Showing 36001 words to 39000 words out of 177624 words
yaron da Zahrah ta amince dashi, yake zuwa zance wajenta, idan kuma bazaka mantaba ai nafaɗa maka shiɗin yaron kirkine, na tabbatar da cewa baisan haka yafaru da ita ba, da nasan dole zaizo" Baffa yaƙare maganar yana mai jinjina kai..
"Shine yayi mawa Zahrah fyaɗe !" Dr S.S yafaɗa murya a kausashe,
Gaba ɗaya idanunsa Baffa ya zaro, alamar maganar ta dake shi, "Zaid fa kace likita !" Baffa yafaɗa cikin kaɗuwa,
"Ƙwarai kuwa domin kuwa jiya ta ambaci sunansa, nakuma ji da kunne na, amma tunda kace ba zaku kai case ɗin kotu ba, bakomai ni zan wuce" Dr Sadeeq yafaɗa yana mai miƙewa tsaye, bayan yaciro damin kuɗi ya a jewa Baffa kan tabarma,,
"A'a hadda ɗawainiya haka likita? to to munagodiya!" Baffa yafaɗa cike da farinciki,
(hmm mai hali dai baya fasa halinsa)
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! Malam hayaƙi, hayaƙi Malam a ɗakin Zahrah !!" Inna tafaɗa cike da tashin hankali, ai da sauri Dr Sadeeq da baffa, suka nufi ɗakin Zahrah'n wanda hayakin haryasoma cika tsakar gidan, dayake ƙofar bata da wani ƙarfi duka ɗaya Dr S.S yayi mawa ƙofar ɗakin tabuɗe, gaba ɗaya ɗakin yaturnuƙe da hayaƙi yayinda wuta kecin wasu kaya dake aje tsakiyar ɗakin, gefe da kayan kuma Zahrah ce durƙushe tana kuka, har wutan yakusa ƙarasowa gareta,
Cikin zafin nama, Dr Sadeeq yasanya hanunsa, ya janyeta daga tsugunnen da take, kai tsaye waje yafito da'ita, domin kuwa hayaƙin yasoma shiga cikin maƙoshinsu, Baffa da Inna kuwa ruwa suka ɗebo suka kashe wutan,
Riƙeta yayi gam yayinda ya kafeta da idanunsa da suka rune tsabar ɓacin rai,
Baisan meyake damuntaba, rashin hankaline ko kuma sangartane baisaniba, yasan cewa tanajin ciwo a cikin zuciyarta, amma abun da take ƙoƙarin aikata mawa kanta, kama yake da taɓin hankali, ƙoƙari yayi wajen danne zuciyarsa, haɗe da saisaita muryarsa, "Maiyasa Zahrah ? bazaki ɗau ƙaddaranki ba ?" yayi mata tambayar cikin tausasa murya, hawayene suke gudu haɗi da ambaliya akan fuskarta, gaba ɗaya jitakeyi duniyar najuya ma ta, dawowanta gida yasake tada mata da mikin dake maƙare cikin zuciyarta, duk da kuwa dama cewa mikin bai wau ya kwanta ba ne,,
Saurin saketa yayi sakamakon ƙarasowar Baffa da Inna wajen, zamewa tayi aƙasa dabas tana mai sakin kuka,
Kallon Baffa Dr Sadeeq yayi, kafun Baffa yace komai Dr Sadeeq yace, "Baffa ni nawuce sai nasake zuwa "
"To Likita mun gode ka gai da gida " Inna da Baffa suka haɗa baki wajen faɗa, da "To" kawai Dr Sadeeq ya amsa musu haɗe da sa kai yafice daga cikin gidan,
Kama hanun Zahrah Inna tayi suka zauna akan tabarma, cike da damuwa Inna tasoma cewa "Maiyake damunkine Zahrah ? sai kace akanki aka fa ra yin fyaɗe? gaba ɗaya duk kinbi kinɗaga hankalinki, muma kin ɗaga mana namu hankalin, a gaskia nida Baffanki munsoma gajiyawa da wannan halin naki, bayan kinso caka mawa kanki almakashi, likita ya hana, yanzu kuma ƙona kanki kikesonyi, wai kina cikin hankalinki kuwa Zahrah?"
