Showing 51001 words to 54000 words out of 123632 words
tadau kudin da Mami tabata dayawa tasaka a jaka da wayarta ta dauka tafito, mai gadi tacema tana son ya kira mata keke napep aiko sai gashi yakira mata, shatan shi tayi har kasuwa tabashi kudi dayawa tace yajirata zai maidata gida, aiko yadinga murna
Yace xai jirata anan, shiga tai cikin kasuwan saika shagunonin saida yadi, na farkon ta shiga, farin yadi ta yanka har yadi shidda ta biya kudi mai dinkin wajen tabamawa tasa yay mata doguwar riga mai shegen fadi da dogon hannu shima mai fadi akai abu abaaya kaman fiffike, murmushi tai ganin yanda rigar tayi tabiya kudi tafito tanata kalle kalle wurin, shagon wasu arna masu kitson attach tagani ta tsaya tanata kallon dogon gashin wig din data gani ajikin kan roba dasuke daurawa, kaman mai tunani kafin ta nisa ta shiga shagon ta tambaya nawane aka cemata dubu goma hakanan ta biya tafito tasai wani farin hodan yara na pears tabiya tafito sanan tabi hanyar data shigo kasuwar tafita mai keken ko nanan ta shiga suka koma gida kara bashi kudi tayi yanata mata godiya itakuma ta shiga gida rai fess, akarkashin gadon dakinta ta tura duka abubuwan gabanta nafaduwa tai sallan azahar harda rokon Allah yasa ya tsoratan sosai, sanan ta sauko kasa ta dafa white rice da stew ta dibi iya cinta takoma sama taci ta kwanta sai bacci, haka dai tawuni tana tunane tunane da neman nasara wurin Allah, wuraren goma tana shirin kwanciya taji shigowar shi gidan hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya tai fixing alarm awayarta karfe biyun dare kafin ta gyara kwanciya tai addu'an bacci sai bacci.
Karfe biyun dare alarm yafara ringing da kyar ta mike tsaye ta bude ido tana dafe kai, bayi ta shiga ta kukkuro baki tafito, agaban gadon ta tsugunna ta jawo kayan daga karkashin gado, doguwar farin rigan ta warware ta daura akan yar figigiyar rigar baccin dake jikinta, rigan ko har kasa yake jan mata, hannun ma yafi hanunta tsawo gashi da fadi saitai kaman wata fatalwa fatalwa aciki, hular dogon gashin tasaka da kyar dan bata iyaba, da sauri ta kalli kanta amadubi yanda tai kaman wata aljana mayya yasa ta ware ido, hodar ta dauka ta zazzaga sosai a hanunta ta lapta a fuskarta sosai saitai kaman aljanna da gasken, tasa hannu ta barbaza gashin ta gaban fuskarta sanan takara kallon yanda tai ita karan kanta bama kanta tsoro take ga kirjinta wani irin dukan biyar biyar yake, ahankali ta bude kofar dakin ta fita tai gaban dakinshi tadade a tsaye tana addu'a kafin ta tattaro jarumtarta takira sunayen Allah, sanan tabude kofar dakin ahankali ta shiga babu hanske sosai dakin sai dan dim light daya bari tana iya hango shi yanda yake baccin shi hankali kwance akan lumtsatsan gadonshi, ya lullube tundaga kafarshi har zuwa cikin shi yana baccin shi daya karama fuskarshi kyau, karasawa gaban gadon tayi ta tsaya zuciyar ta kaman zai fashe wani irin ajiyar zuciya ta sauke tana dafe kirjinta kafin ahankali ta mikar da hannunta tareda girgiza kanta tayanda gashin wig din ya yabazu sosai, dan gyara murya tayi kafin tai wani irin murya tace "Ay yaaaa nuuuuu, Ay yaaaaaa nuuuuuuu, Ayyyyyy Yaaaaaaa, Nuuuuuuuuu" dan motsi yay kaman yasan ana kiranshi, wlh takusa fitsari ajiki da kyar ta daddage ta kirashi da karfi bala'i "Ayyy Yaaaa Nuuuu" firgigit ya bude ido ya daurasu akanta, takusa sumewa amma bata bari yagane ba saima kara mikar da hannunta da rigar yaboye tayi tai wata irin murya tace "Ayy yaaa nuuuuu nu" wani irin ihu Ayaan yayi yamatsa baya da sauri dan sai yanzu idanunshi suka sake clearing, kara matsowa tayi tana wani jujuya kai dan yahango farin fuskarta da kyau tai wani iri da hannu kaman zata kamoshi ihu yay "Popsy" yakira atsorace