Showing 42001 words to 45000 words out of 66781 words

Chapter 15 - KWANKWASON JIMINA BOOK 1 hausa novel

24 Aug 2024

13626

tunda ummyn ta rasu ya dawo tamkar ba shi ba ya zama shiru shiru baya magana gaba daya sai ta kama. .

"Nawraah... Menene haka?" Bappah junaid yace da ita yana kallon ta

Dr. Bintu gabanta ya tsananta bugawa tayi hanzarin seseta kanta. Bappah Auwalu yace,

"Nawrah ya Isa. Ai da yardar Allah Hindu yar aljanna ce. Lokacinta ne yayi. Kuma wannan koma wanene kowacece da sukayi aika aiken nan sai dai muce ubangiji Allah ya saka mana ya biya mana hakkin mu a madakata. Allah Kuma ya bayyana mana su tin a duniya. Hajiya kiyi hakuri kinsan yarinta. Nawraah, Tunda akace a titin nan haka ta rasu kinsan tare ranar suka fita. To abun ya tabata sosai ne wallahi" bappah Auwalu ya ce da dr bintu cikin tabbatarwa

Tayi murmushi tana kallon Nawraah tace,

"Nawraah Allah ya gafartawa mahaifiyar ku kinji? Wallahi banida masaaniyar mutuwar ta ma sai da yar uwata kawata hajia qibdiyya uwar dakinta ta farko ta kirani take gayamun dazu. Wallahi sai na kasa zaune na wuce ofishin mai gidan nake sanar masa. Abubuwa sun masa yawa shi Kuma. Shine fa yace na kawo kayan abincin Kafin yazo. Kuma wallahi nima inata Kiran wayar ta a kashe don nayi mamaki ma da hajia qibdiyya tacemun ta samu wayar Hindu nan take sanar mun ai Hindu ta rasu Kuma accident nema muka kiyasata ranar da tazo gidah na ne ai . Wallahi na shiga dimuwa fiyeda yadda baki zai furta. Don kudin aikinta na wannan watan ma wallahi bata karba ba. Yana waje na, Gasu ma nace bari na kawo . Allah ya jikan Hindu ya gafarta mata"

"Ah kin kyauta. Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa .. Amin"

"Allahumma Aameen. Ni zan tafi sai mai gidan na wa yazo inshaa Allahu, Nima zan sake waiwayowa. Allah ya baku hakurin rashin ta"

"Ko ruwa baa kawo miki ba" nusaiba ta fada tana mikewa tsaye itama

Dr bintu tace da ita,

"A koshe nake karki damu. Nagode. To sai anjiman ku"

"Sai anjima, Allah yabada ladan "

Ficewa tayi da sauri nusaiba tabi bayanta tana cewa da ita,

"Angode sosai... Sai da safe."

Dr bintu ta daga mata hannu kawai alamar bye bye, ta shiga bayan mota da sauri driver yaja suka tafi. Ta saka hannunta akan kirjinta saboda yadda yake mata duka.

Tiryan tiryan maganganun Nawraah suka shiga mata yawo a kwakwalwa, Wannan wace iriyar yarinyar ce ne? Bata mantuwa? To me take tunani kenan! ? Lalle wannan yarinyar sai anyi dagaske akanta kar ta ballo musu ruwa

Duk kuwa da yadda ac din motar ke turarawa hakan bai hana tashin hankalin da Dr bintu ke ciki ba jikewa jagab da ruwan gumi tamkar tayi wanka da kayanta a jike..

Har suka koma gidah bata daina nazari akan maganar da Nawraah tayi ba...


Tirk'ashi!

_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_


_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_

_K'K'J_
_(M/W/S)_


_✍️:MX_


_30_


:::::::::

   Tana zaune akan sallaya tun sallar asubah data tashi bata koma bacci ba, Bacci ya kauracewa idanun ta ..

Kamar ko da yaushe tana karanta wasu surori na daga cikin alqur'ani ta ciki harda su suratul Kauthar da Mulk ta roki Allah ladan ya kai wa mahaifiyar su ummy da sauran musulmai baki daya da suka rigamu da gidan gaskia ..

Mikewa tayi bayan ta karasa sauraron addu'oin ta tayi azkhar. Bandaki ta shiga ta dauraye shi kasancewar akwai wuta. Kuma da ruwa ko'ina a cike...

Ta dubi autar su Amnah dake baccin ta ahankali tana sauke numfashi. Ta rankwafa tana duban fuskar ta sosai. Daman kanwar tasu duk cikin su tafi su debo kama da mahaifiyar ta su marigayiya Hindu .

Kallon ta take tana hasaso fuskar ummyn ta su. Da tana raye da tuni yanzu tana kasa ta fara hada karin kumallo da kintsa gidah da sauran su ..

