Showing 36001 words to 39000 words out of 66781 words

Chapter 13 - KWANKWASON JIMINA BOOK 1 hausa novel

24 Aug 2024

13630

nera dari ta mika mata,

"Maza maza tafi gidah"

"Ummy meyasa?"

"Ni dai nace miki ki tafi gidah ko? Tafi da wayar tawa ma "

"Idan aka kira ki fa"

"Baa wanda zai kira ma jeki yi sauri karki juyo ki, tafi gidah ki wuce kar ki dawo. Ki kashe wayar ma me kikayj awayar ne"

"Recording wakar Maher Zain nayi"

"Lokacin duk suna wadannan maganganun?"

"Eh bansani ba ni dai tun dazu na ajiye ta"

"SubhanAllah to tafi gidah dai ki kashe wayar idan kinje gidah ki bawa Hamman ku ya ajjye idan na dawo zan karba "

"Kai ummy?"

"Nawrah nace ki tafi ko?"

"Tohm shikenan. Ga tawa ki rike" ta mika naga wayar me torchlight ta ummyn ta da da ta bar mata ,

Ummyn ta girgiza kai tana kakaro murmushi tace,

"Ai dole sai kin saka na karba Kai nawrah dadi na dake KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA... Je ki Allah ya miki albarka..."

Ummyn ta karba tana cusa ta a jakarta ta hannu ... Tana kambama jarumta irin ta Nawrah tun tana karama. Lalle idan ta girma za'ai mace mai kamar maza....

Nawrah ta futa daga gidan taje titi ta hau mota ta koma gidah. Yayinda malama Hindu ta koma cikin kitchen din duk abunda da suke ashe Dr bintu na hango su... Ba dai ta jiyo maganganun da suke..

Jikin malama Hindu na rawa ta shiga aikin data sakata ta dama kunun tazuba a flask

"Hajia na karasa"

"Hindu"

"Naam"

"I don't care da rantse rantsen da kike Amma Allah idan naji magana daya ta fita wallahi sai kinyi mamaki"

"Wace magana hajia nace ba abunda naji"

"Ni dai na gaya miki"

"Inshaa Allah hajia. Ni ba zamma Kara aikatau ba wallahi daga yau da yardar Allah, na tuba dan Allah kiyi hakuri ki gafarce ni" ta durkusa kasa tana hada hannuwan ta

"Shikenan jeki sai da safe"

Hindu ta mike dasauri jikinta na rawa ta zura takalman ma wari da wari ta saka..

Tana futa Alhaji Sambaso ya mike zai fita shima,

"No Alhaji please "

"Kin aminta da ita.. ba ita ce mai aikin su ba kafin tafiyar su waje"

"Dan Allah ka kyaleta nasan ba zata fada ba"

"Okay ni ba wajenta zani ba"

"But am...

"Nace miki ba wajenta zani ba. Refreshing brain na kawai zanyi zan dan fita yanzu ba nisa zanyi ba ita kuwa ai nasan ta hau mota ta tafi ma"

"Shikenan sai ka dawo"

Fita yayi wajen gidan ya dau motar sa ya fita daga cikin gidan a hankali yake tafiya yana hango malama Hindu tana tafe tana waiwaye tana tafiya atsorace...

Tunani dankare cikin kirjinta, wannan wace iriyar rayuwa ce haka? Dama zaman cin amana suke da su? Lalle duniya abar tsoro ce... Wayar dake gurin ta ce ta fara kara mai gidan ta ne wato bappah junaidu ta dauka muryarta na rawa ta saisaita kanta tace gata nan zata dake yanzu inshaa Allah...

Daman titin yayi dubu ba street lights sun mutu..Salati ta fara yi tana karanta la'ilaha illa anta subhanaka jnni kuntu minazzalimin..

Alhaji Sambaso ya kara gudu zuciyar sa na kuna,, wato har ta fara kiran waya tana fada kenan? ya tashi kanta tana komawa gefen bishiya ya hadata da bishiyar ta daga sama can ta fado kasa tim kamar ba mutum ba ..

