komai Wanda mahaifi da mahaifiyar su zasuyi musu. Zan share musu kukan su. Da yardar Allah ba zasuyi na damar kukan rashin iyayen su ba a kusa. Barkan mu da rana dama gayshe mu nazo yi. Ku huta lafiya..."
Ya juya ya fice cikin zafi nama. Ransa na matukar Susa. Ya rakube a jikin wani gini Yana kuka sosai. Dama haka Yan uwantakar take? Wato idan kana raye ne akeyi da Kai da iyalan ka idan ka rasu baya ake juya musu ana kyamatar su haka? Lalle sunyi rashin bango majingina.
"Yaa Allah.... Ka dubi maraicin mu ka kawo mana dauki Aaameen." Ya fada Yana goge hawayen sa yayi hanyar gidan su jiri nata dibar sa.
Jijiyar kansa ta tashi radau ransa amatukar javula haka ya seseta kansa ya shiga gidan na su. Kai tsaye ya wuce dakin su. Ashfeef baya nan. Ya nemi katifar su ya kwanta Yana rufe fuskar sa da tafin hannun sa..
Hawaye masu matukar dumi suka shiga kwarara daga idanun sa...
:::::::::
_Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._
_idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_
_zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._
_kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_
[3/6, 2:22 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_38_
:::::::::
Bappah Auwalu ya mike tsaye yana nuni da kofar da Ashir ya futa hawaye na gangara a fuskar sa yace,
"Kun gani ko? Tun ba'aje ko'ina ba. Kun fito kun nunawa iyalan sa na cikin sa ba kaunar su kuke ba. Haba haba haba wallahil azim kunban kunya. Wallahi summa tallahi da inada halin da zan rike yaran nan wallahi zan rike su.. Amman tir da halayen ku, kun yanke amanar zumuncta Allah kyauta"
"Ni dai na gaya maka uzuri na. Ai wata kusan tafi wata kusa. Har ga Allah banga ma abunda akayi anan ba. Yaran dai dama yanada tinkaho ne kawai amman me akayi anan ko salisu?"
"Gaskia nima sani banga abunda akayi ba. Magana ce fa aketa gaskia domin Allah. Magana ce ta dindinin abunda zaka dore. Ai bakyau mutum ya dau a abinda ba zai iya cigaba da shi ba. Mun fito mun fadi uzurin mu shin menene matsalar anan? Me mukayi ni gaskia banga wani aibu da akai anan ba kai ma Auwalu da son kakaro mana lefi. "
"Hmm bare ni dana amince zan rike daya daga cikin su. Ni menene aibuna? Na amince zan karbeta na riketa. Ba shikenan ba? Amman yaci ace yaron nan yazo tsakiyar mu manyan sa, da uban sa yace zai gasa mana maganganu har haka? " Yakunbo Aminatu ta karasa fada tana jan dogon tsaki...