Hawaye sirara suka shiga zirara daga idanun ta ta saka kasan dankwalin ta ta goge..

Mikewa tayi ta sauka kasa don sharewa, ko'ina tas an share har da dorin kamshin turaren wuta na tsinke dake ci daga gefen wata huda..

Motsin karar kwanuka data ji ne daga kitchen yasa ta nufi kitchen din tana kiran sunayen,

"Hamma ne ko Hamma Ashfeef?" Ta karasa shiga cikin kitchen din bakinta dauke da sallama.

Ashir ne a tsaye, Yana gyara zaman kwanuka acikin kwando.

"Hamma" Ta kira sunan sa

Ya juya jin kamar an kira sunan sa. Yana hangota yayi murmushi yana goge hannuwan sa ajikin tsumma,

"Nawraah"

"Naam Hamma... Ai nayi sallama na kira sunan ka baka ji ba"

"Banji ba Nawraah. An tashi lafiya?"

"Alhamdulillah Hamma. Ina kwana?"

"Alhamdulillah Nawraah..."

"Hamma ai nace ka barshi zan dinga yi Allah. Naga har shara kayi ka gyara ko'ina"

Murmushi Ashir yayi, Yana shanya tsumma akan wani karfe yace

"Kaki damu babu komai ai.... Duk yiwa kai ne, Na gaya miki ai nace ki dinga wanke bandakin sama kawai kina gyara dakin ku dana abbiey. Kasa zan gyara inshaa Allah. Namu bandakin Kuma Ashfeef zai dinga wanke shi. Kije ki koma ki kwanta oh ba da makaranta ba yau kuna da exams?"

"Hamma Allah ya saka maka da mafificin alkhairin sa. Ai bana jin bacci tun Kiran sallar fari. Zan dai yi wanka sai nazo naga abunda zaa dafa"

"Kakki damu ai na dafa shayi tun jiya Kuma an sayo biredi."

Hawaye ne ya cika idanun ta taf. Ashir ya dubeta yana girgiza mata kai,

"Mayar da wannan kukan na meye?"

"Hamma dukkanin abubuwa da kake ko ummy na nan sai haka. Gaba daya baka hutawa"

"Idan banyi muku ba wanene zai muku Nawraah? Bakisan cike nake da farin ciki ba idan Ina taya wasu abubuwan na aiyukan gidah? Banda wani babban burin daya wuce naga farin ciki shimfide akan fuskokin ku. Nawraah ummy da kanta ta bani amanar ku tun da ranta... Don haka duk abunda kikaga nayi muku wallahi ban fadi ba. Fatan Allah ya buda mana duka ya yalwata mana kofofin arzuka Amin. Allah Kuma ya jikan mahaifiyar mu da dukkanin musulmai baki daya Aameen"

"Allahumma Aameen Hamma.. Tohm shikenan. Allah ubangiji ya dafa maka ya shi maka albarka ya baka mata tagari Amin"

Murmushi yayi jin ta ambaci maganar auren sa. Ta kalle shi tana murmushin itama tace,

"Hamma ko budurwa ma baka da ita fa ko meyasa oho"

"Nawraah ai yanzu ba lokacin kule kule yammata bane, Ta gidah ake yanzu bana waje ba. Idan komai yayi normal agidah sai mu duba mugani."

"Amma Hamma lokaci na kurewa ai"

"Aa fa... Komai da nasa lokacin ballantana ni bana son kule kulen yammatan nan haka. Fatana kawai Wanda zan nema ma ta kasance ita zan aura kingane? Banason yaudara. "

"Hakane kam Hamma Allah ya dafa maka adukkanin abunda ka cinma buri."

"Allahumma Aaamin Nawraah"

"Ga ruwan zafi nan a bokiti ki juye kiyi wanka zan Kara wannan da zai tafasa akai Wanda ya riga tashi bayan ke sai yayi wankan"

"Tohm Hamma yanzu kuwa. Bari naje nayi"

Ta dakko bokiti ta debi ruwan ta haye bandakin su na sama tayi wanka. Tanata sauri tana shiryawa kasancewar a yau ne zasu zana jarabawar su ta karshe ta gama sakandire.

Tana cikin shiryawa Amnah ta tashi lokacin garin har yayi haske. Tayi mata wanka ta saka mata kaya suka sauka kasan a tare

Abincin karin kumallo suka ci. Suna cikin ci Ashfeef ya tashi shima yayi wanka ya shirya zuwa kayan aiki zasuyi fenti ra fenti don sun samu aiki na fente wani site da ake ginawa...