"Gaya mata dai Salame, domin nima nan nasoma gajiya da rarrashi, yanzu dakika ƙona kayayyakin daya baki, shiɗin kika ƙona ne? tambayanki nake shiɗin kika ƙona ?" Baffa yafaɗa cikin faɗa faɗa, domin ya lura idan suka biyewa Zahrah tofa bazata taɓa daina yunƙurin kashe kanta ba..
Zuciyar Zahrah ne tasakeyin rauni, " Allah sarki ni, komai nayi, ganin laifina suke, shin bancancanci rarrashi da kulawaba? fyaɗe akayimini amma hakan baiwani shiga jikin kowa ba, natabbata idan da iyayena suna da rai, to tabbas da bazasu taɓa kwantar da hankalinsu ba, kuma nasan dolene sai sun ɗaukarmin fansa, bakuma zasu taɓa gajiyawa daniba, wayyo Allah na mutuwa tayi mini yankan ƙauna daku iyayena !!" maganar da Zahrah take faɗa kenan a cikin zuciƴarta, hawayenta ne suka sake tsananta zuba, sai yau ta tabbatar cewa Maraici bashi da daɗi, sai yau tasake tabbatar da cewa Allah ne kaɗai gatan ta, Zaid ya cuceta, yayi mata babban tabo wanda hargaban abada ba zata taɓa mantawa dashi ba, "maiyasa Zaid ?" tasake tambayar kanta bayan kuma tasan bata da amsa,,
Haka Inna da Baffa suka wuce ɗaki suka barta zaune a tsakar gida tana tsiyayar hawaye, babu mai rarrashi.
Tuƙin mota yake amma gaba ɗaya hankalinsa yanaga yanda yabaro Zahrah, tsantsar tausayinta yakeji, yanason taimaka ma ta amma to tayaya? ta wacce hanya? duk alokaci ɗaya ya tambayi kansa, wayarsa ce tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, Zabba'u shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar, ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da ɗaukan wayar yakara a kan kunnensa,
"Cike da sangarta Zabba'u tayi masa sallama, amsa sallaman yayi a daƙile haɗe da cewa "Ganinan zuwa" ƙit yakashe wayar haɗe da cillata kan kujeran mai zaman banza, shi sam baisan yanda zaiyi da Zabba'u ba, amma a zahirin gaskia ɗabi'u da tarbiyanta basu masa ba,duk da kuwa cewa ƴar uwa take a garesa.
New York City
Tsaye yake agaban wani tangamemen cupboard paper, wanda yake liƙe ajikin wani abu kamar allo, sanye yake da 3 guater jeans, yayinda yabar gaba ɗaya surar jikinsa a waje, kasancewar baisanya rigaba, babban abun ɗaukar hankali ajikinsa shine lafiyayyun, 6 packs ɗinsa, dake kwance raɗa raɗa akan cikinsa, riƙe yake da wani dogon pen a hanunsa da'alama dai wani abu yake zanawa mai mahimmancin gaske,, ƙayataccen murmushinsa yasake, haɗe da ɗaukan glass cup ɗin da wine ɗinsa ke ciki, yakai bakinsa, saida ya shanye duka wine ɗin dake cikin kufin, kafun ya aje kofin kan wani ɗan ƙaramin table dake kusa dashi,
Hanunsa yasanya akan kyakkyawar fuskar daya zana a jikin cupboard paper ɗin, a hankali yashiga shafa zanen , hanunsa yakai dai dai saitin bakinta, haɗe da shafawa, idonsa ɗaya yakashe haɗe da lasan laɓɓansa,
"Kinkasa barina My Sugar Baby, maiyasa ? " yayi tambayar yana mai tsare zanen dake jikin cupboard papern da ido,
"Bazaki amsaminba ko? fushi kike dani ko sugar baby na?"
Yasake tambayar wannan zanen dake jikin cupboard paper'n.
Murmushi yakumayi haɗe da matsawa daf da cupboard paper'n bakinsa yaɗaura adai dai kumatun ta yamanna mata kyakkyawan kiss, "Kikulamin da kanki kinji My Zahrah!!" yafaɗi maganar cikin shauƙi,, sai alokacin nalura ashe zanen fuskar Zahrah ne raɗau ajikin cupboard paper'n, bakaɗan ba kuma zanen yayi kyau,, kyakkyawan ƙyalle yasanya yarufe zanen, haɗe da ɗaukar wayarsa yafice daga cikin ɗakin...