Bappah Auwalu ya ja tsaki akaro na uku yana karkada hannu Yana nuni da ceiling dinsa yace,
"Wannan ceiling din da sabun kofofin nan/kyaurukan nan. Marigayi ne ya kawo mun kudin wallahi kyauta ma yace ya bani shi zai biya su. Nace aa wallahi bazan amince ba nafi kaunar ni na biya da Kai na idan na samu. Domin junaidu adadin bashikan da yaron nan ya biyamun Allah ba zasu fadi ba. Cin mu , suturar mu, komai namu wallahi Allah shine shahidi. Junaidu yana matukar kokari ganin ya mana dai dai gwargwadon ikon sa. Haka ma matar sa wallahi batada bakin hali kwata kwata. Hakama yaran nasu baki dayan su wallah kowanne sai sam barka. Amman tin da ga kowanne acikin ku uzurin daya kawo bazan takura muku ba. Allah ya kyauta. Ni naji na amince zan rike su"
Nusaiba ta fito daga cikin dakin da take labe. Ta daga hannu tayi guda ta nana a cinyarta tace,
"Katarar ubancan. Lalle ma Auwalu, mu sai yan hakora. Da jiki duk qashi muna tafiya da kwana acikin talauci. Kache zaka rakito mana wasu rayikan har hudu su tare awurin mu. ? Shin Ina zamu saka su acikin wannan gidan naka mai ukubar rayuwa eh? To ahir dinka. Wallahi ahir dinka. Narantse da uban da ya haifeni ban amince ba"
"Gaskia babu babbar butulu a duniya irin kiba nusaiba. Babu Allah. Menene a duniya Wanda mamatannan basu Miki ba su da yaran su.? Junaidu daki sukutum ya dauka ya baki kika saka kiwon da kike. Banda tarin alkhairin da yake mana mu da yaran mu kullum. Marigayiya Hindu baiwar Allah nan ba abunda ta rage Miki ta dauke ki tamkar kanwarta bata Miki kallon faccala dede da second daya. Duk sanda tayi awarar data fara ta sayarwa har Allah ya karbu ranta kullum yaumin sai ta aiko mana, karewarta ma ranar da zata rasu sai data shigo muka gaysa tace daman wajen ki tazo ma tamiki fada . Yaran nan wataran wajen ki zasu dawo ki rike su ma ke zaki aurar da su. Wai Amman duk wasiyyar da take bar miki din kuwa wasiyya ce dai dai da kwayar zarra baki taba ajiyar ta ba a...
"Ya Isa dakata da wannan wa'azin kurman da kake don ba saurara nake ba. Da fari kana magana yo wancen akurkin dakin ai sai da ya tabbatar dan Adam ba zai iya kwana aciki ba ko da kuwa rai daya ne bare yace zai moriyar sa shine ya jefe ni da shi. Su kansu kiwon dakyar suke nunfashi saboda azabar zafi da duhu ba ai wundo ba a dakin haba haba dan Allah... Kana maganar awara awarar banza awarar wofi Allah ya kwashewa waken soya ma albarka Auwalu, . Kana maganar suna kyautata mana to ba dole su kyautata ba kudin yafendo ne data bayar ya handame don kuwa sata yayi yasa tayi masa kyautar dole. Dake Kai zakara ne sai da tsaba ya saye ka da kananun kashin kudin da yake maka ya rufe maka baki baka iya ganin lefin sa . Wannan kai ya dama. Na fada na sake fada ba yaran da zai zauna mun agidah wallahi. Muna karime Karime to abincin da zamu ci kullum na rai hudu dakyar zaka karo mana wasu hudun? Tukun nama aina zasu kwana? Wannan gidan Mai kama da turken agwagwi. Muma bai ishe mu ba bare Karin wasu mutanen Na gama magana Allah . Ba dan da yar da zasu zauna mun " tana karasa maganar ta shiga daki ta bugo kofar.
Bappah Auwalu yayi shiru ya kasa cewa komai. Babban abunda yafi daure masa kai da Yan uwan sa uwa daya uba daya ke wajen basu tanka sun tsawatar mata ba, Amman ba wani abun mamaki bane tunda sun ki amincewa su rike yayan kanin su uwa daya uba daya .
"Allah ya kiyaye hanya idan kun tafi. Na bar ku lafiya Allah yabada ladan taaziyya mungode"
Ya saka kansa ya fuce ya bar su zaune... Suka gama maganar da zasu yiyyi suka hada Yan kudin hannun su suka zura a takardar envelope suka saka masa a bayan kujerar da ya tashi
.
Daya bayan daya suka dare suma batare da sunji kunyar abunda suka aikata ba na kin daukar 'ya'yan kanin su uwa daya uba daya...
Ashir yana kallon kowannen su ya shiga motar sa ya tafi, ta cikin windon dakin sa.. yakumbo aminatu ma direban ta yazo daukar ta ta shiga mota tatafi.
Rayuwa kenan dama wasu dangin basayi da iyalin ka sai kana raye idan ka rasu kabar iyalan kama juya musu baya suke..