Daga baya ba jimawa bappah junaid ya sakko sika gayshe da shi baki daya. Dakyar yaci abinci kadan ya tashi ya koma sama yayo wanka bayan Ashfeef ya Kai masa ruwan zafi sama.

Nawraah taje tayiwa bappan su sallama sai ta dawo, zata tafi zana jarabawar ta ta karshe ta kammala sakandire, Yayi musu addu'ar temako da samun nasarar jarabawar.. ya dakko kudin break ya bata, tayi masa addua ta futa rike da hannun nawrah kasancewar zata kaita gidan bappah Auwalu Kafin su dawo tunda Hamma ma dashi zaai aikin fentin...

Ta kai Nawraah gidan bappah Auwalu wajen Nusaiba. Daga nan ta jira Layla ta karasa shiryawa suka nufi makaranta don zana jarabawar..

Da misalin karfe hudu na yamma sika kammala zana jarabawar karshe ta sakandire... Sai fatan samun nasara da dinbin fatan alkhairi ga sabbabin kofofin rayuwa da zasu bude.....

_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_


_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_

[3/5, 7:07 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_


_✍️:MX_


_33_


:::::::::

Amnah yau lafiya gobe babu. Sunata zuryar asibiti duk kudaden hannuwan su suka kare.

An mata tasa tasai an gani tanada ciwon tonsils shi ke sakata amai da yunkurin aman. Sannan typhoid ta mata illa..

Bappah junaidu bayasan bin mutane ko yan uwan sa yana cewa su temaka masa. Don haka ya saka gidan su jingina bada masaniyar kowa ba ya karbu kudin aka yiwa Amnah aiki da shi aka kwantar da su a asibiti sukayi jinya sosai.

Sai bayan da aka sallamo su ne bappah junaidu ya shirya ya tafi ofishin da Alhaji sambaso ya bashi katin.

Ya nufi unguwar har kamfanin akace ya shiga. Ya nufi ofishin zai shiga ya ja ya tsaya jin da akwai mutane aciki suna magana.

Har zai juya yaji an ambaci sunan sa da na matar sa. Sai kuma ya jiyo suna maganar tarin dukiyar dr Abubakar dollars dayake so ta zama mallakin sa har ya saka hannu. Can kuma yake gayawa mutumin, Tsautsayin daya same shi na niyyar illata Malama Hindu sai kuma ya kasheta har lahira. Kafafun Bappah junaid suka gaza daukar sa. Ya sanya hannu a baki ya toshe saboda wani abu daya taho masa. Kafafun sa suka gaza daukar sa. Ya nemi jikin kofar ya jingina saboda wani yanayi na tashin hankali daya samu kansa aciki.

Alhaji sambaso suka gama magana da mutumin na ciki sukayi sallama. Mutumin ya tashi ya nufi kofa zai tafi.

Laptop din Alhaji sambaso ta fara karan shigowar waya ta app ya dauka yana murmushi kasancewar video call ne…

Alhaji ateeks na daga masa hannu yana bude kofar sai ga Bappah junaidu fuskar sa shabe shabe da hawaye. Alhaji ateeks ya dube shi ya wuce dan baisan waye ba ma.

Alhaji sambaso ya ja hannun sa ciki yana rufe ofishin. Ga video call din nata tafiya. Na ciki yanata 'hello hello' yana duban sa.

“Meyasa ka kashe mana Hindu? Me ta maka?”

Alhaji sambaso ya bude baki yana shafo keyar sa yana hura iskar bakin sa mai zafi yace...

"Bangane me kake nufi akai ba. Hankalin ka daya kuwa kasan me kake cewa?"

"Na sani mana, da hankali na duk na ji dukkanin abubuwan da kuke fada, Kai da abokin ka. Kun hada kai kun kwato duniyar Dr abubakhr dollars ta karfin dole. Kun kashe Hindu meta muku? Shin akan wani dalili kuka kashe mana hindu? Ashe kai ka bigeta a mota ka kasheta Alhaji? Yanzu duk wadannan kayan abinci da kake aika mana da sauran su dama duk toshiyar baki ne? To Allah ya tona asiirin ku wallahi Allah kuwa daga yau zaka kwashe kashin ka a hannu"

Ya saka hannu akan mabudin kofa da niyyar murzawa ya fita Alhaji Sambaso yayi hanzarin riko hannun nasa yana duban sa sosai,

"Ka tsaya muyi magana ta hankali ba abunda kake tunani bane"

"Babu abunda zanji. Kuka samu kanku gaban hukuma zakuyi bayani, yanzu a yau zan bankada dukkanin kofofin sharrin ku. Mugaye kawai. Allah ya yi wadai da halayen ka"