Yana fita falo Abid dake tsaye tun ɗazu yana zaman jiransa, ya saki tsuka, haɗe da cewa " Wai don Allah maika tsaya yi ? tun ɗazu fa kasan nakejiranka, amma ka shanyani "
Zama Zaid yayi akan kujera haɗe da jawo kwalbar wine ɗinsa, yashiga shan abunsa, ganin haka yasa Abid sauƙe ajiyar zuciya haɗe da girgiza kai, wato dai yau ƴan halinne suka motsa, gaskia Zaid yanada wuyan sha'ani, bakoda yaushe kake gane gabansa da bayansa ba, duk da kuwa tsananin sabon dake tsakaninsu, amma shi kansa wataran idan Zaid ya juye tofa baya iya gane masa.
"Kana yawan shan wine Zaid, baka tunanin zata iya janyomaka matsala nan gaba ?" Abid ya tambaya cike da kulawa, domin kuwa, shi ko za'a kasheshi bazai iya shan rabin wine ɗin da Zaid yakesha a rana ba,
"Maiyashafeka da shan wine ɗina ?sanin kankane natsani sa'ido " Zaid yayi maganar cikin haɗe fuska,
Dariya Abid yayi, domin kuwa yanzu yatabbatar cewa Shu'umin cin nasa ne ya motsa, "Okay i'm sorry bazanƙara ba, amma yakamata ace musauƙa ƙasa, babes ɗin nan fa suna jiranmu " Abid yafaɗa yana mai duba agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa,
"Kaje kawai ka sallamesu, nikam bana ma buƙatar ganinsu, mata duk a bubbushe, ba wani diri mai burgewa, sai kace 1, kaje can kata fama idan zaka iya" Zaid yafaɗa cike da ƙuncin rai,
Dariya sosai Abid yayi, haɗe da tashi kawai yafita daga falon, gaba ɗaya kwana biyun nan yarasa maiyake damun Zaid..
Abid na fita Zaid yagyara zamansa, haɗe da lumshe idanunsa, gaba ɗaya fuskar Sugar Babynsa ne yake yimasa gizo a cikin idanun nasa.
Abuja Nigeria
Zahrah ce zaune akan ƴar yaloluwar katifarta, ta tanƙwashe ƙafafunta, yayinda kanta ke kallon sama, ruwan hawayene kawai ke gangarowa daga cikin idanunta, kallo ɗaya zakai mata wata irin muguwar tausayinta yadaki zuciyarka, domin kuwa wani irin muguwar rama ce ta bayyana a jikinta,
Da sallama Khausar tashigo cikin ɗakin, kamar daga sama haka Zahrah taji muryar aminiyarta ta wato Khausar, tana kai kallonta bakin ƙofa taga Khausar ɗin tsaye tayi turus,,
Ai dagudu Zahrah taje tafaɗa jikin Khausar, haɗe da sakin wani sabon kuka mai sauti, duk da cewa Khausar batasan abun dayake faruwa ba, amma tasan cewa ba lafiya ƙawartata take ba, kawai itama sai tafashe da kuka, hakanan taji wani irin tausayin Zahrah'n yacika zuciyarta, rungumeta tayi da kyau a jikinta, ko kaɗan Khausar batayi yunƙurin hana Zahrah kuka ba, saida Zahrah tayi kuka sosai, kafun ta tsagaita, a hankali take sauƙe ajiyar zuciya,, hanunta Khausar takama suka zauna akan katifar Zahrah'n,,
"Zahrah!" Khausar taƙira sunanta cikin sanyin murya, Zahrah bata iya amsa mata ba, sai ɗago idanunta da suka kumbura suntum tsabar kuka, tayi ta kalli Khausar ɗin,
Zaro idanu Khausar tayi, cike da tashin hankali tace "Zahrah maiyake faruwa ne, tun ranan nake ƙiran wayarki a kashe, nazo gida kuma bansamu kowaba, nazo yafi sau huɗu bana samun kowa acikin gidan, dan Allah ƙawata kifaɗamin maiyake faruwa ?" Khausar tayi maganar cikin damuwa.