Ya arce dagudu ya hau babban titi. Sai bayan yan mintina tukun sannan mutane sika taru tana numfashi dakyar,..aka lalubo waya ajikinta aka Kira number data amsa Kira karshe ta bappah junaid da nawrah tayi saying da abbiey ban da nan suka kira shi suka gaya masa hankalin da ake ciki.
.
Suka nufi gidan da ita wani mutumi ya temaka aka kaita kasancewar ummyn tanata magana da kyae kan akaita gidah

Ana kaita baki daya yaran sukai kanta sunata ife ife da adduoi. Daga na suma rankaya asibiti

Likitoci sukai kanta aka saka mata oxygen kasancewar numfashin ta ya fara sarkewa.

Likitocin sunata kokarin bata temako, Bayan wani lokaci, Likita on duty ya fito daga emergency ward yana zare facemask dinsa ya dubesu kansa a kasa .

Ashir ya karasa kusa dashi yana girgiza kafadar sa,

"Ya jikin ummyn wani abun ake bukata? Jini? Kudi? magani? Me kuke so?"

Likitan ya girgiza kansa bayan ya sauke katuwar bahaguwar zuciya yace,

"Sai dai muyi hakuri Allah ya mata rasuwa...babban dadin kuma ta cika da kalmar shahada Alhamdulillahi....


_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_


_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_

[3/1, 1:57 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_


_✍️:MX_


_26_


:::::::::
    *Dukkanin* su a tare ji da ganin su suka dauke na 'yan wasu daki'kai...

Ji ka ke timmmmmm... Bappah junaidu ya fadi wanwars a kasa sumamme ..

Likitan yayi kansa. Ashir ya shiga bubbuga kansa a bango... Yayinda Amnah ke duban su duka tana hawayen itama duk kuwa da karama ce ainun. Ashfeef ya rike hannun ta shima yana rera kukan sa ahankali

Nawraah ta sulale daga jikin bango ta yi zaman dab'as na yan bori...Ta saki marayan kuka mai tsuma zuciyar duk wanda ya saurara....

"Ummy.... Wayyo ALLAH na ummy" Ta shiga maimaitawa tana bubbuga hannuwanta a kasa.

Bappah Auwalu yana tsaye daga bakin kofar dakin bawa marasa lafiya na gaggawa temako inda aka shigar da Bappah junaidu da yayi doguwar suma suna bashi temako don ya farfado.

Nusaiba na gefe tana girgiza kai... Mutuwar Hindu kwarai matuka ta girgiza ta. Hawaye suka shiga zirarowa daga idanun ta ..

Su Layla suka karasa asibitin itada Ahmad... Ganin su suka yi cikin yanayi marar dadi...

Jikin su yayi sanyi. Layla ta karasa wajen Nawraah dake kuka sosai kamar ranta zai fita ta zauna a kusa da ita tana kallon ta,

"Nawraah..... Meya faru? Meya samu ummy? Operation ake ma ta? Ko ciwon ne ya kara tsamari?"

Nawraah ta girgiza mata kai tana zubar da hawaye. Ta saka hannun ta ta share hawayen tace da ita, cikin rawar murya,

"Ummy ta rasu"

"Inna Lillahi wa inna ilaihi raji'un... Ummyn?"

Fashewa tayi da kuka sosai itama ta saka tafukan hannuwan ta akan bakin ta. Ahmad ma ya fara hawayen yana girgiza kansa cikin dimaucewa,

Har tsakiyar dare Bappah Auwalu ya futa ya kawo musu burodi dakyar ya tsawatar musu suka sha da ruwa. Wasa wasa har akayi asubah sukaci sauran burodin...