Ya sake kai hannu zai fita Alhaji Sambaso ya tare hanyar ya riko shi yana duban cikin idanun sa yace,

"Kasan wanane ni kuwa! ? Na ga alamar ba hankalin ka kake ba, wannan zantukan, Idan kudi kuke bukata zan baka ishasshe yanzu. Dan naga alamar rashin su ya fara taba maka kwakwalwa kake ta surutun magana da sambatu acikn ta"

"Wai ka dauka kudi na sayan mutane? Ka dauka dukiya itace kwanciyar hankali? Ka dauka dukiya itace maganin damuwa? To ka bude kunne ka kaji. Daga yau kwanan ka a doren duniya cikin gidan ka babu kai babu kwanciyar hankali. Inshaa Allahkashin ka ya bushe. Police station zan tafi wallahi wallahi " ya fada yana duban sa cikin tsantsar tsana.

Alhaji Sambaso yayi hanzarin riko kafadunsa. Bappah junaidu ya fuzge. Alhaji ya sake riko shi. Suka shiga kici kici har zuwa wajen wata baranda. Bappah junaidu ya jinga a jikin bango yana magana cikin fushi

Jiyuwar nan da Bappah Junaid yayi Alhaji Sambaso ya hada shi da karfen baranda yana dukan cikin sa.

Ya daga hannu cikin tsantsar tashin hankali da tsana ya shararawa masa mari

Alhaji Sambaso ya rike kuncinsa, Yana duban bappah Junaid daya sake daga hannu zai kauda masa wani , Alhaji Sambaso ya jinginar da shi a jikin baranda, bappah junaid ma ya tattake ya buga shi da kofar.

Alhaji Sambaso cikin hazalar fushi ya cakumi wuyan bappah junaid ya hankada shi da karfunan barandar.

"Kashe ni zakai? Nima ka mar yadda ka kashe matata?"

Alhaji Sambaso ya saka hannu, Yana rufe bakin bappah Junaid dayaki ya sake cakumar sa. Alhaji Sambaso ma ya riko tasa yana sake cakomar rigar sa yace,

"Shashasha"

"Kai ne shashasha, Mugu, Azzalumi...."

Garin riko shi zai naushe shi ya hankada shi. Bappah junaidu ya fada kasa ji kake 'Timmmmm

Kamar kara ya fada, Take kansa ya fashe bai shura ba ya mutu awajen alokacin....

_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_


_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[3/5, 7:07 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_


_✍️:MX_


_34_


:::::::::

Rufe bakinsa yayi da sauri, yana zare idanuwa jin muryoyi suna kururuwa daga waje lalle da alama mutumin ya mutu....

Tun sanda mutumin ya shigo dama yayi hanzarin danna recording kiran na video call da sukeyi....

Alhaji Sambaso ya saka hannunsa ya shafo kasan keyar sa, Yana rufe bakinsa da tafin hannun sa....

"Naga kaman labarai kake kalla ko? Bari na kashe na sake kira yanzu nima zanyi abune?"

Ya jiyo murya daga cikin laptop. Dama bai katse video call din ba? Ai baki daya ya manta.

Ya dafa teburin yana kallon sa ta cikin system din yace

"Dama baka kashe ba? Me kake nufi da labarai? Ka saurari maganganun da nake fada ne?" Alhaji Sambaso ya tambaye shi cikin tsananin tashin hankali

Ya girgiza kansa yana bashi amsa da

"No da naga Jana kallon labarai ne kome. Magana sama sama sai na tashi na shiga bandaki fitowata kenan kuma naga kaman da kanta ma muna waya"

"Ka tabbatar abunda ka sani kenan?"

"Eh mana... "Ya kakaro daria ya sake cewa,

"Futsari na tashi nayo ma sai na tsaya na karba parcel dina da aka kawo yanzu"

"Oh okay. To shikenan zamuyi magana, yanzu zamu shiga meeting ne " ya katse kiran yana rufe laptop din baki daya..

Zagayawa yayi ta kofar baya emergency exit dinsa wanda ba kowa bane ya sani a kamfanin ya fita ta ciki ya koma kasa...

Nan da nan maaikatan wajen suka fara taruwa akan gawar bappah junaidu....

Da sauri wasu maaikatan suka nufi ofishin nasa suka bude baya ciki. Aka dudduba bayan ko'ina

Nan suka shiga fara kiraye kirayen wayar sa. ... Ya fito daga cikin wani guri a kasan kanfanin da suke kira da lodge .

Daki ne da parlor da bandaki inda manyan maaikatan suke shiga su huta.

Nan ya futo daga ciki yana mitssika idanu,

"Ah ranka ya dade ashe baka cikin ofishin na ka?" Cewar wani leburan kamfanin daya nufe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login