"Rayuwata taƙare Khausar, yacuceni,ya yi mini babban illa, dakuma tabo wanda bazai taɓa gogewa ba, ya nakasamin rayuwata, ashe haka ƙaddara zata zomin mummuna? nayarda cewa kowani bawa da'irin tasa ƙaddaran amma ni tawa ƙaddaran tafi takowa muni, danasan haka zata faru dani, dana roki Allah daya kasheni kafun yanzu na...." Saurin toshe mata baki Khausar tayi, cike da ruɗani haɗi da tashin hankali, Khausar tace "Kada kiyi saɓo Zahrah, kinsani acikin duhu, kisanar dani maike faruwa dan Allah, gaba ɗaya kinsani cikin tashin hankali !" Khausar tafaɗa cikin ƙosawa,
"Za..i..d yayi min fyaɗe Khausar !!!" Zahrah tafaɗa tana maisake rushewa da kuka,,
Tamkar anwatsamata ruwan zafi haka Khausar taji ajikinta, lokacin da maganan Zahrah yadaki dodon kunnenta, "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! Fyaɗe fa kikace Zahrah ?" Khausar ta tambaya cikin matsanancin tashin hankali, lokaci guda hawaye suka shiga sauƙa daga cikin idanunta, take jikinta yayi sanyi laƙwas,,
"Yacutar da rayuwata Khausar, ashe haka soyayya ta ke? rama alkhairi da cuta, ashe haka duniya take cike da azzaluman bayi? maiyasa yayi min haka Khausar? mainayi masa? yaruguzamin duk wani farincikin rayuwata, wayyo Allah na Khausar ki karɓi wuƙannan ki kasheni dashi ko da zansamu sauƙi da salama acikin zuciyata !!" Zahrah taƙare maganar tana mai miƙomawa Khausar wata wuƙa da ke aje gefenta,,
Matsanancin kuka Khausar tasanya, haɗe da jawo Zahrah jikinta, ta rungumeta ƙam, kuka suka shiga yi wiwi, babu mai lallashin ɗan uwansa...
((Agaskia banson abunda wasunku sukemin,musamman masu cewa naƙara musu yawan typing, inaso kusani cewa, banda wadataccen lokaci, inazuwa makaranta, inada miji, sannan kuma nima inada wasu uzururrukan, yakamata kuna hakuri, amma wasu har baƙar magana su ke ƙoƙarin gayamin don kawai shekaran jiya nayi muku typing kaɗan, hmm wlhy kunbani mamaki, ni bana neman faɗa da kowa, saboda banɗauki duniya komai ba, shekaran jiya a matuƙar gajiye nake saboda naje school, amma haka na lallaɓa nayi muku typing, a she duk da haka wasunku basu godeba, haka sukaita ƙananan maganganu, wata har cewa take wai tagaji da wayon danake yi,koda yaushe sai nace na gaji, yes dole nagaji tun da dai ni ba engine bace, da za'ace bazan gaji ba, kuma ina da abubuwanyi. kuyi haƙuri my real fans na zage inata faɗa, wlhy raina ne yaɓaci wasu komai kamusu baka burgesu.
Nadawo gareku sisters masu cewa Zahrah tasoma basu haushi sbd abubuwan da takeyi, yaka mata ace kufahimceta, bawai inabin bayan tabane, amma yana da kyau ku yi imagine akan ya mace za taji idan har akai mata fƴaɗe?dole za taji matsanancin ciwo, acikin zuciyarta, kuma dole ne abun zai zama babban tabo wanda bazai taɓa gogewa acikin zuciyarta ba, saboda haka kuyi hakuri kuyi mata uzuri. ))
*18/November/2019**
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier (My ƙwarnafi, da mita, lol 😄)*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Kusha Sha'aninku Team ZAIDU👇🤣*
*1-Rhupys khair*
*2-Maimunerh minah*
*3-Saudat 0ne*
*4-maryam wazeer*
*5-Aisha salis*
*6-Mar'uda*
*7-Oum Zahrah*
*8-Oum Aboul*
*9-Oum saddiqa*
*10-Oum suwaib*
*11-Nana jasko👌*
*12- Halima nancy*
*13-Zuwaira ibraheem*
*14-Aminan bash*
*15-Saudi ghans, real tawajena*
*16- Surayyah*
*17-Shamsiyya-7 shams*
*18- Rauda Umar*
*Kunayi inajin daɗi team Zaidu 🤣 amma fa iyakune kawai team ɗin nasa waƴanda basa ganin laifinsa, lol, nasu Zahrah kam ba'a magana suna cikin ƙunci😥, saura kuma Dr S.S.😂*
*Chapter 33 to 35*
(Kuyi haƙuri nayi mistake, ƙawar Zahrah sunanta Husnah ne ba Khausar ba, kamar yanda nasa a page ɗin baya, Husnah nakeson sawa, to bestyna saita tsayamin arai nasa sunanta,lol.)