Wata nurse ta futo daga ciki tana duban su... Kowanne cikin tashin hankali. Bappah Auwalu ne kawai yake kokartawa yana kukan zuciya,

Ta karasa kusa da shi tana masa sallama. Ya amsa ta yana sharce hancin sa da hankici,

"Mashaa Allah an samu ya farfado mun masa allura saboda ya samu nutsuwa . Ita kuma marigayiya idan akwai motar da zaa sakata aciki to idan babu munada kurkura mota ta haya sai a sakata aciki, dubu biyar ne kudin kaiwa"

Ya kada kai yana sanya hannu acikin aljihu zai zaro kudin Nusaiba dake gefe tana duban su ta karasa da sauri,

"Menene ?"

"Kudin motar da za'a saka Hindu aciki ne zan biya meya faru?"

"Har nawane kudin?"

"Menene haka sai? Dubu biyar ne mana "

"Yanzu dubu biyar din zaka kwasa ka bayar?"

"Bakida hankali Nusaiba wallahi bakida hankali "

"To ai gaskia ne. Shi ya bayar mana.... Dubu biyar dinnan idan ka kwasa ka bayar ya zamuyi da sayen taliyar...?"

Dogon tsaki yayi ya girgiza kai cike da takaicin maganganun ta yace,

"Zaki matsa ko sai na hanbare ki?"

"Hanbareni halin naka zaka nuna a bainar jamaa hanbare ni Auwalu"

Kudin ya kirga da sauri ya mikawa nurse din ta koma ciki.

Ya bar Nusaiba a tsaye tanata banbamin mita. Ya nufi wajen Ashir ya riko shi

Ashir din ya fashe da kuka. Bappah Auwalu ya riko shi ya rungume shi tsam a jikinsa

Ashir ya shiga rusgar kuka tamkar karamun yaro yana kiran sunan mahaifiyar ta su

"Ummy... Ummy"

"Dan Allah ku dai na mata kuka, ku dai na zubar mata da hawaye. Addua take bukata yanzu ba zubar hawayen ku ba. Soyayyar kadai da zaku nuna mata yanzu addua ce. Sai tafi bukatar ta. Kuyi hakuri dan Allah. Uhm munyi rashi kam . Allah ya gafartawa Hindu ya kyautata namu zuwan. Bar kuka Ashir dan Allah kaji? Alhamdulillah jikin mahaifin naku ma ya farfado yanzu nurse ta fada. Kuma zamu kai gawar gidah don a sallace ta.,"

"Wayyo Allah na. Ummy na wayyo Allah " Nawraah ta shiga nanatawa tana cigaba da hawaye.

Bappah Auwalu ya shiga wajen da aka rufe gawar malama Hindu da wani yadi shudi baki daya ya rib'e ya koma kalar jini. Saboda tsananin jinin dake futa daga jikinta har yanzu. Tun sanda aka kawo ta. Daman bayan likitocin sun yi gwaje gwajen su angani ta samo karaya takwas. Hudu a kwibi. Biyu kafafun ta daya hannun ta. Yayinda dayan Kuma gefen wuyan ta. Sai internal bleeding shima data samu. Sai Kuma jini daya taru a kwakwalwar ta. Sai ciwo a gefen goshin ta da aka mata dinki har zuwa lebenta. Domin fuskar ta ma ta rabe gidah biyu. Da sauran ciwuka Wanda ba zasu kirgu ba don da tayi rai ma ba lalle ta cigaba da moruwa ba, kasancewar spinal cord dinta ma ya tsinke.

Bappah Auwalu ya saka hannu ya toshe bakin sa da tafin hannunsa alokacin daya shiga dakin yaga an lullube Hindu har kanta. Dankwalin data saka a kanta shi aka rufe fuskar ta. Tabbas kayan data saka ne dazu da ta je gayshe su.

Kwakwalwar sa ta shiga tariyo masa ashe dama bankwana take musu na tafiya tamkar wasiyya? . .

Wani siririn hawaye ya silalo masa ya sharce da bayan hannunsa sa.

Tsayawa yayi aka gama cike ciken da zaai na takardu kasancewar irin wannan idan aka kawo marasa lafiya ranga ranga haka magashiyan, To police na shiga cikin case din.