wani irin murya tai tace "am yourrrr spirittt, kai saaakoo aaakkaaa baan in kaawooomaaa" wlh gabaki dayan jikinshi rawa yake bilhakki ya tsorata yana komawa baya me wanan waye wanan a tsakiyar daren nan, tana biyoshi tana wani irin jujjuya kai kaman zombie tace "ance-idan-har-aka-koma ga Allah-ba-zaka gamu da fishin ma'aiki, kadena wasa da salla, sallan ma ajam'i zaka dinga yi, ka gyara rayuwar ka, kaaa naaatsuuu kaaabi Allah yakai wanan bawan kanaji na kona maidakai biri" gyada kai yayi da sauri kaman zaiyi kuka yakasa kallonta saima shishigewa dayakeyi a bangon gado, itama yanda takejin wani irin tsoranshi na shiganta idan har takara koda minti dayane zai iya kamata hakan yasa tace "kulle idanun ka zan kooomaaa duniiiyarrr mu" da sauri ya kankame ido ganin haka yasa ta juya sadaf sadaf ta bude kofar ahankali tafita ta shiga dakin ta da gudu, ta cire rigar ta goge hodar fuskarta dashi sanan ta cire gashin tahadesu ta dukunkune ta tura karkashin gado tahau gado da gudu tareda jan bargo tana numfashi sama sama kirjinta ko kaman zai rushe sabida tsoro.
[7/21, 9:27 AM] +234 706 571 7620: ♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦
Maman Abd Shakur
49 - 50
Yay kusan minti biyar idanunshi arufe jikinshi ko ina na rawa bai taba ganin abu hakaba in his life kafin ya bude idon ahankali yana bin dakin da kallo, ganin kaman tanamai gizo a ido yasa ya fasa ihu. "Popsy" ya sauka daga gado da gudu yafita daga dakin yay downstairs, tana cikin bargo taji ihunshi tafashe dawani irin dariya tana taushe bakinta dudda yanda kirjinta ke bugawa amma bakaramin dariya tayiba. Haka ya zauna a falon ya kalli nan ya kalli chan sai kiran sunayen Allah daya dade bai kiraba yake dan wlh ya tsorata har ranshi, haka ya zauna a wurin yana istigifari har aka kira sallan asalatu mikewa yayi da sauri ya shiga bayin falon ya dauro alwala tsabagen yanda yake tsoron dakinshi yasa yakasa komawa, car key daya bari anan center table yadauka yafita tsakar gida yabude mota yanada wasu kaya awurin yadauko jallabiya yadawo daki yasaka sanan yafita shine harda tashi mai gadi su tafi masallacin tare, akan kunenta yabude kofa yafita aiko bakaramin dadi abin yamata ba harda sujjada tana godema Allah, ta shiga bayi ta dauro alwala tazo ta tada salla, saida gari yay haske sosai wuraren 9 sanan ya shigo gidan daga masallaci sama yatafi ahankali saida ya bude dakinshi ya dade abakin kofa yana kallon dakin kafin ya shiga ya kwaso kayan dazaisa yaje asibiti dasu sanan ya sauko kasa ya ijiye kan kujera, abayin falo yay wanka ya shirya yafita agurguje dan yay latti kuma yanada aikin dazaiyi.
Wuraren biyar na yamma yadawo gidan dauke da leda ahannu, bataji dawowan shiba tana zaune afalo cikin riga da sket na atampa tai nisa cikin karatun novel awayanta taji ana kokarin bude kofa, tashi tai a tsorace zata gudu dan gani take kaman yana ganin idonta zai gane itane aiko garin gudu ta bige da kujera, ihu tai ta rike kafarta daidai lokacin ya shigo dakin da sauri ya karasa gabanta yana kallon fuskarta dan ya dade bai ganta ba, ahankali ya tsugunna yana duba karfar ganin babu wani ciwo dataji yasa yace "mesa kike gudu" anatse kaman ba shiba, girgiza mai kai tayi tana hawaye gabanta na faduwa gani take kaman idan suka hada ido zai gane itace ta tsorata shi jiya, sakinta yayi ganin yanda jikinta ke rawa kafin ya ijiye ledar daya shigo dashi akan center table ya nuna mata da hannu yace "dauka kitafi dashi" ledan ta kalla kafin ta kalli fuskarshi saiyanzu ma talura yau babu sarkan babu dan kunen akunenshi ya kwanta tareda lumshe ido kaman mai tunani, da sauri tadau ledan tai sama da gudu bude ido yay kadan yabita da kallo kafin ya sauke ajiyar zuciya ahankali.