Lalle bango majingina ya fadi. Allah ya jikan Bappah junaidu da malama Hindu. Ya Kuma raya musu yaran da suka bari, Ashir, Ashfeef , Nawraah da auta Amnah.
Sabon shafin rayuwa suka bude mai ban tausayi da ban tu'ajjabi....
_Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._
_idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_
_zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._
_kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_
[3/7, 2:50 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_39_
:::::::::
_ADVERT👇👇_
_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
:::
**Dawowar sa kenan daga bakin tashar motar unguwar su ta Naduka zone. Ya shiga gidah bakin sa dauke da sallama. A matukar gajiye yake baki daya jikin sa ciwo yake tamkar ana kwankwatsar kashin sa.
Ya bude parlorn ya shiga yana doka sallama. Amnah ce zaune akan kujera dauke da kofi a hannun ta.
Ta amsa sallamar tana murmushi. Kasancewar akwai shakuwa sosai tsakanin ta dashi. Kusan shi ya reneta tun tana zanin goyo har girman ta.
"Amnah nah"
"Hamma" Ta kira sunan sa tana murmushi.
"Sai ke kadai? Suna Ina?"
"Adda Nawraah ta na kitchen hamma Ashfeef kuma baya nan"
"Me kike sha ne baki rage mun ba?"
'kunu ne Hamma. Gashi na rage maka" ta mika masa kofin
Ya girgiza kai yana komawa kusa da ita ya zauna yana kai hannun sa kan goshin ta,
"Ya jikin naki?"
"Da sauki hamma"
"Toh sannu kinji? Allah yabaki lafiya mai dorewa Amnah"
"Aamin Hamma"
Bakar ledar dake aljihun gefen rigar sa ya janyo ya sunceta. Yana dubanta yace,
"Kinci abinci?"
"Na koshi Hamma"
"Ah ai bazeyiwu ba. Jeki ce Adda nawrah tabaki plate. To zakici biredi?"
Nanma ta grigiza kai tana mikewa tsaye tace,
'ga kunu nasha. Na koshi"
"Toh jeki kice ta baki plate"
Tayi hanyar kitchen zata kira Nawraah sai ga fitowar nawraahn "
"Ah hamma yaushe ka dawo?"
"Ba dadewa kenan na shigo. "
"Sannu da dawowa hamma. A kawo abinci?"
"Aa barbabincin nan cikina ya cushe ban dai ruwa kawai, ki taho da plate"
"Tohm Hamma"
Kitchen ta koma tana yan zikirinta labbannata na motsawa ahankali . Ta dakko plate da ruwa ta kawo masa ta durkusa ta mika masa ya karba,
"Allah ya shi miki albarka"
"Aamin Hamma. Wa iyyakum"
Ya karasa shan ruwan kenan sai ga shigar Ashfeef parlorn ya dawo daga filin ball.
Ya tsaya suka gaysa da Hamman na su sai Kuma ya wuce bandaki. Wanka yayi ya sauya kayan sa zuwa na gidah ya koma parlor ya zauna shima
Ashir ya nannade takardar naman ya zazzage naman akan tray. Ba wani mai yawa can bane. Amman yankan su nada girma ya debi manyan tsoka da yawa ya mikawa Amnah
'kin dora akan abinci. A Zuba Miki ko da biredi zakici uhm?"
"Zanxi da bread"
"Yauwa Ashfeef Miko mata bread idan da akwai"
"Suaran sa kenan dazu na cinye Kafin na gama abinci wallahi." Nawraah ta amsa shi tana langabar da Kai
'okau ba damuwa Ashfeef huta ka karno bread anan shagon naga Yan majalisa fal dawowata dana aika Nawraah,
"Ah zan karbo Hamma. Ai ban gaji sosai ba"
"Rike ungo ban naka ne. Nawraah kema ungo naki." Ya daddanka musu nasu kasan naman yana karkade hannun sa
"Hamma Kai fa?" Nawraah ta tambaye shi cike da tausayin sa
Ya girgiza kai yana kauda shi yace,
"Yana yankawa Ina ci. Kaki damu" ya bata amsa da haka
Sarai tasan bawani naman dayaci sanda ana yankawa. Wannan dabiar tasa ba zai taba sauyawaba. Kusan kullum hakane ke faruwa. Ko abinci ne bai Isa ba zai ce su cinye shi a koshe yake..