Don haka anyi dikkanin abunda ya dache daga karshe maaikatan suka Kai gawar malama Hindu cikin mota yar kurkura aka saka ganye agaba da bayan motar

Ballah Auwalu ya tattara kan su baki daya yaje su tafi gidah zaa yiwa malama Hindu wanka a sallace ta...
.
Bappah junaid da allura ta sake shi ya dubi Karin ruwan da ake masa ya fizge shi da karfi ya mike Yana dafa bango ya fita

Likitocin sukai kansa suna kokarin mayar dashi dakin hutun na marasa lafiya atafau yaki yace shi gidah zashi shima a sallaci malama Hindu da shi.

Ba yadda sika iya haka suka kyale shi bayan sun bada maganin da aka saya masa.

Akayi hayar mota ta debe su baki daya suka koma gidah

Ko da suka koma gidan ma sabon shafin alhini sika bude. Masu kuka na yi masu surutai nayi masu dukan kansu nayi.

Aka Kira yaran nasu baki daya lokacin da aka gama yiwa marigayiya malama Hindu wanka aka nadeta cikin likkafini fuskar ta kawai aka bari abude saboda yaran su gana da ita na karshe suyi mata addua. Fuskar ta takara kyau tamkar tana murmushi .

Ataree suka shiga baki daya har bappah Junaid kowanne da addu'ar da yake suna sake bude babin wani kukan mai kuna

"Allah ya jikan ki da rahamar sa Hindu Allah ya yaye Miki dukkanin zunuban ki ya sadaki da ajnabin rahama . Rabbi ya karbi bakuncin ki yasa karshen wahalar kenan. Ba abunda kikai min Hindu idan ma da akwai na yafe miki duniya da lahira Allah ya gafarta miki" bappah Junaid ya karasa fada har yana dora kansa akan gawar bappah auwalu ya fita dashi dakyar.

"Ummy ... Ummy Allah ya gafarta miki Allah ya yafe mi ki, Allah ya sa aljanna makoma agare ki ummy. Ummy na rike alkawarin ki dayardar Allah zan cigaba da rike yan uwana har karshen rayuwata ummy" Ashir ya fada shima ya tashi ya mike ya fita kamar yadda bappah Auwalu yace kowanne idan yayi sai yabar dakin

"Ummy Allah ya jikan ki Allah ya jikan ki ummy Allah ya jikan ki ya gafarta miki ya shayar da ke ruwan alkausara" Cewar Ashfeef ya mike da kyar ya fita yana boye hawayen sa

"Ummy.... Ummy na... Ummy Allah ya jikan Ki da rahama Allah ya gafarta Miki Allah ya kyautata makwancin ki Allah ya sa aljannatul firdaws makomar ki ce, ummy inshaa Allah indai har Ina raye da raina da yardar Allah sai na kwato Miki hakkin ki da dik Wanda yayi Miki wannan mummunan hukuncin . Ubangiji Allah ya dafamun ummy. Inshaa Allah, Allah sai ya tozarta su ya wulakanta su ya d'ai d'aita su. " Mikewa tayi dakyar ta futa tsna sake fashewa dakuka... Nusaiba ta bi bayanta da kallo tana nazari akan kalaman ta na karshe... Suwaye suka kàshe Hindu? Nawrah tasan wani abu kenan? Lalle akwai sauran kallo a gaba idan da rai. Domin Nawraah KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA....

"Bappah... Ummy ta mutu yaushe zata dawo eh?" Amnah ta fada tana rike kafar wandon bappah Auwalu .m

"Allah ya miki albarka Amnah Allah ya raya ki ya tsare ki kinji?" Ya fada mata yana kokarin mayarda kukan daya tayo masa

Waje ya futar da ita bakin kofa. Nusaiba dawasu mata makota suka sake rufe gawar malama Hindu har zuwa fuskar ta suka daure.