Tana shiga daki ta rufo kofanta ta zauna akasa ta bude ledan, ice cream ne manya manyan roba gudu uku different flavors, murmushi tayi ta gyara zama ta dauko daya daga cikinsu coconut flavor tahau sha tana lumlumshe ido, kasa shanye wa tayi ta ijiye agefe tana murmushi, ana kiran magrib taji yabude kofa yafita hakan yasa ta sauko ta saka ice cream din a freezer sanan takoma sama tai alwala tai salla ana kiran isha ma tai alwala tai salla tai karatu kafin ta tashi ta shiga bayi tai wankan dare tazo tasaka rigar baccin ta iya gwuiwa ta kwanta abinta tareda saka alarm yau biyu da rabi.
Alarm na tashin ta ta jawo kayan ta saka ta malka uban hoda a fuskarta dayama fi najiya tana dariyan keta dudda yanda kirjinta ke bugawa, fitowa tai Sadaf Sadaf kaman wata mayya ta bude kofar dakinshi bata ganshi ba hakan yasa ta fito tunawa da dazu a falo taga ya kwanta, tana hawa stairs ta ganshi ko akan doguwar kujera yana bacci awahale daga ganinshi kasan bai dade dayin bacci ba, sakkowa tai sadaf sadaf tana tattare rigar dan karya zubar da ita hartazo gabanshi ta tsaya tana kallonshi kafin takira sunashi. "Ayyyy yaaa nuuu" afirgice ya farka dan dama bacci baidade da saceshiba dan kasa bacci yayi tun bayan yadawo daga sallan Isha'i, a tsorace ya mike zaune ya makale jikin kujera yana kallon aljannar mai dogon gashi, ga gashin ta yakusa kai ciki, kara matso wa tai tana mimmikar da hannu kaman zata kamoshi, ihu yayi yana kokarin mikewa daga jikin kujera yace "wlh na riga na tuban ma Allah" wlh takusa dariya amma ta daure kirjinta na dukan uku uku tace "kaaayiii salla yauuuu?" gyada kai yayi yama kasa magana da sauri tace "in har ka kara aikata wani aiki na zunubi bazamu barka ba, rufe idonka lokacin bacewata nakoma duniyar mu tayi" ta dakamai tsawa dawani irin murya, da sauri yarufe ido jikinshi na rawa aiko ta juya da gudun bala'i tai sama batare data bari kafarta yay karaba, ahankali ta bude kofar dakinta ta shiga ta mayar ta rufe ahankali sabida karyay kara, ta cire rigan da sauri tana goge hoda fuskarta da ita kafin ta tunbuke gashin ta dukunkune su tare ta turasu karkashin gado tahau gado da gudu ta ja bargo tarufe tana dariya kasa kasa tana dafe kirji sabida yanda yake beating fast.
Yafi minti goma kankame da idanu ya rirrike lumtsa lumtsan filon kujera kafin ya bude idon ahankali yana kalle kallen falon ganin babu aljanar ta bace yasa ya mike tsaye da sauri yay sama, dakinta ya bude ya shiga arude, abirkice ta yaye bargo tana zazzaro ido da hawaye har yacika su dan tazaci yagano itane ke tsorata shi, shigowa yayi yana kallon dakin ko ina a gyare sai kamshin turaren wuta yake maida kofar yayi yarufe yazo yahayo gadon ya kwanta batare daya cemata kala ba sai ajiyan zuciya yake saukewa, a tsorace ta zabura ganinshi kusada ita zata sauka daga gadon ya riko hanunta yajawota yasata ajikinshi batare dayace mata kalaba ya kankameta yana ijiyan zuciya, tana iyajin yanda kirjinshi ke bugawa fatfat, kankametan dayayi yasama ko kwawkwaran motsi takasa sai hawayen wahala data farayi ahaka bacci yay gaba da ita, kasa bacci yay saima kara kankametan dayayi yanamai jin natsuwa ya sumbaci goshin ta yay istigifari akan kura kurenshi da laifuffukan dayama Allah swt.