Ganin irin kallon da suke masa su ukun yasa ya kakaro murmushi don tabbatar da su yace,
"Gyaran wata mota mukai babba. Ta gyaru sosai shine mutumin da aka gyarawa dayazo karba yaji dadin gyaran sai yayi mana alkhairi"
"Allah sarki Hamma. Allah ya kara daga ku ya inganta ku"
"Aameen. Jam'an"
Ashfeef ya fita ya sayo biredi. Haka suka gaggand'a da abinci suka ci. Dare yaja suka kwanta..
Ashir na tsaye tsayin daka akan su. Kwata kwata baya samun hutu ko na minti. Kullum Yana aikin da zai rufawa kansa dana Yan uwan sa asiri.
Idan yaga ana gini zai cire kayan sa. Yaje ya musu lebura ya debo musu ruwa su biya shi ko bulo, Idan yaga gidan Mai yayi datti ya shiga ya share a biya shi.
Yaje gareji nanma yayi gyaran mota ya Kuma wanke ta a biya shi. Ahakan Kuma duk da haka idan fenti aikinsa ya taso yana zuwa yayi shi da Ashfeef
Ya yinda Nawraah ke kula da gidan tana dawainiya da kanwar ta su marar cikakkiyar lafiya wato Amnah...
Nawraah tana yin kitso akan mutane daya daya haka. Da haka suke hada yan kudaden su rufawa junan su asiri mashaa Allah...
_Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._
_idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_
_zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._
_kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_..
[3/7, 2:50 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_40_
_Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._
_idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_
_zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._
_kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_..
:::::::::
.... Suna zazzaune baki dayan su a parlorn su. Nawraah na koyawa Amnah karatun alqur'ani tana kara mata ayoyi biyu kamar ko da yaushe na daga surar da suke...
Domin Amnan kasancewar batada cikakkiyar lafiya. Kullum a kwance take. Hakan yasanya baa sata a makarantar ba tun da ran mahaifan su...
Ashir na zura yan ashirin ashirin da goma goma na dari takwas din daya samu awajen wankin mota. Yana ta cusa su acikin asusu yace taru zasuyi sosai da azumi sai afasa inshaa Allah ayiwa yaran kayan sallah da abincin sallah.
Ashfeef Kuma Yana gefe da yar wayar sa rakani Kashi a hannu Yana latsawa.
Bubbuga kofar gidan na su aka fara yi da karfi kamar zaa ballo kofar baki daya. Ashfeef ya mike ya fita .
mutane ne guda biyu suka zo acikin wata zungureriyar mota. Sun fakata a daidai kofar gidan tamkar zasu shigar da ita aciki saboda yadda tayi dab da dab motar da kofar shiga gidan.
Sallama yayi musu suka amsa masaa gayshe su yayi Yana bin su da kallon Karin bayani.
Manyan mutane ne Wanda kallo daya zakai musu kasan masu kudi ne.. dubada motar da suka zo da ita da kayan dake jikin su ma na manyan attajirai ne.
"Kai dan gidan marigayi junaidu me ko?"
"Eh Dan sa ne"
"Eh ga kamar Nan" daya daga ciki ya fada
"Kai ne babban Dan sa?"
"Aa akwai Hamma Yana ciki"
"Kira mana shi yanzu "
"Tohm. Amma su waye zaa ce?"
"Kache magana zaai da shi"
"Tohm" ya fada Yana komawa cikin gidan ya shiga Yana sallama suka amsa Ashir ya daga Kai Yana kallon sa yace
"Su waye?"
"Wasu