Aka sanyata a tabarma aka kullubeta da wani zanun aka sanyata a makara. Bappah Auwalu ya kira su Ashir aka sallaceta aka kaita gidan ta na gaskia

Kafin a fitar da ita daga gidan sai da akayi dagaske yaran ta gaba daya da bappah Junaid sika birkice suna riko makarar suna hawaye kowanne yana surutai kamar mahaukata. Dakyar aka banbare su aka fita da ita zuwa makabarta aka binne ta

Ta samu yabo sosai daga bakunan jama'ar da suka santa. Takuma samu mutane sosai da suka halarci jana'izar ta aka sallaceta suka kaita gidan ta na gaskia.

Sannan aka dawo gidah akayi cirko cirko unguwar tayi tsiit. Yayinda zuriyar hamidniyya Lebanon tamkar ruwa ya cinye su saboda alhini . Hakika baa taba musu mutuwa data grigiza su bayan ta yafendo ba sai wannan ta rasuwar malama Hindu, Mai dakin bappah junaidu, Kuma mahaifiyar su Ashir, Ashfeef, Nawraah da kuma auta Amnah...

_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_


_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[3/1, 7:15 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_


_✍️:MX_


_27_


:::::::::
*Haka* rayuwar ta cigaba da garawa.... Bayan kwanaki arba'in da rasuwar malama Hindu. Dangi na kusa dana nesa duk sun Kokkoma inda suka fito. Yayinda kowanne ya cigaba da rayuwar sa idan ka cire ahalin na malama Hindu da mutuwar ta dake su kwarai matuka...

A Kwanakin ne Kuma hajia qibdiyya dake kasar waje ta kira wayar malama Hindu dake hannun Ashir.

Ya amsa mata bayan sun gaysa ne data tambayi malama Hindu yake sanar mata cewar ai Allah ya mata rasuwa tun kwanaki...

Hakika mutuwar ta daki hajia qibdiyya ji tayi tamkar da Wasa ko Kuma waswasi kunnenta yake mata sai data sake tambayar sa har sai uku Yana tabbatar mata sannan ta amince.

Kuka ta fashe da shi tun awayar tana sallallamin wallahi batada masaniya. Don kwana biyu itama wayar tata bata hannunta sakamakon ta haihu dan ba rai kuma ciwon ta ya tashi na hauhawar jini sai da mai gidan nata ya sake zuwa yayi ciku ciku ya sake canza date din ranar da zasu dawo zuwa dogon zango mai nisa.

Ashir sai ya koma bata hakuri jin tana kuka sosai mutuwar ta dake ta. Dakyar ta iya kashe wayar bayan ta bashi mai gidan ta Dr. Dollars ya musu gaisuwa. Ta Kuma bawa yaranta daya bayan daya sunyi musu gaisuwa ta wayar. Ta kashe wayar jikinta asanyaye

Sai datayi kuka ta koshi sosai har sai da zazzabin ya tasar mata ta kira Dr bintu a waya don tasan Kila batada masaniya bata gaya mata ba bayan sunyi waya jiya da su .

A handsfree ta saka wayar bayan sun gaysa. Murya a cike da alhini tache,

"Baki da labarin rasuwar da akayine Dr bintu ko kuwa mantawa kike baki sanar min?"

"Rasuwa kuma? Rasuwa fa kikace? Waye ya rasu? Kinganni a zaune Kinsa na mike a tsaye. Bangane ba waye ya rasu eh?"

"Hindu dai mai aikina da ke maki aiki a yanzu"

"Innnalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Wallahi bansani ba. Yaushe ta rasu? Rannan tazo da yamma kamar yadda nace mata tazo da yamma tayi abinci wlh har take cewa zata dena aikatau. Naceto shikenan. Dama inata cewa kwanaki biyu shiru idan nakira wayar ta ma a kashe nache to inaga hutawar take bari nan da kwanaki kadan sai na kirata ko naje da Kai na na Kai mata kudin sallamar ta wannan watan meya sameta ? Zazzabin nan da akeyi ko Kuma tana da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login