Ahaka wahalallen bacci yay gaba da shi ana kiran assalatu ya bude ido tatas ya sauke su akan fuskarta duk ta takure ajikinshi tana bacci yafi minti goma yana kallon fuskar ta kafin ahankali ya ijiyeta agefe kaman yana ijiye Kwai, bayinta ya sauka ya shiga, ko ina kwalkwal ga kamshin dayake bayan yagama abinda zaiyi yafito daure da alwala, da bismilla yafita daga dakin yana Kalle Kalle gani yake kaman witch din zata fito, yay maza yafita daga gidan ya tada mai gadi atare suka tafi masallacin.
Wuraren 9 ya shigo gidan dauke da kayan dazaisa daya dauko daga mota har bayason kallon doguwar kujeran da witch din tazomai yanakai jiya, yay sama da sauri ya bude dakinta ya shiga bata ciki hakan yasa ya ijiye kayan akan gado ya shiga bayi yayo wanka yafito daure da pink towel dinta yafara shiri yana cikin kulle boturin hannu riga ta bude kofa tana ganinshi ta juya da sauri batare datama shigo dakinba zata tafi ahankali kaman ba Ayaan din daba yace "dauko min takalmina adakina" hannu tasa ta taushe bakinta jin dariya yazo mata aranta batare data juyo sun hada ido aranta tace "ashe akwai abinda zai iya chanza ka mugu" dakinshi ta shiga tana kalle kalle dan bataga takalmi ba.
Yana gama sa bituran hannun rigar yadau wallet dinshi dake kan bedside drawer yasaka a aljihun bayan wando, sanan ya mika hannu yadau wayarshi kiran iPhone xmas, mistakenly wayar yafadi anan kasa gefen gado, dan gajeren tsaki yaja kafin ahankali ya tsugunna dan daukar wayar dayaga yanakan wani farin yadi dayaga yadan leko daga karkashin gado, tsugunnawa yayi yadau wayar ya mike tsaye yasa kafa zai tura farin yadin dabemasan nameba dayadan leko yakoma ciki sai kuma yasake tsugunnawa hakanan yaji zuciyar shi na fizgar shi daya duba kome, ahankali yasa hannu yajawo farin yadin gabaki daya, yanayin yanda yajawo da karfi yasa abubuwan suka barbaje babban roban hoda yay tsalle yay gefe saikuma gashin dokin arna yay gefe daya saikuma ga yadin dayake aduddunkule, da mamaki yake kallon kayan dama yarinyar nan nasa attachment ne, saikuma ya mika hannu yadau farin yadin ya mike tsaye ya warware rigan yana tabe baki, rigan yabi dawani irin kallo daidai lokacin ta bude kofar ta shigo hanunta rike da black cover shoe dinshi, rigar bashi tsoro dataga ya warware yana wani irin kallo yasa ta zaro ido ta kallai, tsabagen yanda jikinta ke rawa batamasan sanda ta yar da takalman ba wani irin kallo yamata yasa arude tafara komawa dayaba tana tafiya. "dan girman Allah ka yakuri, wlh so nake kawai ka gyaru ka dinga salla saisa namaka hak..." da gudu ta kwasa tai downstairs ganin yanda yayo kanta, shi dayaga rigan yadaiga yay kama dana aljanna but ko kadan baikawo wani tunani aranshi ba maganan datayi yasa yagane kenan itace ta tsorata shi, take yaji rashin yana wani irin soyuwa, ganin binta yake yas ta kwasa da gudu tafita daga gidan mai gadi namata magana kota kanshi bata bi tafita babu hijabi ajikinta daga ita sai doguwar riga da dan kwalin ta, tana ko fita taci sa'a daidai wani keke napep yay dropping wata mata wup ta shige duk ta rude tana kallon waje ganin harya fito daga gate shima fuskarshi babu alamun rahama yasa tace "malam kama Allah mutafi kafin yazo ya kasheni, GRA zamu" da sauri mai keken ya kunna kafin Ayaan ya iso harsun waske, da sauri yakoma cikin gida ya shiga mota yabi bayansu dan baisan inda zataba, sune har GRA batadai san sunan layinsu ba amma