Kuka suka shugayi wiwi babu mai lallashin ɗan uwansa, da ƙyar Husnah ta'iya tsagaita kukanta,haɗe da daidaita nutsuwarta, duk da cewa zuciyarta bata daina bugu ba, tamkar ƴar uwa ta jini haka ta ɗauki Zahrah, saboda haka duk wani abu daya faru da Zahrah tamkar da ita yafaru, domin kuwa abokin kuka shi'ake gayawa mutuwa, wannan abotar tasu tasamo asaline tun suna yara, haka kuma sun ƙulla abotansu cikin gaskia da yarda da juna,,
"Bazance miki kidaina kuka ba, Zahrah domin idan nace miki haka, banyi miki adalci ba, sai dai zan sake tunatarmiki cewa akwai Sarkin sarakuna, mai tausayi ga bayinsa, mai amsa addu'an bayinsa, mai basu, mai kuma hanasu, shi ishashshene akan dukkan komai, yanaji,kuma yana gani, sannan kuma shi ya wanzar da faruwar haka a gareki, tunkafun ya halicceki ya tsara, cewa hakan zai faru a kanki, kada kiyi jayayya Zahrah, domin kuwa babu wani bawa a duniya daya isa ruguza tsarin Allah, Allah baya bacci, yanasane da wanda sukayi cuta, dakuma wanda aka cuta, zaifi kyau ki miƙa al'amuranki garesa, haƙiƙa nasan cewa abun da Zaid yayi miki, abune mafi matsanancin ciwo acikin rayuwar ƳAMACE, amma kashe kai, ko kice a kasheki banaki bane Zahrah, rungumar ƙaddara ita tafi dacewa dake, haƙiƙa nasan cewa har gaban abada bazaki mantaba, amma inaso kiɗauki ƙaddaranki, kimiƙawa Allah lamuranki, da sannu zakiga sakayya, ke ba jahila bace, da iliminki na addini dana zamani, saboda haka inaso kiyi amfani da wannan ilimin naki wajen ɗaukar ƙaddaranki hanu bibbiyu, kada kice na faɗi haka ne don banasonki, wlhy inasonki ƙawata, inajinki tamkar jinin jikina, kawai dai hakan shine mafita !!" Husnah tayi maganar cikin tsananin tausayawa, yayinda ruwan hawaye suka gama wanke fuskarta...
A hankali Zahrah taɗago idanunta dasuyi jajur tamkar anwatsa musu garin barkono, ta kalli Husnah, sosai maganar Husnah yadaki zuciyarta, sai dai yazame mata dole shiga ƘUNCIN RAYUWA, da ace zata buɗewa mutane ƙirjinta suga, cikin zuciyarta, to tabbas da tayi hakan, domin tasan duk wanda yaga ciwon dake mamaye da zuciyarta, to tabbas dole ne zai koka mata, domin kuwa wani irin danƙareren ciwone yabaibaye zuciyarta, wanda batasa ran zata warke har gaban abada,
" Ashe babban kuskurene ɗaukar soyayya ka bawa wanda yafika? menene aibuna dan nafito a mace? me maza sukaɗauki mata ne? a she dan kana talaka shikenan kai bakomai bane? bakuma ka da ƴanci? ya ketamin haddina da ƙarfin tsiya, yanunamin ƙarfi da kuma fifiko, duk dan kawai ina mace, maiyasa ya tsalleke dukkan mata yazo kaina nida banda kowa sai Allah? nayi masa kuka, nayi masa magiya, na roƙesa amma ya toshe kunnuwansa, yacire duk wani imaninsa ya cutar da rayuwata, kigayamin miye laifina dan nafita cikin hayyacina ? ki faɗamin shin bancancanci in haɗiyi zuciya in mutu ba, f...ya...ɗ...e fa yayi mini Husnah!!!" Zahrah tafaɗi maganar cikin matsanancin kuka,
Duk yanda Husnah taso ta sake danne zuciyarta kasawa tayi, kawai sai ta sake sakin kuka haɗe da rungume Zahrah ƙam acikin jikinta,
Saida sukayi kuka sosai, kafun suka soma sakin ajiyar zuciya, take zuciyar Husnah tayi sanyi, amma banda ta Zahrah, domin babu wani sanyi daya ragewa zuciyar Zahrah.
A hankali Husnah tashiga shafa bayan Zahrah, wacce haryanzu sheshsheƙan kuka take,
" Ki tsaida kukanki Zahrah, kuka baya maganin komai, sai dai ya sanyamiki ciwon kai, addu'a ita kaɗai ce magani, nasanki Zahrah, inakuma da yaƙinin cewa baki kai kukanki ga Allah ba, kiji rani inazuwa " Husnah tafaɗa tana me miƙewa tsaye, kaitsaye ficewa tayi daga ɗakin, yayinda Zahrah tafaɗa kan katifa taci gaba da kukanta,,,
Mintuna kaɗan Husnah tashigo ɗakin hanunta riƙe da wasu magungunan da likita ya kawowa Zahrah, wanda takarɓo wajen Inna,,
Ledan da tashigo dashi ta jawo, haɗe da ƙarasowa wajen Zahrah, tamkar ƴa da uwa, haka Husnah ta jawo Zahrah jikinta, cike da tausayi haɗi da rauni tace " Kidaina kuka dan Allah Zahrah, kinga ko na tahomiki da abincin da kikafi so, Shinkafa da Kifi, Mom ce ta dafa " Husnah taƙare maganar tana mai buɗe wni kula, wanda ta ciro a cikin ledan da tazo dashi,
"Nasan bakici komaiba, kuma koda nace kici ma, cemin zakiyi kin ƙoshi, amma dan Allah kici ko kaɗanne zanji daɗi Zahrah, baki da kowa sai Allah, amma kada kimanta nidake tamkar gudan jini muke, damuwarki damuwata ce " Husnah tafaɗa tana mai zub da ƙwalla,
Kallonta Zahrah tashigayi, take kuma zuciyarta ta karye, sai kawai tafaɗa jikin Husnah, tashiga sauƙe ajiyar zuciya,,
Cike da lallami Husnah tashiga bawa Zahrah shinkafa da kifin da takawo, duk dacewa maɗaci yafi abincin daɗi a bakinta, amma hakanan ta daure takeci, badon komaiba sai don Husnah tacancanci tayi mata komai a rayuwarta, itace mace ta farko data fara bata kyakkyawan kulawa wanda tunda abunnan yafaru da ita babu wanda yabata, sai likita..
Duk da cewa bata wani ci mai yawa ba, amma zaiyi mata amfani, domin kuwa cikinta yajima ba'asa mai komai ba a cikinsa,,
Husnah nagama bata abincin, ta ɗauko musu Al'Qur'ani guda biyu, miƙawa Zahrah ɗaya taƴi, haɗe da buɗe mata fejin farko, cemata tayi su karanta a tare, duk da cewa da ƙyar muryarta yake fita amma sosai tayi ƙoƙari wajen karanta Al'Qur'ani,n.
Babu abun da yagagari Allah, Al'Qur'ani littafine mai cike da tarin haske, yana wanke zuciyar maikarantasa, yanasanya nutsuwa ga ma'abocin karantashi, take ƙuncin dake maƙare acikin zuciyar Zahrah yasoma ragewa, sunacikin karatun wani irin bacci ya yi gaba da'ita,, take ta kwanta a wajen tahau bacci,,
Murmushi