tasan gidan, hakan yasa tana ganin gidan tanuna mai yana parking ko tsayawa mai magana batayi ba ta shiga gidan da gudun bala'i daidai nan Ayaan shima yay wani irin wawan parking awaje ya biyota a haukace, Mami, big Mummy, da Abba ne afalon, Abba da Big Mummy na zaune Mami kuma na tsaye daga ta wurin dining tanama wata yar aiki magana, tana shiga dakin bama ta lura dasu Abba ba ganin Mami yasa ta fasa wani irin ihu tai wurinta ta shiga bayanta ta kankame ta sosai tana nuna bakin kofa tace "Mami karki bari yadakeni wlh kasheni zaiyi yau" kafin Mami tama gama gane kan zancen ta shima ya shigo dakin ya dumfaro su idanunshi dasuka kankance tsabagen bacin rai akanta, yanda ta rirrike Mami tana neman ma fadir da itama tsabragen tsoro, "Ayaan!" Abba yakira shi da kakkausar murya, hakan yasa ya tsaya chak batare daya karasa wajen ba, Abba yataso yace "lafiyan ku kalau kuwa meya hadak...?" ko karashe maganan Abba baiyiba cikin kuka tafara tonama kanta asiri cikin kuka tace "Abba dama, uhm dama bayason yin salla ne shine nai shiga kaman dodo da daddare nabashi tsoro nace ance nazo na tunatar dashi yabi Allah ne...." nan tabasu duka labarin abinda yafaru habawa zokaga dariya gun Abba da Mami banda Big Mummy data daure fuska tana hararan Bilkisu data labe abayan Mami tana kuka. Juyawa yay zaifita daga falon azuciye Abba yakamo hannunshi yana cigaba da dariya abinshi, ya kalli Bilkisu dahar lokacin kuka take amma kadan kadan yace "Allah yamiki albarka yar arziki irin albarka mace tagari, ke Allah ya zundumaki a aljanna, Allah nagode maka dakabama Boy mata kaman Bilkisu" Mami kam harda mata kiss a goshi tana share mata hawayen datake tace "kin kyauta ina alfahari dake daughter na stop crying" Big Mummy cikeda fada tace "haba dai adinga adalci mana, sa'an tane da zatazo zo tana tsorata shi da daddare, yaro dan gata baisaba da irin rayuwar taba, baisan me wahala da sauran suba shine zata tsorata shi, gaskiya sam wanan abu bai daceba bata kyautaba kuma yahukun tata wlh" tunda Mami take bata taba kula Big Mum idan tafara kananun maganganun taba amma yau takasa hakura tace "dan tana neman shi da shiriya tana son yakoma ga Allah shine bata kyautaba? Shi yaro ne salla saiya gadama zaiyi aduk lokacin daya nishadan tu dayayi, haba mana hajiya" afadan ce Big Mummy tace "to ita waye dazata mai haka? Ai Allah gafurun raheemu ne, nannan mukaga karuwa data shiga aljanna sabida kare, Ayaan kobaya salla yanada dabi'u da dama masu kyau, yaro dai kin haifa amma kinkasa sonshi kullum kyaran shi kike, yanzu kuma namasan hala kece nan kikasa yarinyar nan ta tsorata shi, mai bakin hali kawai wacce ta tsani dan.." "saratu!" Abba yakira ta da kakkausar murya yana nunata da yatsa.
[7/21, 9:18 PM] 0mmer Farouk: ♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦
Maman Abd Shakur
51 - 52
Cikin fushi Abba yace "idan bazaki fadi alheri ba kiyimana shiru anan kona sassaba miki mara mutunci kawai da rashin sanin yakamata" ya karashe maganan yana kallon Ayaan dayama daskare awurin sai kallon fuskar ta yake, yakasa daina mamakin yanda yar yarinyar nan tai fooling dinshi haka on top of dat kuma tafito ahaka ba hijabi ba mayafi, juyo dashi Abba yay yana murmushi tareda shafa kuncin shi cikeda jin dadi yace "ashe saisa jiya darana dakazo office naganka a sahun farko a masallaci" dariya Abba yay sosai yace "masha Allah, am so proud of yata, and"